• English
  • Business News
Monday, July 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Jinping Ya Gana Da Gwamnan Jihar California Dake Amurka

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Xi Jinping Ya Gana Da Gwamnan Jihar California Dake Amurka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Da yammacin yau Laraba 25 ga wata ne, shuguban kasar Sin Xi Jinping, ya gana da gwamnan jihar California ta kasar Amurka, Gavin Newsom, a babban dakin taron al’umma dake birnin Beijing.

Xi ya ce, cimma nasarori wajen raya dangantakar Sin da Amurka tun lokacin da har zuwa yanzu, ba abu mai sauki ba ne, wanda ya cancanci a daraja. Manufofin gwamnatin kasar Sin kan Amurka, har kullum su ne, mutunta juna, da zaman jituwa, da yin hadin-gwiwa bisa cimma moriyar juna. Kasar Sin za ta ci gaba da yin kokari a wannan fanni, kana, tana fatan Amurka za ta bada hadin-kai.

  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Fashin Daji Da Dama, Sun Kwato Makamai A Sokoto
  • Gasar Wasannin Asiya Ajin Masu Bukata Ta Musaman Ta Hangzhou Ta Bayyana Kulawar Da Sin Take Baiwa Wannan Rukuni Na Al’umma

A nasa bangaren, Gavin Newsom ya ce, babu wata dangantakar kasa da kasa a duniya da ta fi dangantakar Amurka da Sin muhimmanci, dangantakar da ta shafi makomar Amurka gami da alfanun al’ummar kasar. Ya yarda da manufofin da shugaba Xi ya bayyana wajen raya dangantakar kasashen biyu, da shaida aniyar kara tuntubar juna tsakanin jiharsa wato California da kasar Sin, da fadada hadin-gwiwarsu a fannonin da suka shafi sauyin yanayi da sabbin makamashi. California din tana son zama kakkarfar abokiyar hadin-gwiwar kasar Sin na dogon lokaci. Bugu da kari, a yau ne, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya mika wasikar taya murnar bikin ba da lambar yabo na kwamitin kula da dangantakar da ke tsakanin kasashen Amurka da Sin na kasar Amurka.

Shugaba Xi Jinping ya yabawa kwamitin bisa kokarin sa kaimi ga inganta mu’amala da hadin gwiwa a tsakanin Amurka da Sin a fannoni daban daban, kana ya taya Henry Alfred Kissinger, murnar samun lambar yabon.

Shugaba Xi ya yi nuni da cewa, a matsayin manyan kasashe biyu a duniya, yadda Sin da Amurka suke mu’amala da juna ta hanya mai dacewa ko a’a, yana da nasaba da makomar zaman lafiya da bunkasuwa da kuma dan Adam a duniya. Ya ce Sin tana son bin ka’idojin girmama juna, da yin zaman tare cikin lumana, da yin hadin gwiwa don samun moriyar juna, da kara hadin gwiwa tare da kasar Amurka, da daidaita sabanin da ke tsakaninsu, da tinkarar kalubalen duniya tare, don samun moriyar juna, da wadata tare, da kuma amfanawa jama’ar kasashen biyu har ma da duk duniya baki daya.

Labarai Masu Nasaba

Sin Da Amurka Na Kokarin Tabbatar Da Ci Gaban Da Aka Samu Na Yarjejeniyar London

Sin Na Maraba Da ’Yan Jaridar Duniya Da Su Halarci Bikin Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Harin Japan Da Na Tafarkin Murdiya 

Shugaba Xi yana fatan kwamitin da kuma abokai daga bangarori daban daban za su ci gaba da nuna goyon baya ga raya dangantakar dake tsakanin Sin da Amurka don taka muhimmiyar rawa wajen sa kaimi ga raya dangantakar kasashen biyu yadda ya kamata.
Kana a wannan rana, shugaban kasar Amurka Joseph Biden shi ma ya mika wasikar taya murnar bikin. (Murtala Zhang, Zainab)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaIsra'ilaSin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Karbar Haraji Mai Yawa Ne Ya Durkusar Da Masana’antu A Nijeriya – Kwamiti

Next Post

Pedri Ba Zai Buga El-Clasico Ba Saboda Rauni

Related

Sin Da Amurka Na Kokarin Tabbatar Da Ci Gaban Da Aka Samu Na Yarjejeniyar London
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Na Kokarin Tabbatar Da Ci Gaban Da Aka Samu Na Yarjejeniyar London

