• English
  • Business News
Monday, August 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsaro Shi Ne Kashin Bayan Ci Gaban Kowacce Kasa

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Tsaro Shi Ne Kashin Bayan Ci Gaban Kowacce Kasa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An kaddamar da babban taron tattauna batutuwan tsaro na kasa da kasa na Xiangshan karo na 10, jiya Litinin a birnin Beijing. Tabbas batun tsaro muhimmin batu ne da ya shafi kowacce kasa da yanki da kuma duniya, domin shi ne kashin bayan samun ci gaban da ake muradi. 

Sauye-sauyen da bil adama ke gani a wannan zamani, kama daga ayyukan ta’addanci da juyin mulki da yake-yake da fito-na-fito, abubuwa ne da aka dade ba a gani ba, wanda kuma bai kamata a ce ana fama da su a wannan zamani na wayewar kai ba.

  • Kasar Sin Ta Gudanar Da Taron Koli Kan Harkokin Kudi
  • Shugaba Xi Jinping Ya Amsa Wasikar Mashahurin Masanin Kimiyya Da Fasaha Na Kasar Cuba

Lamuran dake faruwa a baya-bayan nan sun nuna cewa, babu wanda zai iya tsira daga irin wadannan matsaloli, don haka, ya dace kasashe su tashi tsaye domin daukar dabarun dakatar da faruwarsu, ta hanyar tattaunawa da musayar ra’ayi da hadin gwiwa da koyi da dabarun juna.

A baya-bayan nan, kudurin neman tsagaita bude wuta a rikicin Falasdinu da Isra’ila ya samu kuri’un amincewa mai yawa a MDD, lamarin da ya nuna cewa kasashen duniya suna da ra’ayi na bai daya kan samun zaman lafiya a duniya. Sai dai, abin takaici shi ne, duk da haka, akwai wadansu tsiraru dake cin gajiyar rikice-rikicen, inda suke yin biris da matsalolin da suka addabe su a cikin gida, suke kara rura wutar rikici tsakanin kasa da kasa

Kamar yadda mataimakin shugaban rundunar sojin kasar Sin janar Zhang Youxia ya bayyana a jawabin bude taron Xinagshan, dole ne kasashen duniya su farga game da karuwar rikice-rikice, da fito-na-fito. A ganina, dabarar yin hakan ita ce, hadin gwiwa da girmama juna da tattaunawa, a don haka nake ganin wannan taro ya zo a daidai lokacin da ake bukatarsa.

Labarai Masu Nasaba

An Fara Bayar Da Hidimomin Da Suka Shafi Sauka Da Tashi Domin Gasar Wasanni Ta Duniya Ta Chengdu

Ana Gaggauta Ayyukan Gyara Tituna Da Gadojin Da Ambaliya Ta Lalata A Arewacin Kasar Sin

Kasar Sin mai masaukin baki, ta bayyana cewa, a shirye take ta ci gaba da zurfafa hadin gwiwa kan tsaro da karfafa tsarin tsaro na duniya. Kowa zai iya shaidar kasar Sin wajen nuna dattako da kai zuciya nesa. Wannan ya tuna min da furucin da mataimakin shugaban Nijeriya Kashim Shettima ya yi a kwanakin baya yayin zantawarsa da sashen Hausa na rediyon kasar Sin cewa, Sin ba ta taba kai hari ba, kuma tana kaunar zaman lafiya da ci gaban al’umma.

Yayin da muke kara shaidawa da fahimtar yanayin da duniya ke cika, dole ne kasashenmu su yi koyi da Sin, su kasance masu kaunar zaman lafiya da hadin gwiwa da tuntuba da girmama juna, domin samun zaman lafiya da ci gaban da al’ummar duniya ke muradi. (Fa’iza Mustapha)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Harkokin cikin gidaIranIsra'ila
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Ethiopia Da Ci 4 A Abuja

Next Post

Kotu Ta Yanke Wa ‘Yan Daudu 8 Hukuncin Daurin Watanni 3 A Kano

Related

An Fara Bayar Da Hidimomin Da Suka Shafi Sauka Da Tashi Domin Gasar Wasanni Ta Duniya Ta Chengdu
Daga Birnin Sin

An Fara Bayar Da Hidimomin Da Suka Shafi Sauka Da Tashi Domin Gasar Wasanni Ta Duniya Ta Chengdu

21 hours ago
Ana Gaggauta Ayyukan Gyara Tituna Da Gadojin Da Ambaliya Ta Lalata A Arewacin Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Ana Gaggauta Ayyukan Gyara Tituna Da Gadojin Da Ambaliya Ta Lalata A Arewacin Kasar Sin

22 hours ago
Shugabar Tanzania Ta Kaddamar Da Cibiyar Cinikayya Da Jigila Da Sin Ta Gina A Kasar
Daga Birnin Sin

Shugabar Tanzania Ta Kaddamar Da Cibiyar Cinikayya Da Jigila Da Sin Ta Gina A Kasar

23 hours ago
Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya
Daga Birnin Sin

Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya

2 days ago
Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya
Daga Birnin Sin

Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

2 days ago
Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya
Daga Birnin Sin

Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya

2 days ago
Next Post
PDP A Kano: Kotu Ta Sanya Ranar Yanke Hukuncin Shari’ar Sadiq Wali Da Abacha

Kotu Ta Yanke Wa 'Yan Daudu 8 Hukuncin Daurin Watanni 3 A Kano

LABARAI MASU NASABA

Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

August 4, 2025
Gwamna Buni Ya Bukaci Sabon Sarkin Gudi Ya Jagoranci Zaman Lafiya, Hadin Kai, Da Ci Gaban Kasa

Gwamna Buni Ya Bukaci Sabon Sarkin Gudi Ya Jagoranci Zaman Lafiya, Hadin Kai, Da Ci Gaban Kasa

August 4, 2025
Gina Tituna A Karkara Yana Bunkasa Tattalin Arziki – Gwamna Sule

Gina Tituna A Karkara Yana Bunkasa Tattalin Arziki – Gwamna Sule

August 4, 2025
Tsohon Dan Majalisar Taraba Usman Ya Fice Daga APC

Tsohon Dan Majalisar Taraba Usman Ya Fice Daga APC

August 4, 2025
Yadda Al’ummar Da Ke Zaune Da ‘Yan Bindiga Ke Rayuwa A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane Da Dama A Kauyukan Zamfara

August 4, 2025
Gwamnatin Kano Za Ta Mayar Da Gidan Gyaran Hali Na Kurmawa Gidan Tarihi

Gwamnatin Kano Za Ta Mayar Da Gidan Gyaran Hali Na Kurmawa Gidan Tarihi

August 4, 2025
Kashe N712bn Kan Gyaran Filin Jiragen Saman Legas Rashin Sanin Ya Kamata Ne – ADC 

Kashe N712bn Kan Gyaran Filin Jiragen Saman Legas Rashin Sanin Ya Kamata Ne – ADC 

August 4, 2025
Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina

Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina

August 3, 2025
Sanata Shehu Buba Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Da Rigakafin Shanu A Bauchi

Sanata Shehu Buba Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Da Rigakafin Shanu A Bauchi

August 3, 2025
Wasu Kungiyoyi Sun Yi Kira Ga Dan Majalisa Aminu Sani Jaji Ya Fito Takarar Gwamnan Zamfara 

Wasu Kungiyoyi Sun Yi Kira Ga Dan Majalisa Aminu Sani Jaji Ya Fito Takarar Gwamnan Zamfara 

August 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.