• English
  • Business News
Monday, July 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babu Wani Shiri Na Kwaso ‘Yan Nijeriya Daga Falasdin Ko Isra’ila –Gwamnatin Tarayya

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Babu Wani Shiri Na Kwaso ‘Yan Nijeriya Daga Falasdin Ko Isra’ila –Gwamnatin Tarayya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin tarayya ta bayyana cewa babu wani shirin kwaso ‘yan Nijeriya daga kasar Israila ko kuma Falasdin, domin babu wanda ya bukaci hakan.

Ma’aikatar kula da ‘yan Nijeriya da ke kasashen ketare (NiDCOM), ita ce ta bayyana hakan, inda ta ce ba ta samu wani kiran waya ba daga wani mutum ko kungiya na ‘yan Nijeriya da ke cikin barazana ba game da yakin da ya barke tsakanin Isra’ila da Falasdinawa.

  • Gobe Za A Tsame Duk Ma’aikacin Tarayya Da Ba Ya Cikin Tsarin IPPIS Daga Biyan Albashi
  • Xi Jinping Ya Gana Da Gwamnan Jihar California Dake Amurka

NIDCOM ta kara da cewa za ta kwaso ‘yan Nijeriya ne kawai idan ta samu kiran waya daga ‘yan Nijeriyan da ke kasashen guda biyu, amma har yanzu ba ta samu hakan ba.

Mai magana da yawun ma’aikatan, Abdur-Rahman Balogun shi ya bayyana hakan lokacin da yake zantawa da kamfanin dallancin labarai na Nijeriya (NAN) a Abuja.

Balogun yana mayar da martani ne ga wata tambaya kan ko me gwamnatin tarayya ke yi na kwashe ‘yan Nijeriya mazauna yankunan da ake gwabzawa fada a gabas ta tsakiya.

Labarai Masu Nasaba

Ranar Talata Mai Zuwa Zan Koma Zauren Majalisar Dattawa – Sanata Natasha

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

Dubban ‘yan kasashen waje ne suka makale a Isra’ila da kuma kasar Falasdin, inda ake gwabza kazamin yaki tun bayan da kungiyar Hamas ta kaddamar da hari.

Rikicin ya yi sanadin mutuwar dubban mutane daga bangarorin biyu, kasashe da dama sun kaddamar da ayyukan kwashe ‘yan kasarsu zuwa gida, yayin da wasu ke shirin yin hakan.

Ya zuwa yanzu dai kasashe irinsu Amurka da Jamus da Ukraine da Thailand da Koriya ta Kudu da Austiriya da Brazil da kuma Argentina na daga cikin kasashen da suka mayar da ‘yan kasarsu gida.

Mai magana da yawun NiDCOM ya ce ‘yan wasu kasashe sun yi kiran gaggawa ga gwamnatocinsu na gida don neman taimako, “amma ba mu samu ko kira daya daga ‘yan kasarmu da ke yankunan guda biyu ba.”

Ya tunatar da cewa Ministan Harkokin Waje, Yusuf Tuggar, ya fitar da wata sanarwa, inda ya ce ’yan Nijeriya mazauna kasashen waje ba sa fuskantar matsin lamba saboda yakin da ake yi a zirin Gaza.

A cewarsa, ma’aikatar za ta iya yin aiki ne kawai idan ta sami kiran gaggawa daga mutanen da ke cikin kasashe masu fama da rikici.

Ya kara da cewa a lokacin da NiDCOM da sauran hukumomin da abin ya shafab a kasar suka samu kiran gaggawa daga ‘yan Nijeriya mazauna kasar Sin, a lokacin barkewar cutar Korona, da kuma na yakin Ukraine da Sudan lokacin da yakin ya barke a yankunan, “mun amsa kuma da yawa daga cikin ‘yan kasarmu mun mayar da su gida.”

Sojojin Isra’ila sun umurci sama da mutane miliyan daya da su fice daga arewacin Gaza cikin sa’o’i 24 gabanin wani samame da sojoji ke shirin kaiwa.

Kusan ‘yan Falasdin 5,100 ne aka kashe a Zirin Gaza tun bayan da Isra’ila ta kaddamar da hare-haren bama-bamai a yankin da ta mamaye bayan harin da Hamas ta kai a cikin Isra’ila fiye da makonni biyu da suka wuce.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Fatattakar Gaza: Ya Kamata Duniya Ta Yi Mana Adalci – Jakadan Falasdin A Nijeriya

Next Post

GORON JUMA’A

Related

Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha
Manyan Labarai

Ranar Talata Mai Zuwa Zan Koma Zauren Majalisar Dattawa – Sanata Natasha

19 hours ago
Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC
Manyan Labarai

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

2 days ago
Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP
Manyan Labarai

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

2 days ago
Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC
Manyan Labarai

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

2 days ago
‘Yansanda Sun Kama Barayi 15, Sun Kwato Motocin Sata 20 A Kano
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja

3 days ago
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha
Manyan Labarai

Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha

3 days ago
Next Post
GORON JUMA’A

GORON JUMA'A

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Arewa Za Su Yi Murna Idan Na Zama Shugaban Ƙasa — Peter Obi

Ƴan Arewa Za Su Yi Murna Idan Na Zama Shugaban Ƙasa — Peter Obi

July 7, 2025
AI Zai Maye Gurbin Ayyuka Miliyan 92 A Duniya – Farfesa Pate

AI Zai Maye Gurbin Ayyuka Miliyan 92 A Duniya – Farfesa Pate

July 7, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Tunisiya Da Ci 3-0 A Moroko

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Tunisiya Da Ci 3-0 A Moroko

July 6, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato

‘Yan Boko Haram Sun Kashe Mutane 9, Tare Da Jikkata Wasu Mutum 4 A Borno

July 6, 2025
Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya

Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya

July 6, 2025
Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

July 6, 2025
Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin

Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin

July 6, 2025
Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

July 6, 2025
Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama

Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama

July 6, 2025
Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC

Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC

July 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.