• English
  • Business News
Wednesday, October 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasuwanci Tsakanin Sin Da Zimbabwe Ya Bunkasa

by CGTN Hausa
2 years ago
Zimbabwe

Ofishin jakadancin Sin dake kasar Zimbabwe ya bayyana cewa, cinikayya tsakanin Sin da Zimbabwe a cikin watanni 9 na farkon bana, ya karu da kashi 39.4 cikin 100, zuwa dalar Amurka biliyan 2.43, idan aka kwatanta da makamancin lokaci a shekarar da ta gabata, wanda ya zarce jimillar cinikin da aka yi a shekarar 2022.

A cewar ofishin jakadancin, darajar kayayyakin da Zimbabwe ta fitar zuwa kasar Sin a cikin wannan lokaci, ta kai dalar Amurka biliyan 1.36, yayin da darajar kayayyakin da aka shigo da su cikin kasar daga kasar Sin, ta kai dalar Amurka biliyan 1.07. Yana mai cewa, kayayyakin da kasar Sin ta ci gaba da shigo da su cikin kasar, sun taimakawa Zimbabwe wajen samun rarar cinikayyar da ta kai dalar Amurka miliyan 29.

  • Xi Jinping Ya Gana Da Gwamnan Jihar California Dake Amurka
  • Me Ya Sa Dangantaka Da Sin Ke Samun Karbuwa A Afrika?

A cewar hukumar kididdiga ta kasar Zimbabwe, a cikin watan Agusta, kasar Sin ta kasance kasa ta uku wajen fitar da kayayyaki zuwa kasar Zimbabwe, inda makwabciyarta Afrika ta Kudu ta kasance a kan gaba, sai hadaddiyar daular Larabawa a matsayin babbar kasuwa ta biyu a fannin fitar da kayayyaki zuwa kasashen waje. Dangane da shigo da kayayyaki kuwa, a watan Agusta, kasar Sin ta kasance babbar kasuwa ta biyu ga Zimbabwe, bayan Afirka ta Kudu.

Sannan a yau Laraba 25 ga watan Oktoba, ranar yaki da kakaba takunkumi ce da kungiyar raya kudancin Afirka ko kuma SADC a takaice ta ayyana. Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin, Mao Ning ta bayyana cewa, kasarta ta sake kira ga wasu kasashe da kungiyoyi ’yan kalilan, da su saurari muryoyin kasashe daban-daban, da gaggauta soke takunkuman da suka kakabawa kasar Zimbabwe ba bisa doka ba, da daukar matakai a zahirance, don taimaka mata habaka tattalin arziki da kyautata rayuwar al’umma, gami da taka rawar gani a fannin shimfida zaman lafiya da samar da ci gaba a duniya baki daya.

Mao ta jaddada cewa, Sin za ta ci gaba da goyawa Zimbabwe baya wajen nuna adawa ga shisshigin da wasu kasashe suka yi mata, don ta kama tafarkin samar da ci gaba bisa ’yancin kanta. (Ibrahim Yaya, Murtala Zhang)

LABARAI MASU NASABA

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 
Daga Birnin Sin

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

October 21, 2025
Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa
Daga Birnin Sin

Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa

October 21, 2025
Ci Gaban Kasar Sin Ya Shaida Cewa Yawan Jama’a Ba Dalili Ne Na Rashin Ci Gaba Ba
Daga Birnin Sin

Ci Gaban Kasar Sin Ya Shaida Cewa Yawan Jama’a Ba Dalili Ne Na Rashin Ci Gaba Ba

October 21, 2025
Next Post
UNESCO Ta Yi Bikin Ranar Amfani Da Kafofin Watsa Labarai Da Yada Bayanai Ta Duniya A Abuja

UNESCO Ta Yi Bikin Ranar Amfani Da Kafofin Watsa Labarai Da Yada Bayanai Ta Duniya A Abuja

LABARAI MASU NASABA

Gobara Ta Tashi A Kasuwar Alaba Da Ke Legas

Gobara Ta Tashi A Kasuwar Alaba Da Ke Legas

October 22, 2025
Gwamnoni Sun Yi Ta’aziyyar Mutanen Da Suka Rasu A Fashewar Tankar Mai A Neja

Gwamnoni Sun Yi Ta’aziyyar Mutanen Da Suka Rasu A Fashewar Tankar Mai A Neja

October 22, 2025
Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

October 21, 2025
Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa

Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa

October 21, 2025
Aikin Jinya Kyauta: Gwamnatin Zamfara Ta Kammala Zagaye Na 10 Na Kula Da Marasa Lafiya 3,447

Aikin Jinya Kyauta: Gwamnatin Zamfara Ta Kammala Zagaye Na 10 Na Kula Da Marasa Lafiya 3,447

October 21, 2025
Ci Gaban Kasar Sin Ya Shaida Cewa Yawan Jama’a Ba Dalili Ne Na Rashin Ci Gaba Ba

Ci Gaban Kasar Sin Ya Shaida Cewa Yawan Jama’a Ba Dalili Ne Na Rashin Ci Gaba Ba

October 21, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Gwamna Yusuf Ya Buƙaci Hukumar NBC Da Ta Sa Ido Kan Gidajen Rediyo Da Talabijin Na Yanar Gizo

October 21, 2025
Me Aka Gano Kan Makomar Tattalin Arzikin Kasar Sin Daga Karuwar 5.2% Na Tattalin Arzikinta?

Me Aka Gano Kan Makomar Tattalin Arzikin Kasar Sin Daga Karuwar 5.2% Na Tattalin Arzikinta?

October 21, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisa Ta Tabbatar Da Yusuf A Matsayin Sabon Shugaban NPC, Wasu 2 A Matsayin Kwamishinoni

October 21, 2025
Jirgin Kasa Mafi Saurin Gudu A Duniya Ya Fara Zirga-Zirgar Gwaji A Sin

Jirgin Kasa Mafi Saurin Gudu A Duniya Ya Fara Zirga-Zirgar Gwaji A Sin

October 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.