• English
  • Business News
Monday, June 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsaro Shi Ne Kashin Bayan Ci Gaban Kowacce Kasa

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Tsaro Shi Ne Kashin Bayan Ci Gaban Kowacce Kasa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An kaddamar da babban taron tattauna batutuwan tsaro na kasa da kasa na Xiangshan karo na 10, jiya Litinin a birnin Beijing. Tabbas batun tsaro muhimmin batu ne da ya shafi kowacce kasa da yanki da kuma duniya, domin shi ne kashin bayan samun ci gaban da ake muradi. 

Sauye-sauyen da bil adama ke gani a wannan zamani, kama daga ayyukan ta’addanci da juyin mulki da yake-yake da fito-na-fito, abubuwa ne da aka dade ba a gani ba, wanda kuma bai kamata a ce ana fama da su a wannan zamani na wayewar kai ba.

  • Kasar Sin Ta Gudanar Da Taron Koli Kan Harkokin Kudi
  • Shugaba Xi Jinping Ya Amsa Wasikar Mashahurin Masanin Kimiyya Da Fasaha Na Kasar Cuba

Lamuran dake faruwa a baya-bayan nan sun nuna cewa, babu wanda zai iya tsira daga irin wadannan matsaloli, don haka, ya dace kasashe su tashi tsaye domin daukar dabarun dakatar da faruwarsu, ta hanyar tattaunawa da musayar ra’ayi da hadin gwiwa da koyi da dabarun juna.

A baya-bayan nan, kudurin neman tsagaita bude wuta a rikicin Falasdinu da Isra’ila ya samu kuri’un amincewa mai yawa a MDD, lamarin da ya nuna cewa kasashen duniya suna da ra’ayi na bai daya kan samun zaman lafiya a duniya. Sai dai, abin takaici shi ne, duk da haka, akwai wadansu tsiraru dake cin gajiyar rikice-rikicen, inda suke yin biris da matsalolin da suka addabe su a cikin gida, suke kara rura wutar rikici tsakanin kasa da kasa

Kamar yadda mataimakin shugaban rundunar sojin kasar Sin janar Zhang Youxia ya bayyana a jawabin bude taron Xinagshan, dole ne kasashen duniya su farga game da karuwar rikice-rikice, da fito-na-fito. A ganina, dabarar yin hakan ita ce, hadin gwiwa da girmama juna da tattaunawa, a don haka nake ganin wannan taro ya zo a daidai lokacin da ake bukatarsa.

Labarai Masu Nasaba

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

Kasar Sin mai masaukin baki, ta bayyana cewa, a shirye take ta ci gaba da zurfafa hadin gwiwa kan tsaro da karfafa tsarin tsaro na duniya. Kowa zai iya shaidar kasar Sin wajen nuna dattako da kai zuciya nesa. Wannan ya tuna min da furucin da mataimakin shugaban Nijeriya Kashim Shettima ya yi a kwanakin baya yayin zantawarsa da sashen Hausa na rediyon kasar Sin cewa, Sin ba ta taba kai hari ba, kuma tana kaunar zaman lafiya da ci gaban al’umma.

Yayin da muke kara shaidawa da fahimtar yanayin da duniya ke cika, dole ne kasashenmu su yi koyi da Sin, su kasance masu kaunar zaman lafiya da hadin gwiwa da tuntuba da girmama juna, domin samun zaman lafiya da ci gaban da al’ummar duniya ke muradi. (Fa’iza Mustapha)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Harkokin cikin gidaIranIsra'ila
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Ethiopia Da Ci 4 A Abuja

Next Post

Kotu Ta Yanke Wa ‘Yan Daudu 8 Hukuncin Daurin Watanni 3 A Kano

Related

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya
Daga Birnin Sin

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

52 minutes ago
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu
Daga Birnin Sin

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

2 hours ago
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

3 hours ago
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere
Daga Birnin Sin

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

4 hours ago
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku
Daga Birnin Sin

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

5 hours ago
Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa
Daga Birnin Sin

Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa

7 hours ago
Next Post
PDP A Kano: Kotu Ta Sanya Ranar Yanke Hukuncin Shari’ar Sadiq Wali Da Abacha

Kotu Ta Yanke Wa 'Yan Daudu 8 Hukuncin Daurin Watanni 3 A Kano

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

June 30, 2025
Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

June 30, 2025
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

June 30, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

June 30, 2025
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

June 30, 2025
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

June 30, 2025
CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

June 30, 2025
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

June 30, 2025
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.