• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Ya Gana Da Firaministan Girka Da Yin Tattaunawa Da Shugaban Gwamnatin Jamus

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Xi Ya Gana Da Firaministan Girka Da Yin Tattaunawa Da Shugaban Gwamnatin Jamus
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya gana a yau Juma’a da firaministan Girka, Kyriakos Mitsotakis a birnin Beijing. Yayin ganawar, shugaba Xi ya ce, tun bayan kulla huldar diflomasiyya tsakanin kasashen biyu cikin sama da rabin karni, Sin da Girka sun yi ta raya dangantakar cikin aminci da juriya.

Ya ce, a shirye Sin take ta inganta hadin gwiwar dabarun ci gaba da Girka, da zurfafa hadin gwiwa a fannonin sufuri da jiragen ruwa da makamashi da sadarwa da hada-hadar kudi da fadada damarmakin hadin gwiwa a fannin bunkasa tattalin arziki ba tare da gurbata muhalli ba da kirkire-kirkiren kimiyya da fasaha da inganta hadin gwiwar shawarar “Ziri Daya da Hanya Daya” tare da samar da gaba mai karko da dorewa na tashar ruwa ta Piraeus

  • Xi Jinping Ya Taya Murnar Gudanar Da Babban Taron Birane Masu Sada Zumunta Na Sin Da Amurka
  • Xi Jinping Ya Jaddada Muhimmancin Samar Da Kyakkyawar Fahimtar Al’ummantaka Ga Jama’ar Kasar Sin

A nasa bangare, Kyriakos Mitsotakis ya ce, a shirye kasarsa take ta ci gaba da inganta hadin gwiwar shawarar “Ziri Daya da Hanya Daya” da kasar Sin, da kara ci gajiya da fadada damarmakin hadin gwiwa a fannonin jiragen ruwa da sufurin jiragen ruwa da makamashi mai tsafta, tana mai fatan karin kayayyakin kasar za su shiga kasuwar kasar Sin tare da maraba da masu yawon bude ido na Sin a Girka.

Sannan, shugaba Xi Jinping ya kuma gana da shugaban gwamnatin kasar Jamus Olaf Scholz yau Juma’a ta kafar bidiyo.

Xi
Shugaba Xi da Takwaransa na Girka

A cewar Xi Jinping, a yanzu haka, cinikayya tsakanin Sin da Jamus na samun ci gaba yadda ya kamata, kuma yawan jari a tsakaninsu ma na karuwa, baya ga dangantakarsu dake kara kyautatuwa da kara karfi da samun nasarori.

Labarai Masu Nasaba

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Sama da kamfanonin Jamus 130 ne za su halarci baje kolin kayayyakin da ake shigo da su kasar Sin CIIE karo na 6, wanda ke nuna kwarin gwiwar da kamfanonin Jamus din ke da shi kan ci gaban Sin. Ana kuma fatan bangaren Jamus zai nace ga fadada bude kofar hadin gwiwa ga kamfanonin kasar Sin.

A nasa bangare, Olaf Scholz ya bayyana ra’ayin kasarsa game da rikicin Palasdinu da Isra’ila, yana mai fatan ci gaba da tuntubar juna tsakanin Jamus da Sin kan batun.

Game da hakan, Xi Jinping ya ce idan ana son warware tushen rikicin Palasdinu da Isra’ila ko kuma rikicin Ukraine, to akwai bukatar yin tunani mai zurfi a bangaren tsaro, da nacewa ga samar da cikakken tsaro na bai daya cikin hadin gwiwa da samar da ingantaccen tsarin tsaro mai dorewa kuma bisa adalci. (Fa’iza Mustapha)

(Fa’iza Mustapha)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaGirkaJamus
ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Jinping Ya Taya Murnar Gudanar Da Babban Taron Birane Masu Sada Zumunta Na Sin Da Amurka

Next Post

NLC Za Ta Shiga Yajin Aiki Kan Cin Zarafin Shugabanta, Ajaero

Related

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru
Manyan Labarai

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

9 hours ago
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu
Ilimi

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

14 hours ago
Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?
Labarai

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

15 hours ago
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya
Kotu Da Ɗansanda

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

16 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

17 hours ago
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano
Manyan Labarai

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

18 hours ago
Next Post
NLC Za Ta Shiga Yajin Aiki Kan Cin Zarafin Shugabanta, Ajaero

NLC Za Ta Shiga Yajin Aiki Kan Cin Zarafin Shugabanta, Ajaero

LABARAI MASU NASABA

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

August 24, 2025
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

August 23, 2025
Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

August 23, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

August 23, 2025
Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

August 23, 2025
Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

August 23, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

August 23, 2025
Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

August 23, 2025
Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.