• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsaro Shi Ne Kashin Bayan Ci Gaban Kowacce Kasa

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Tsaro Shi Ne Kashin Bayan Ci Gaban Kowacce Kasa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An kaddamar da babban taron tattauna batutuwan tsaro na kasa da kasa na Xiangshan karo na 10, jiya Litinin a birnin Beijing. Tabbas batun tsaro muhimmin batu ne da ya shafi kowacce kasa da yanki da kuma duniya, domin shi ne kashin bayan samun ci gaban da ake muradi. 

Sauye-sauyen da bil adama ke gani a wannan zamani, kama daga ayyukan ta’addanci da juyin mulki da yake-yake da fito-na-fito, abubuwa ne da aka dade ba a gani ba, wanda kuma bai kamata a ce ana fama da su a wannan zamani na wayewar kai ba.

  • Kasar Sin Ta Gudanar Da Taron Koli Kan Harkokin Kudi
  • Shugaba Xi Jinping Ya Amsa Wasikar Mashahurin Masanin Kimiyya Da Fasaha Na Kasar Cuba

Lamuran dake faruwa a baya-bayan nan sun nuna cewa, babu wanda zai iya tsira daga irin wadannan matsaloli, don haka, ya dace kasashe su tashi tsaye domin daukar dabarun dakatar da faruwarsu, ta hanyar tattaunawa da musayar ra’ayi da hadin gwiwa da koyi da dabarun juna.

A baya-bayan nan, kudurin neman tsagaita bude wuta a rikicin Falasdinu da Isra’ila ya samu kuri’un amincewa mai yawa a MDD, lamarin da ya nuna cewa kasashen duniya suna da ra’ayi na bai daya kan samun zaman lafiya a duniya. Sai dai, abin takaici shi ne, duk da haka, akwai wadansu tsiraru dake cin gajiyar rikice-rikicen, inda suke yin biris da matsalolin da suka addabe su a cikin gida, suke kara rura wutar rikici tsakanin kasa da kasa

Kamar yadda mataimakin shugaban rundunar sojin kasar Sin janar Zhang Youxia ya bayyana a jawabin bude taron Xinagshan, dole ne kasashen duniya su farga game da karuwar rikice-rikice, da fito-na-fito. A ganina, dabarar yin hakan ita ce, hadin gwiwa da girmama juna da tattaunawa, a don haka nake ganin wannan taro ya zo a daidai lokacin da ake bukatarsa.

Labarai Masu Nasaba

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Kasar Sin mai masaukin baki, ta bayyana cewa, a shirye take ta ci gaba da zurfafa hadin gwiwa kan tsaro da karfafa tsarin tsaro na duniya. Kowa zai iya shaidar kasar Sin wajen nuna dattako da kai zuciya nesa. Wannan ya tuna min da furucin da mataimakin shugaban Nijeriya Kashim Shettima ya yi a kwanakin baya yayin zantawarsa da sashen Hausa na rediyon kasar Sin cewa, Sin ba ta taba kai hari ba, kuma tana kaunar zaman lafiya da ci gaban al’umma.

Yayin da muke kara shaidawa da fahimtar yanayin da duniya ke cika, dole ne kasashenmu su yi koyi da Sin, su kasance masu kaunar zaman lafiya da hadin gwiwa da tuntuba da girmama juna, domin samun zaman lafiya da ci gaban da al’ummar duniya ke muradi. (Fa’iza Mustapha)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Harkokin cikin gidaIranIsra'ila
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Ethiopia Da Ci 4 A Abuja

Next Post

Kotu Ta Yanke Wa ‘Yan Daudu 8 Hukuncin Daurin Watanni 3 A Kano

Related

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu
Daga Birnin Sin

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

5 hours ago
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili
Daga Birnin Sin

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

7 hours ago
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa
Daga Birnin Sin

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

7 hours ago
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya
Daga Birnin Sin

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

11 hours ago
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

13 hours ago
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

13 hours ago
Next Post
PDP A Kano: Kotu Ta Sanya Ranar Yanke Hukuncin Shari’ar Sadiq Wali Da Abacha

Kotu Ta Yanke Wa 'Yan Daudu 8 Hukuncin Daurin Watanni 3 A Kano

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.