• English
  • Business News
Tuesday, September 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Muna Alfahari Da Dangote  – Tinubu

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Muna Alfahari Da Dangote  – Tinubu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu, ya bayyana cewa gwamnatin Nijeriya na alfahari da Dangote kan yadda yake inganta tattalin arzikin kasar nan.

A jiya ne kamfanin Dangote ya samu gagarumar lambar yabo daga shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, wanda ya bayyana matsayin gwamnati kan ci gaban da kamfanin ya samu a Nijeriya da ma nahiyar Afirka baki daya.

  • Jikar Dantata Ta Rasu Tana Da Shekaru 40 A Duniya
  • Nijeriya Ta Yi Nasara A Kotun Ingila Kan Rikicinta Da Kamfanin P&ID

Amincewa da shugabancin ya zo ne bayan karramawa da lambobin yabo da kamfanin ya samu don samar da dubban ayyukan yi da kuma mai tasiri ga tattalin arzikin Nijeriya.

Shugaba Tinubu wanda ya halarci taron tattalin arzikin Nijeriya karo na 29 da ke gudana a Abuja, ya ce: “Kuna da tasiri. Ku ci gaba da yin kyawawan abubuwan da kuke yi. Ku ci gaba da saka hannun jari a Nijeriya.”

Dangote shi ne babban mai daukar ma’aikata bayan gwamnati, kuma daya daga cikin manyan masu hannu da shuni a nahiyar.

Labarai Masu Nasaba

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara

A jawabin da ya gabatar tun farko lokacin da yake bude taron shekara-shekarar, shugaban ya yi kira ga kamfanoni masu zaman kansu da su shiga sahun masu dawo da ci gaban tattalin arzikin Nijeriya, inda ya kara da cewa kasar za ta iya bunkasa ne ta hanyar hadin gwiwa.

Masana da suka yi jawabi a wajen taron sun bayyana cewa Nijeriya na jiran matatar man fetur ta Dangote, inda suka bayyana kwarin gwiwar cewa hakan zai kawo wani gagarumin ci gaba ga tattalin arzikin kasar nan.

Da yake jawabi a wajen taron mai taken: ‘Bude Hanyar Yaki Da Cin Hanci da Rashawa’, Manajan Daraktan Rukunin Kamfanin Dangote Industries Limited, Mista Olakunle Alake, ya ce ya yi farin ciki da yadda gwamnatin Shugaba Tinubu ta fahimci rawar da kamfanoni ke takawa, tare da karfafa bukatar hadin gwiwa.

Mista Alake ya ce dole ne Nijeriya ta bunkasa tattalin arzikinta musamman bangaren masana’antu domin samun damar taka muhimmiyar rawa a yankin Afirka da bangaren ciniki (AFCFTA).

Ya ce duk da cewa AFCFTA ba ita ce mafita ga tattalin arzikin Nijeriya ba, amma ya yi watsi da cewa kasar nan za ta iya samun tagomashi daga gare ta ta hanyar tallafawa ci gaban masana’antu.

Mista Alake ya bukaci gwamnatocin kasashen Afirka ta Yamma da su gyara matsalolin da ke kawo cikas ga aiwatar da ka’idojin kungiyar ECOWAS, inda ya bayyana cewa har yanzu harkokin kasuwanci a kasashen yammacin Afirka na samun koma baya.

Ya bayar da shawarar inganta iyakokin, tashoshin jiragen ruwa a nahiyar domin samun bunkasar tattalin arziki.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ci GabaDangoteTaroTattalin ArzikiTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Aka Yi Walimar Saukar Alkur’ani Ta ‘Yar Abba El-Mustapha

Next Post

Gwamnan Zamfara Zai Binciki Badakalar Miliyan 774 A Hukumar Alhazai Ta Jihar

Related

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
Manyan Labarai

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

7 hours ago
Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara

13 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato

15 hours ago
Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja
Manyan Labarai

Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

17 hours ago
KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano
Manyan Labarai

KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

19 hours ago
Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba
Manyan Labarai

Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

1 day ago
Next Post
Dawowar Ta’addanci Ta Sake Jefa Sakkwatawa Da Zamfarawa Cikin Zullumi

Gwamnan Zamfara Zai Binciki Badakalar Miliyan 774 A Hukumar Alhazai Ta Jihar

LABARAI MASU NASABA

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

September 15, 2025
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

September 15, 2025
Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

September 15, 2025
Tinubu

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

September 15, 2025
Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

September 15, 2025
Sanata Natasha Za Ta Fuskanci Hukunci Daga Kwamitin Ɗa’a Na Majalisa

Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa

September 15, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

September 15, 2025
Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

September 15, 2025
Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Zurfafa Dunkulewar Kasuwannin Kasa Ta Bai Daya”

Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Zurfafa Dunkulewar Kasuwannin Kasa Ta Bai Daya”

September 15, 2025
Neja

Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar

September 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.