• English
  • Business News
Wednesday, November 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hadarin Da Ya Auku Ya Bankado Karyar Japan Game Da Ruwan Dagwalon Nukiliyar Da Take Zubarwa A Teku

by CGTN Hausa
2 years ago
Teku

Duk da kakkarfar adawa daga gida da waje, kamfanin samar da lantarki na 2 na Tokyo ko TEPCO dake kasar Japan, ya fara zubar da ruwan dagwalon nukiliyar Fukushima cikin teku a zagaye na 3, aikin da ake fatan ci gaba da gudanarwa har zuwa ranar 20 ga watan nan na Nuwamba, kuma adadin ruwan da za a juye a wannan lokaci zai kai kusan tan 7,800.

Sai dai duk da haka, mako guda da ya gabata, kamfanin ya gamu da hadarin fitar birbishin “radioactive”, wanda ya jefa 2 daga cikin ma’aikatan kamfanin cikin hadari, aka kuma garzaya da su zuwa asibiti. Wannan lamari ya karyata ikirarin Japan, na cewa ruwan dagwalon da take zubarwa a teku ba shi da hadari, kuma bai dace a yi wasa da hadarin dake tattare da hadarin birbishin nukiliya dake cikin ruwan ba.

  • Kungiyar ‘One Germany’ Ta Fara Gangamin Samar Da Karin Masu Zuba Jari A Afirika
  • Xi Ya Gana Da Firaministan Girka Da Yin Tattaunawa Da Shugaban Gwamnatin Jamus

Bayan aukuwar wannan hadari, jami’an hukumar lura da sana’ar kamun kifi ta Fukushima, sun ce ba su da sauran kwarin gwiwa game da kamfanin TEPCO. Kaza lika rahotanni daga wasu kafofin watsa labarai na nuna cewa, da yawa daga manyan jami’an kasar Japan da suka yi ritaya, suna aiki a kamfanin na TEPCO a matsayin masu ba da shawarwari, kuma wasu jami’ai dake aiki a sashen masana’antun nukiliyar kasar za su shiga gwamnatin ta Japan a matsayin rukunin masu ba da shawara.

Yanzu haka dai watanni biyu ke nan tun bayan da kasar Japan ta fara zubar da ruwan dagwalon nukiliyarta cikin teku. Sai dai abun da ya faru na hadari a baya bayan nan, ya tabbatar da bukatar da ake da ita, ta aiwatar da tsare tsaren sanya ido na kasa da kasa na dogon lokaci, kuma masu inganci.

Idan har da gaske ne kasar Japan tana da karfin gwiwa game da rashin hadarin wannan mataki nata, to kamata ya yi ta zubar da ruwan dagwalon bisa hangen nesa, kana ta goyi bayan kafuwar tsarin sanya ido na dogon lokaci, tare da halartar dukkanin masu ruwa da tsaki, ciki har da sanya ido daga sassa masu zaman kansu daga wasu kasashe.

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

Teku dai tamkar gida ne na bai daya ga daukacin bil Adama, kuma bai dace sauran sassan duniya su dauki alhakin son zuciyar kasar Japan ba. (Saminu Alhassan)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika
Daga Birnin Sin

Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

November 4, 2025
‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba
Daga Birnin Sin

‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

November 4, 2025
Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar
Daga Birnin Sin

Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar

November 4, 2025
Next Post
Bashin Biliyan 500 Da Ganduje Ya Bari Ne Ya Hana Mu Fara Aiki Akan Lokaci – Abba

Bashin Biliyan 500 Da Ganduje Ya Bari Ne Ya Hana Mu Fara Aiki Akan Lokaci - Abba

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

November 4, 2025
Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

November 4, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Ceto Mutane 3 Da Aka Sace A Kwara

November 4, 2025
‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

November 4, 2025
tinubu

Tinubu Ya Umarci Ma’aikatar Ilimi Ta Kawo Ƙarshen Yajin Aikin ASUU

November 4, 2025
Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar

Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar

November 4, 2025
2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC

2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC

November 4, 2025
Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

November 4, 2025
Karancin Abinci: Kofar Ofishin Tinubu A Rufe Take, Har Wasu Ministoci Ba Su Iya Ganinsa – Ndume 

Zargin Kisan Kiyashi Ga Kiristoci: Trump Bai San Ƙalubalen Tsaron Da Najeriya Ke Ciki Ba — Ndume

November 4, 2025
Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

November 4, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.