ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Jinping Ya Gana Da Gwamnan Jihar California Dake Amurka

by CGTN Hausa
3 years ago
Xi Jinping

Da yammacin yau Laraba 25 ga wata ne, shuguban kasar Sin Xi Jinping, ya gana da gwamnan jihar California ta kasar Amurka, Gavin Newsom, a babban dakin taron al’umma dake birnin Beijing.

Xi ya ce, cimma nasarori wajen raya dangantakar Sin da Amurka tun lokacin da har zuwa yanzu, ba abu mai sauki ba ne, wanda ya cancanci a daraja. Manufofin gwamnatin kasar Sin kan Amurka, har kullum su ne, mutunta juna, da zaman jituwa, da yin hadin-gwiwa bisa cimma moriyar juna. Kasar Sin za ta ci gaba da yin kokari a wannan fanni, kana, tana fatan Amurka za ta bada hadin-kai.

  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Fashin Daji Da Dama, Sun Kwato Makamai A Sokoto
  • Gasar Wasannin Asiya Ajin Masu Bukata Ta Musaman Ta Hangzhou Ta Bayyana Kulawar Da Sin Take Baiwa Wannan Rukuni Na Al’umma

A nasa bangaren, Gavin Newsom ya ce, babu wata dangantakar kasa da kasa a duniya da ta fi dangantakar Amurka da Sin muhimmanci, dangantakar da ta shafi makomar Amurka gami da alfanun al’ummar kasar. Ya yarda da manufofin da shugaba Xi ya bayyana wajen raya dangantakar kasashen biyu, da shaida aniyar kara tuntubar juna tsakanin jiharsa wato California da kasar Sin, da fadada hadin-gwiwarsu a fannonin da suka shafi sauyin yanayi da sabbin makamashi. California din tana son zama kakkarfar abokiyar hadin-gwiwar kasar Sin na dogon lokaci. Bugu da kari, a yau ne, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya mika wasikar taya murnar bikin ba da lambar yabo na kwamitin kula da dangantakar da ke tsakanin kasashen Amurka da Sin na kasar Amurka.

ADVERTISEMENT

Shugaba Xi Jinping ya yabawa kwamitin bisa kokarin sa kaimi ga inganta mu’amala da hadin gwiwa a tsakanin Amurka da Sin a fannoni daban daban, kana ya taya Henry Alfred Kissinger, murnar samun lambar yabon.

Shugaba Xi ya yi nuni da cewa, a matsayin manyan kasashe biyu a duniya, yadda Sin da Amurka suke mu’amala da juna ta hanya mai dacewa ko a’a, yana da nasaba da makomar zaman lafiya da bunkasuwa da kuma dan Adam a duniya. Ya ce Sin tana son bin ka’idojin girmama juna, da yin zaman tare cikin lumana, da yin hadin gwiwa don samun moriyar juna, da kara hadin gwiwa tare da kasar Amurka, da daidaita sabanin da ke tsakaninsu, da tinkarar kalubalen duniya tare, don samun moriyar juna, da wadata tare, da kuma amfanawa jama’ar kasashen biyu har ma da duk duniya baki daya.

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Shugaba Xi yana fatan kwamitin da kuma abokai daga bangarori daban daban za su ci gaba da nuna goyon baya ga raya dangantakar dake tsakanin Sin da Amurka don taka muhimmiyar rawa wajen sa kaimi ga raya dangantakar kasashen biyu yadda ya kamata.
Kana a wannan rana, shugaban kasar Amurka Joseph Biden shi ma ya mika wasikar taya murnar bikin. (Murtala Zhang, Zainab)

Xi Jinping
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

MASU ALAKA

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje
Daga Birnin Sin

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Next Post
Pedri Ba Zai Buga El-Clasico Ba Saboda Rauni

Pedri Ba Zai Buga El-Clasico Ba Saboda Rauni

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.