ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsaro Shi Ne Kashin Bayan Ci Gaban Kowacce Kasa

by CGTN Hausa
3 years ago
Tsaro

An kaddamar da babban taron tattauna batutuwan tsaro na kasa da kasa na Xiangshan karo na 10, jiya Litinin a birnin Beijing. Tabbas batun tsaro muhimmin batu ne da ya shafi kowacce kasa da yanki da kuma duniya, domin shi ne kashin bayan samun ci gaban da ake muradi. 

Sauye-sauyen da bil adama ke gani a wannan zamani, kama daga ayyukan ta’addanci da juyin mulki da yake-yake da fito-na-fito, abubuwa ne da aka dade ba a gani ba, wanda kuma bai kamata a ce ana fama da su a wannan zamani na wayewar kai ba.

  • Kasar Sin Ta Gudanar Da Taron Koli Kan Harkokin Kudi
  • Shugaba Xi Jinping Ya Amsa Wasikar Mashahurin Masanin Kimiyya Da Fasaha Na Kasar Cuba

Lamuran dake faruwa a baya-bayan nan sun nuna cewa, babu wanda zai iya tsira daga irin wadannan matsaloli, don haka, ya dace kasashe su tashi tsaye domin daukar dabarun dakatar da faruwarsu, ta hanyar tattaunawa da musayar ra’ayi da hadin gwiwa da koyi da dabarun juna.

ADVERTISEMENT

A baya-bayan nan, kudurin neman tsagaita bude wuta a rikicin Falasdinu da Isra’ila ya samu kuri’un amincewa mai yawa a MDD, lamarin da ya nuna cewa kasashen duniya suna da ra’ayi na bai daya kan samun zaman lafiya a duniya. Sai dai, abin takaici shi ne, duk da haka, akwai wadansu tsiraru dake cin gajiyar rikice-rikicen, inda suke yin biris da matsalolin da suka addabe su a cikin gida, suke kara rura wutar rikici tsakanin kasa da kasa

Kamar yadda mataimakin shugaban rundunar sojin kasar Sin janar Zhang Youxia ya bayyana a jawabin bude taron Xinagshan, dole ne kasashen duniya su farga game da karuwar rikice-rikice, da fito-na-fito. A ganina, dabarar yin hakan ita ce, hadin gwiwa da girmama juna da tattaunawa, a don haka nake ganin wannan taro ya zo a daidai lokacin da ake bukatarsa.

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

Kasar Sin mai masaukin baki, ta bayyana cewa, a shirye take ta ci gaba da zurfafa hadin gwiwa kan tsaro da karfafa tsarin tsaro na duniya. Kowa zai iya shaidar kasar Sin wajen nuna dattako da kai zuciya nesa. Wannan ya tuna min da furucin da mataimakin shugaban Nijeriya Kashim Shettima ya yi a kwanakin baya yayin zantawarsa da sashen Hausa na rediyon kasar Sin cewa, Sin ba ta taba kai hari ba, kuma tana kaunar zaman lafiya da ci gaban al’umma.

Yayin da muke kara shaidawa da fahimtar yanayin da duniya ke cika, dole ne kasashenmu su yi koyi da Sin, su kasance masu kaunar zaman lafiya da hadin gwiwa da tuntuba da girmama juna, domin samun zaman lafiya da ci gaban da al’ummar duniya ke muradi. (Fa’iza Mustapha)

Tsaro
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Japan Ta Kwaye Lullubin Da Take Fakewa Da Shi Wajen Kiran Kanta Mai Kaunar Zaman Lafiya

MASU ALAKA

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar
Daga Birnin Sin

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”
Daga Birnin Sin

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

June 12, 2026
Next Post
PDP A Kano: Kotu Ta Sanya Ranar Yanke Hukuncin Shari’ar Sadiq Wali Da Abacha

Kotu Ta Yanke Wa 'Yan Daudu 8 Hukuncin Daurin Watanni 3 A Kano

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.