22 minutes ago
Sin Na Maraba Da ’Yan Jaridar Duniya Da Su Halarci Bikin Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Harin Japan Da Na Tafarkin Murdiya 
Daga Birnin Sin

Sin Na Maraba Da ’Yan Jaridar Duniya Da Su Halarci Bikin Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Harin Japan Da Na Tafarkin Murdiya 

1 hour ago
Cinikayyar Shige Da Fice Ta Sin Ta Karu Da Kaso 2.9 Bisa Dari A Watanni Shida Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Cinikayyar Shige Da Fice Ta Sin Ta Karu Da Kaso 2.9 Bisa Dari A Watanni Shida Na Farkon Bana

2 hours ago
Kasar Sin Ta Nuna Alhinin Rasuwar Tsohon Shugaban Nijeriya Buhari
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Nuna Alhinin Rasuwar Tsohon Shugaban Nijeriya Buhari

3 hours ago
Za A Yi Taron Shugabannin Matasa Na Farko Na Dandalin Zaman Lafiya Da Tsaro Na Sin Da Afirka A Nanjing
Daga Birnin Sin

Za A Yi Taron Shugabannin Matasa Na Farko Na Dandalin Zaman Lafiya Da Tsaro Na Sin Da Afirka A Nanjing

4 hours ago
Afirka Ta Kudu Na Fatan Karfafa Alakar Cinikayya Tare Da Sin Ta Hanyar Halartar Baje Kolin CISCE
Daga Birnin Sin

Afirka Ta Kudu Na Fatan Karfafa Alakar Cinikayya Tare Da Sin Ta Hanyar Halartar Baje Kolin CISCE

1 day ago
Next Post
Pedri Ba Zai Buga El-Clasico Ba Saboda Rauni

Pedri Ba Zai Buga El-Clasico Ba Saboda Rauni

LABARAI MASU NASABA

Dangote Na Neman Izinin Gina Babbar Tashar Jiragen Ruwa Mafi Zurfi A Nijeriya

Dangote Na Neman Izinin Gina Babbar Tashar Jiragen Ruwa Mafi Zurfi A Nijeriya

July 14, 2025
Sin Da Amurka Na Kokarin Tabbatar Da Ci Gaban Da Aka Samu Na Yarjejeniyar London

Sin Da Amurka Na Kokarin Tabbatar Da Ci Gaban Da Aka Samu Na Yarjejeniyar London

July 14, 2025
Sarkin Maroko Ya Aike Da Ta’aziyya Ga Nijeriya Bisa Rasuwar Buhari

Sarkin Maroko Ya Aike Da Ta’aziyya Ga Nijeriya Bisa Rasuwar Buhari

July 14, 2025
Sin Na Maraba Da ’Yan Jaridar Duniya Da Su Halarci Bikin Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Harin Japan Da Na Tafarkin Murdiya 

Sin Na Maraba Da ’Yan Jaridar Duniya Da Su Halarci Bikin Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Harin Japan Da Na Tafarkin Murdiya 

July 14, 2025
Osimhen Na Dab Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

Osimhen Na Dab Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

July 14, 2025
Gwamnan Zamfara Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

Gwamnan Zamfara Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

July 14, 2025
Za A Iya Yarda Da Buhari Kan Kowace Irin Amana A Duniya — Abdulsalami

Za A Iya Yarda Da Buhari Kan Kowace Irin Amana A Duniya — Abdulsalami

July 14, 2025
Cinikayyar Shige Da Fice Ta Sin Ta Karu Da Kaso 2.9 Bisa Dari A Watanni Shida Na Farkon Bana

Cinikayyar Shige Da Fice Ta Sin Ta Karu Da Kaso 2.9 Bisa Dari A Watanni Shida Na Farkon Bana

July 14, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 1,111, Sun Yi Garkuwa Da 276 A Nijeriya Cikin Watan Yuni

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 1,111, Sun Yi Garkuwa Da 276 A Nijeriya Cikin Watan Yuni

July 14, 2025
Kasar Sin Ta Nuna Alhinin Rasuwar Tsohon Shugaban Nijeriya Buhari

Kasar Sin Ta Nuna Alhinin Rasuwar Tsohon Shugaban Nijeriya Buhari

July 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.