• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Kano ya buɗe Cibiyar Hadda da Nazarin Alƙur’ani A Gidan Kwankwaso

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Kwankwaso
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamna Abba Yusuf ya buɗe Cibiyar Hadda da Nazarin Alƙur’ani, wadda aka raɗa wa suna Majidaɗi Institute for Qur’anic Research and Advancement (MIQRA).

An sadaukar da cibiyar ne ga mahaifin Kwankwaso, Musa Sale Kwankwaso. Kuma an gina cibiyar a gidan Kwankwaso da ke kan titin Miller Road, Kano.

  • Nasihar Kwankwaso Ga Angwaye Da Amaren Kano: Ku Guji Binciken Wayoyin Junanku
  • Shirin Bunƙasa Ilmi A Kano: Yadda Gwamnatin Abba Gida-gida Ta Tura Dalibai 1001 Karatu Kasashen Waje

Sanarwar da Kakakin Yaɗa Labarai na Gwamnan Kano, Sanusi Bature ya fitar, ya ce, “Gwamna Abba ya yaba wa Sanata Rabi’u Kwankwaso dangane da wannan gagarimin tanadi da ya yi wa al’umma wajen bunƙasa ilmin addinin Musulunci.”

Gwamnan ya ce, an kafa cibiyar a daidai lokacin da ya dace, idan aka yi la’akari da yawan makarantun allo da na Islamiyya da ke faɗin jihar, waɗanda ke buƙatar a narkar da su cikin tsarin makarantun zamani, domin daƙile yadda almajirai ke ta gararamba kan tituna.

Gwamnan ya ƙara da cewa, Sanata Kwankwaso ya samu gagarimar nasarar ayyukan inganta rayuwar al’umma a lokacin mulkinsa, musamman wajen bunƙasa addinin Musulunci.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

Ya bada misali da aikin katange dukkan maƙabartun cikin birnin Kano, gyaran masallatan Juma’a a faɗin jihar, gina makarantun Islamiyya a ƙananan hukumomi 44.

Sai dai kuma Abba ya nuna damuwa dangane da yadda Gwamnatin da ta shuɗe a Kano, ta ƙi ƙarasa sauran makarantun da Kwankwaso bai kammala ginawa kafin cikar wa’adin mulkin sa ba.

Saboda haka, Gwamna Abba ya yi alƙawarin ƙarasa makarantun, kuma ya bada umarni ga Ma’aikatar Ilmi ta fara tsare-tsaren fara ɗaukar ɗalibai domin fara zangon karatu.

Sanata Kwankwaso ya ce an kafa MIQRA domin ta riƙa horas da mahaddata Alƙur’ani maza da mata domin samun satifiket ɗin firamare da sakandare, ta yadda za su samu hanyar zarcewa makarantun gaba da sakandare da jami’o’i.

Ɗalibai daban-daban sun jinjina wa Kwankwaso da Gwamnan Kano dangane da wannan shiri mai albarka da aka gina.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gwamna Abba
ShareTweetSendShare
Previous Post

Rike Iyayen Gida Masu Amana Na Daga Sirrin Samun Nasara A Kannyywood – Muhammadu Murtala

Next Post

Mutum 5 Sun Mutu Sakamakon Konewar Tankar Mai A Kwara

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

2 hours ago
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna
Labarai

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

3 hours ago
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu
Manyan Labarai

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

4 hours ago
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya
Labarai

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

5 hours ago
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF
Manyan Labarai

Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

7 hours ago
Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike
Manyan Labarai

Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

9 hours ago
Next Post
Mutum 5 Sun Mutu Sakamakon Konewar Tankar Mai A Kwara

Mutum 5 Sun Mutu Sakamakon Konewar Tankar Mai A Kwara

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

August 25, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

August 25, 2025
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

August 25, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

August 25, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

August 25, 2025
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

August 25, 2025
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.