• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kungiyoyi Sun Nemi Majalisar Dattawa Ta Sa Baki A Cire Karamin Ministan Tsaro

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Kungiyoyi Sun Nemi Majalisar Dattawa Ta Sa Baki A Cire Karamin Ministan Tsaro
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wata ƙungiya ta gamayyar ƙungiyoyin rajin kare dimokuraɗiyya da haƙƙin dan Adam, CSAGP, sun gudanar da zanga-zanga a hanyar shiga harabar Majalisar Dattawa, inda suke neman a cire Ƙaramin Ministan Tsaro, tsohon gwamnan jihar Zamfara, Bello Matawalle.

Masu zanga-zangar na so a cire Matawalle ne  sabida zarginsa da Gwamnatin Zamfara ta yi kan harƙallar “sace kuɗaɗe da batun matsalar ‘yan bindiga a jihar.”

  • Majalisa Ta Soke Bukatar Siyo Jirgin Ruwan Shugaban Kasa, Ta Kara Kudin Ga Lamunin Dalibai
  • Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Da Kafa Kamfanin Abinci Na ‘Arla’

An ga masu zanga-zangar a hanyar zuwa Majalisar Ƙasa dauke da kwalaye da alluna da rubutu akai a ranar Talata, suna kira ga Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio ya nusar da Shugaban Ƙasa Bola Tinubu, domin ya tsige Matawalle.

 

Masu zanga-zangar waɗanda ake kiran gamayyar ƙungiyar ta su da suna ‘Civil Society Advocacy Groups and Probity’, sun kuma zargi Minista Matawalle da laifin jawo ‘yan bindiga a jiki, lamarin da suka ce ya haifar da asarar ɗimbin rayuka da dama a Zamfara da asarar dukiyoyi na Biliyoyin Nairori.

Labarai Masu Nasaba

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Gungun gamayyar ƙungiyar a ƙarƙashin Danesi Momoh, a wani taron manema labarai a ranar Lahadi ya yi kira da a sauke Karamin Ministan Harkokin Tsaron tun a baya.

‘Yan watanni kaɗan kafin saukarsa daga kan kujerar Gwamnatin Zamfara a ranar 29 ga Mayu, EFCC ta zargi Matawalle da karkatar da Naira biliyan 70 na al’ummar jihar, lamarin da ya haifar da ce-ce-ku-ce tsakaninsa da shugaban EFCC na lokacin, Abdulrasheed Bawa.

Masu zanga-zangar sun damƙa wa Majalisar Dattawa takardar ƙorafi domin isarwa ga Shugaban Majalisar Dattawa, Akpabio, mai ɗauke da zargin cewa, mutum kamar Matawalle ba abin bai wa amanar tsaron ƙasa ba ne, musamman muƙami mai muhimmanci a Ma’aikatar Harkokin Tsaro.

Sun kafa hujjojinsu da dalilansu kan wasu zarge-zargen da Gwamantin Zamfara ta watsa kuma ta wallafa, mai nuni kan yadda Matawalle ya karkatar da Biliyoyin Nairorin Zamfara, a harƙallar kwangiloli daban-daban, ciki har da kwangilar gina filin jirgin saman saukale da lodin kaya a Gusau.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Bello MatawalleMa'aikatar tsaroZamafara
ShareTweetSendShare
Previous Post

NLC Za Ta Shiga Yajin Aiki Kan Cin Zarafin Shugabanta, Ajaero

Next Post

Ministan Wajen Sin Ya Yi Kira Da A Tsagaita Wuta A Gaza

Related

Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

6 hours ago
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro
Tsaro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

8 hours ago
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu
Labarai

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

9 hours ago
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta
Manyan Labarai

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

11 hours ago
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai
Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

13 hours ago
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro
Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

14 hours ago
Next Post
Ministan Wajen Sin Ya Yi Kira Da A Tsagaita Wuta A Gaza

Ministan Wajen Sin Ya Yi Kira Da A Tsagaita Wuta A Gaza

LABARAI MASU NASABA

Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

September 13, 2025
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.