ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nasihar Kwankwaso Ga Angwaye Da Amaren Kano: Ku Guji Binciken Wayoyin Junanku

by Sulaiman
3 years ago
Kwankwaso

A wata nasiha kuma gargaɗi da jan-kunne, tsohon Gwamnan Jihar Kano, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya shawarci ma’aurata 1,500 da aka ɗaura wa auren zawarawa a Kano cewa, kada su maida hankali wajen binciken wayoyin junansu.

Kwankwaso wanda shi ne madugun Kwankwasiyya kuma ɗan takarar shugaban ƙasa na NNPP a zaɓen 2023, ya ce yawan binciken wayoyi da ma’aurata ke yi ne sahun gaba wajen yawan rabuwar aure.

  • Zaben Kano: Ba Mu Yarda A Karya ‘Yancin Dimokuradiyya Ba – Kungiya
  • ‘Yansanda Sun Cafke Mutum 3 Bisa Zargin Fashi Da Makami A Jihar Kano

Kwankwaso ya yi wannan nasihar ce a ranar Juma’a, wurin walimar da Gwamnatin Jihar Kano ta shirya wa Angwayen da Amaren a dandalin taro na Gidan Gwamnatin Kano, a ranar Asabar.

ADVERTISEMENT

Tun da farko, a ranar Juma’a, Gwamna Abba Yusuf ne ya tsaya a matsayin waliyyin auren zawarawan, wanda aka gudanar lokaci ɗaya a faɗin ƙananan hukumomi 44 da ke Jihar Kano.

An shirya ɗaura aure 1,800 a lokaci ɗaya, amma kuma an samu ma’aurata 300 da lamarin bai yiwu ba, saboda dalilai na rashin lafiya.

LABARAI MASU NASABA

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

“Na tabbata ana ta ba ku shawarwari daban-daban da nasihohi da gargaɗi kusan kila sau dubu. Malamai, iyaye da danginku da ma ‘yan kasuwa duk sun sha ba ku shawarwarin yadda za ku yi zaman aure a cikin kwanciyar hankali.

“To amma dai ni ina da wata shawara ɗaya, wato kada ku riƙa leƙe-leƙen binciken wayoyin junanku, domin yin hakan ya kawo sanadiyyar mutuwar aure da yawa,” inji Kwankwaso.

Daga nan ya yaba da irin namijin ƙoƙarin da Gwamnan Kano Abba Yusuf ya yi wajen shirya wannan gagarimin bikin auren dandazon zawarawa a Kano.

Haka kuma ya yaba wa Gwamnatin Kano dangane da kashe Naira miliyan 700 wajen ɗaukar nauyin ɗalibai 600 zuwa karatu jami’o’i daban-daban a ƙasashen waje.

A na sa jawabin, Gwamna Abba ya ce Gwamnatin Jihar Kano ce ta ɗauki nauyin shirya auren, ita ta biya sadakin kowane ango da kuma kayan ɗakin amarya, har da kayan gara na kayan abinci da kuma tallafin Naira 20,000 ga kowace amarya domin ta samu jarin fara sana’ar rage raɗaɗin tsadar rayuwa a gidajen auren su.

Daga nan ya hore su su yi zaman lafiya da juna a bisa tafarkin Musulunci.

Gwamna Abba ya ce, an zaɓo ma’auratan ne 30 daga kowace ƙaramar hukuma ɗaya, daga cikin ƙananan hukumomi 44 da jihar ke da su.

A jawabin sa, Shugaban Hukumar Hisbah, Aminu Daurawa, ya ce an ɗaura aure 1,500 a ranar Juma’a.

Ya ce waɗanda ba a samu damar ɗaura auren na su ba saboda lalurar rashin lafiya, su 264 ne, kuma za a ɗaura auren na su da zarar sun kammala shan magani nan gaba kaɗan.

Daurawa ya yi masu nasiha da su sa tsoron Allah a zamantakewar aure a tsakanin su.

Kwankwaso
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan
  • Sulaiman
    ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
  • Sulaiman
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

MASU ALAKA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila
Manyan Labarai

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Next Post
Magoya Bayan Kasar Ingila Sun Yi Wa Henderson Ihu A Wasansu Da Australia

Magoya Bayan Kasar Ingila Sun Yi Wa Henderson Ihu A Wasansu Da Australia

LABARAI MASU NASABA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.