• English
  • Business News
Tuesday, July 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kungiyoyi Sun Nemi Majalisar Dattawa Ta Sa Baki A Cire Karamin Ministan Tsaro

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Kungiyoyi Sun Nemi Majalisar Dattawa Ta Sa Baki A Cire Karamin Ministan Tsaro
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wata ƙungiya ta gamayyar ƙungiyoyin rajin kare dimokuraɗiyya da haƙƙin dan Adam, CSAGP, sun gudanar da zanga-zanga a hanyar shiga harabar Majalisar Dattawa, inda suke neman a cire Ƙaramin Ministan Tsaro, tsohon gwamnan jihar Zamfara, Bello Matawalle.

Masu zanga-zangar na so a cire Matawalle ne  sabida zarginsa da Gwamnatin Zamfara ta yi kan harƙallar “sace kuɗaɗe da batun matsalar ‘yan bindiga a jihar.”

  • Majalisa Ta Soke Bukatar Siyo Jirgin Ruwan Shugaban Kasa, Ta Kara Kudin Ga Lamunin Dalibai
  • Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Da Kafa Kamfanin Abinci Na ‘Arla’

An ga masu zanga-zangar a hanyar zuwa Majalisar Ƙasa dauke da kwalaye da alluna da rubutu akai a ranar Talata, suna kira ga Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio ya nusar da Shugaban Ƙasa Bola Tinubu, domin ya tsige Matawalle.

 

Masu zanga-zangar waɗanda ake kiran gamayyar ƙungiyar ta su da suna ‘Civil Society Advocacy Groups and Probity’, sun kuma zargi Minista Matawalle da laifin jawo ‘yan bindiga a jiki, lamarin da suka ce ya haifar da asarar ɗimbin rayuka da dama a Zamfara da asarar dukiyoyi na Biliyoyin Nairori.

Labarai Masu Nasaba

Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace

Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang

Gungun gamayyar ƙungiyar a ƙarƙashin Danesi Momoh, a wani taron manema labarai a ranar Lahadi ya yi kira da a sauke Karamin Ministan Harkokin Tsaron tun a baya.

‘Yan watanni kaɗan kafin saukarsa daga kan kujerar Gwamnatin Zamfara a ranar 29 ga Mayu, EFCC ta zargi Matawalle da karkatar da Naira biliyan 70 na al’ummar jihar, lamarin da ya haifar da ce-ce-ku-ce tsakaninsa da shugaban EFCC na lokacin, Abdulrasheed Bawa.

Masu zanga-zangar sun damƙa wa Majalisar Dattawa takardar ƙorafi domin isarwa ga Shugaban Majalisar Dattawa, Akpabio, mai ɗauke da zargin cewa, mutum kamar Matawalle ba abin bai wa amanar tsaron ƙasa ba ne, musamman muƙami mai muhimmanci a Ma’aikatar Harkokin Tsaro.

Sun kafa hujjojinsu da dalilansu kan wasu zarge-zargen da Gwamantin Zamfara ta watsa kuma ta wallafa, mai nuni kan yadda Matawalle ya karkatar da Biliyoyin Nairorin Zamfara, a harƙallar kwangiloli daban-daban, ciki har da kwangilar gina filin jirgin saman saukale da lodin kaya a Gusau.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Bello MatawalleMa'aikatar tsaroZamafara
ShareTweetSendShare
Previous Post

NLC Za Ta Shiga Yajin Aiki Kan Cin Zarafin Shugabanta, Ajaero

Next Post

Ministan Wajen Sin Ya Yi Kira Da A Tsagaita Wuta A Gaza

Related

Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace
Manyan Labarai

Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace

53 minutes ago
Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang
Labarai

Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang

2 hours ago
Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu
Labarai

Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu

4 hours ago
Birtaniya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Mutane 33 A Zamfara
Labarai

Birtaniya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Mutane 33 A Zamfara

5 hours ago
Mai Cin Moriyar Kai Da Mai Cin Moriyar Juna
Ra'ayi Riga

Mai Cin Moriyar Kai Da Mai Cin Moriyar Juna

5 hours ago
Kar Ka Zuga Ƴan Arewa Kan Tinubu — Nabena Ya Gargaɗi Kwankwaso
Labarai

Kar Ka Zuga Ƴan Arewa Kan Tinubu — Nabena Ya Gargaɗi Kwankwaso

6 hours ago
Next Post
Ministan Wajen Sin Ya Yi Kira Da A Tsagaita Wuta A Gaza

Ministan Wajen Sin Ya Yi Kira Da A Tsagaita Wuta A Gaza

LABARAI MASU NASABA

Fiye Da Kamfanoni 30,000 Masu Zuba Jari Daga Waje Aka Kafa A Sin A Rabin Farkon Bana

Fiye Da Kamfanoni 30,000 Masu Zuba Jari Daga Waje Aka Kafa A Sin A Rabin Farkon Bana

July 29, 2025
Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace

Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace

July 29, 2025
Sojojin Sin Sun Bi Sahun Shiga Ayyukan Ba Da Agajin Ambaliyar Ruwa

Sojojin Sin Sun Bi Sahun Shiga Ayyukan Ba Da Agajin Ambaliyar Ruwa

July 29, 2025
Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang

Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang

July 29, 2025
Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa

Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa

July 29, 2025
Morocco Ta Shigar Da Ƙara Kan Nasarar Super Falcons A Gasar WAFCON

Morocco Ta Shigar Da Ƙara Kan Nasarar Super Falcons A Gasar WAFCON

July 29, 2025
An Fitar Da Kudaden Farfado Da Sassan Birnin Beijing Da Bala’in Ambaliyar Ruwa Ya Shafa

An Fitar Da Kudaden Farfado Da Sassan Birnin Beijing Da Bala’in Ambaliyar Ruwa Ya Shafa

July 29, 2025
Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu

Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu

July 29, 2025
Xi Ya Yi Kira Da A Yi Azamar Kare Rayukan Al’umma Yayin Da Ake Fuskantar Ibtila’in Ambaliya A Wasu Sassan Kasar Sin

Xi Ya Yi Kira Da A Yi Azamar Kare Rayukan Al’umma Yayin Da Ake Fuskantar Ibtila’in Ambaliya A Wasu Sassan Kasar Sin

July 29, 2025
Birtaniya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Mutane 33 A Zamfara

Birtaniya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Mutane 33 A Zamfara

July 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.