ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Jinping Ya Gana Da Gwamnan Jihar California Dake Amurka

by CGTN Hausa
3 years ago
Xi Jinping

Da yammacin yau Laraba 25 ga wata ne, shuguban kasar Sin Xi Jinping, ya gana da gwamnan jihar California ta kasar Amurka, Gavin Newsom, a babban dakin taron al’umma dake birnin Beijing.

Xi ya ce, cimma nasarori wajen raya dangantakar Sin da Amurka tun lokacin da har zuwa yanzu, ba abu mai sauki ba ne, wanda ya cancanci a daraja. Manufofin gwamnatin kasar Sin kan Amurka, har kullum su ne, mutunta juna, da zaman jituwa, da yin hadin-gwiwa bisa cimma moriyar juna. Kasar Sin za ta ci gaba da yin kokari a wannan fanni, kana, tana fatan Amurka za ta bada hadin-kai.

  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Fashin Daji Da Dama, Sun Kwato Makamai A Sokoto
  • Gasar Wasannin Asiya Ajin Masu Bukata Ta Musaman Ta Hangzhou Ta Bayyana Kulawar Da Sin Take Baiwa Wannan Rukuni Na Al’umma

A nasa bangaren, Gavin Newsom ya ce, babu wata dangantakar kasa da kasa a duniya da ta fi dangantakar Amurka da Sin muhimmanci, dangantakar da ta shafi makomar Amurka gami da alfanun al’ummar kasar. Ya yarda da manufofin da shugaba Xi ya bayyana wajen raya dangantakar kasashen biyu, da shaida aniyar kara tuntubar juna tsakanin jiharsa wato California da kasar Sin, da fadada hadin-gwiwarsu a fannonin da suka shafi sauyin yanayi da sabbin makamashi. California din tana son zama kakkarfar abokiyar hadin-gwiwar kasar Sin na dogon lokaci. Bugu da kari, a yau ne, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya mika wasikar taya murnar bikin ba da lambar yabo na kwamitin kula da dangantakar da ke tsakanin kasashen Amurka da Sin na kasar Amurka.

ADVERTISEMENT

Shugaba Xi Jinping ya yabawa kwamitin bisa kokarin sa kaimi ga inganta mu’amala da hadin gwiwa a tsakanin Amurka da Sin a fannoni daban daban, kana ya taya Henry Alfred Kissinger, murnar samun lambar yabon.

Shugaba Xi ya yi nuni da cewa, a matsayin manyan kasashe biyu a duniya, yadda Sin da Amurka suke mu’amala da juna ta hanya mai dacewa ko a’a, yana da nasaba da makomar zaman lafiya da bunkasuwa da kuma dan Adam a duniya. Ya ce Sin tana son bin ka’idojin girmama juna, da yin zaman tare cikin lumana, da yin hadin gwiwa don samun moriyar juna, da kara hadin gwiwa tare da kasar Amurka, da daidaita sabanin da ke tsakaninsu, da tinkarar kalubalen duniya tare, don samun moriyar juna, da wadata tare, da kuma amfanawa jama’ar kasashen biyu har ma da duk duniya baki daya.

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Shugaba Xi yana fatan kwamitin da kuma abokai daga bangarori daban daban za su ci gaba da nuna goyon baya ga raya dangantakar dake tsakanin Sin da Amurka don taka muhimmiyar rawa wajen sa kaimi ga raya dangantakar kasashen biyu yadda ya kamata.
Kana a wannan rana, shugaban kasar Amurka Joseph Biden shi ma ya mika wasikar taya murnar bikin. (Murtala Zhang, Zainab)

Xi Jinping
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

MASU ALAKA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
Daga Birnin Sin

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Next Post
Pedri Ba Zai Buga El-Clasico Ba Saboda Rauni

Pedri Ba Zai Buga El-Clasico Ba Saboda Rauni

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.