ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nasihar Kwankwaso Ga Angwaye Da Amaren Kano: Ku Guji Binciken Wayoyin Junanku

by Sulaiman
3 years ago
Kwankwaso

A wata nasiha kuma gargaɗi da jan-kunne, tsohon Gwamnan Jihar Kano, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya shawarci ma’aurata 1,500 da aka ɗaura wa auren zawarawa a Kano cewa, kada su maida hankali wajen binciken wayoyin junansu.

Kwankwaso wanda shi ne madugun Kwankwasiyya kuma ɗan takarar shugaban ƙasa na NNPP a zaɓen 2023, ya ce yawan binciken wayoyi da ma’aurata ke yi ne sahun gaba wajen yawan rabuwar aure.

  • Zaben Kano: Ba Mu Yarda A Karya ‘Yancin Dimokuradiyya Ba – Kungiya
  • ‘Yansanda Sun Cafke Mutum 3 Bisa Zargin Fashi Da Makami A Jihar Kano

Kwankwaso ya yi wannan nasihar ce a ranar Juma’a, wurin walimar da Gwamnatin Jihar Kano ta shirya wa Angwayen da Amaren a dandalin taro na Gidan Gwamnatin Kano, a ranar Asabar.

ADVERTISEMENT

Tun da farko, a ranar Juma’a, Gwamna Abba Yusuf ne ya tsaya a matsayin waliyyin auren zawarawan, wanda aka gudanar lokaci ɗaya a faɗin ƙananan hukumomi 44 da ke Jihar Kano.

An shirya ɗaura aure 1,800 a lokaci ɗaya, amma kuma an samu ma’aurata 300 da lamarin bai yiwu ba, saboda dalilai na rashin lafiya.

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

“Na tabbata ana ta ba ku shawarwari daban-daban da nasihohi da gargaɗi kusan kila sau dubu. Malamai, iyaye da danginku da ma ‘yan kasuwa duk sun sha ba ku shawarwarin yadda za ku yi zaman aure a cikin kwanciyar hankali.

“To amma dai ni ina da wata shawara ɗaya, wato kada ku riƙa leƙe-leƙen binciken wayoyin junanku, domin yin hakan ya kawo sanadiyyar mutuwar aure da yawa,” inji Kwankwaso.

Daga nan ya yaba da irin namijin ƙoƙarin da Gwamnan Kano Abba Yusuf ya yi wajen shirya wannan gagarimin bikin auren dandazon zawarawa a Kano.

Haka kuma ya yaba wa Gwamnatin Kano dangane da kashe Naira miliyan 700 wajen ɗaukar nauyin ɗalibai 600 zuwa karatu jami’o’i daban-daban a ƙasashen waje.

A na sa jawabin, Gwamna Abba ya ce Gwamnatin Jihar Kano ce ta ɗauki nauyin shirya auren, ita ta biya sadakin kowane ango da kuma kayan ɗakin amarya, har da kayan gara na kayan abinci da kuma tallafin Naira 20,000 ga kowace amarya domin ta samu jarin fara sana’ar rage raɗaɗin tsadar rayuwa a gidajen auren su.

Daga nan ya hore su su yi zaman lafiya da juna a bisa tafarkin Musulunci.

Gwamna Abba ya ce, an zaɓo ma’auratan ne 30 daga kowace ƙaramar hukuma ɗaya, daga cikin ƙananan hukumomi 44 da jihar ke da su.

A jawabin sa, Shugaban Hukumar Hisbah, Aminu Daurawa, ya ce an ɗaura aure 1,500 a ranar Juma’a.

Ya ce waɗanda ba a samu damar ɗaura auren na su ba saboda lalurar rashin lafiya, su 264 ne, kuma za a ɗaura auren na su da zarar sun kammala shan magani nan gaba kaɗan.

Daurawa ya yi masu nasiha da su sa tsoron Allah a zamantakewar aure a tsakanin su.

Kwankwaso
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
  • Sulaiman
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Sulaiman
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

MASU ALAKA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna
Labarai

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Next Post
Magoya Bayan Kasar Ingila Sun Yi Wa Henderson Ihu A Wasansu Da Australia

Magoya Bayan Kasar Ingila Sun Yi Wa Henderson Ihu A Wasansu Da Australia

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.