ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Ta Kafa Kyakkyawan Misali A Fannin Kare Hakkokin Bil Adama

by CGTN Hausa
3 years ago
sin

Ga duk mai bibiyar al’amuran yau da kullum dake gudana a matakin kasa da kasa, ya kwana da sanin cewa, kasar Sin ta sake samun gurbi a hukumar kare hakkin bil adama ta MDD, sakamakon zabenta da aka sake yi, yayin taron koli na MDD da ya gudana a ’yan kwanakin baya, kuma bisa hakan, za ta kasance cikin mambobin hukumar tun daga shekarar 2024 dake tafe har zuwa 2026.

Wannan ne karo na shida, da Sin din ke samun damar ba da gudummawa a wannan hukuma ta MDD, tun bayan kafuwarta a shekarar 2006. To ko mene ne ya sanya har yanzu ake damawa da kasar Sin a wannan hukuma mai muhimmanci?

  • Sin Ta Kadu Ta Yi Tir Da Kisan Jama’a Masu Tarin Yawa Sakamakon Hari Kan Asibiti A Gaza 
  • Yadda Kasar Sin Ke Ba Da Gudummawar Zamanintar Da Kasashen Duniya Cikin Shekaru 10 Masu Zuwa

Hakika dalilan suna da yawa, amma kadan daga cikinsu su ne gamsuwar da sassan kasa da kasa suka yi, da irin nasarorin da Sin din ta cimma a bangarorin kare hakkokin bil adama a cikin gida, da ma yadda take taka rawar gani wajen shiga hadin gwiwar kare hakkin bil adama a matakin kasa da kasa.

ADVERTISEMENT

Sanin kowa ne cewa, a matsayinta na daya daga cikin kasashe mambobin farko na MDD, kuma mai kujerar dindindin a majalissar, har kullum kasar Sin na shiga dukkanin ayyukan da suka shafi kare hakkin bil adama, tana sauke nauyin tallafawa ayyukan da suka shafi hakan, kana tana goya baya ga tsarin jagoranci na kare hakkokin bil adama yadda ya kamata.

Har ila yau, duniya ta gamsu da yadda Sin din ke ingiza duk wasu matakai na samun ci gaban manufofin kare hakkin bil adama cikin lumana kuma a dukkanin matakai.

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Kaza lika, Sin na martaba ka’idojin MDD, da sauran kudurorin da sassan kasa da kasa suka amince da su game da kare hakkin bil adama, wanda hakan ya sanya ta zama abun koyi ga sauran sassan duniya a wannan fage.

A ganin kasar Sin, kare martabar al’umma shi ne babban jigo na tabbatar da hakkokin bil adama, wato dai farin cikin al’umma shi ne kan gaba, idan ana batun kare hakkin bil Adama.

Ko shakka babu, al’ummar kasar Sin na kara cin gajiya daga nasarorin kasarsu, kuma Sin na sanya bukatun jama’a gaban komai, tana goyon bayan duk wasu tsare-tsare na samar da ci gaban al’umma daga dukkanin fannoni, ta yadda duniya ke yabawa, da irin gudummawarta a bangaren kare hakkokin bil Adama. (Saminu Alhassan)

sin
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

MASU ALAKA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
Daga Birnin Sin

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
Daga Birnin Sin

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
Daga Birnin Sin

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Next Post
Kaduna

Na Sha Alwashin Magance Talauci Da Kashi 80 Cikin 100 A Jihata - Gwamnan Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.