• English
  • Business News
Saturday, October 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin Bayan Zabe: Bamu Amince Da Sakamakon Zaben Sanata A Adamawa Ba – ‘Yan Takara 5

by Muh'd Shafi'u Saleh
3 years ago
Zabe

Bisa zargin aikata ba daidai ba, lokacin gudanar da zaben kujerar dan majalisar dattawa mai wakiltar Adamawa ta kudu, ‘yan takara 5, sunki amincewa da sakamamon zaben fidda gwanin bisa zargin ba’abi ka’ida ba.

‘Yan takaran biyar, sun roki kwamitin gudanar da zaben da ta sanar da Adamu Isma’ila Numun da cewa ya lashe zaben, da ta soke takaransa, bisa cewa ya karya dokar zabe, da sayen kuri’u, don haka bai cancanci tsayawa takaran ba.

  • Kama Ta Ya Yi APC Ta Fitar Da Dan Takarar Shugaban Kasa Daga Kudu —Sanata Gaya

Da su ke magana da ‘yan jaridu a Yola, ‘yan takaran Baresta Bala Sanga, Bridget Zidon, Grace Bent, Sani Jada, Ahmad Abubakar, sun tabbatar da cewa basu shiga zaben da’akace Adamu Isma’ila ya lashe zaben ba.

Da yake magana amadadin ‘yan takaran Baresta Sanga yace “bukatarmu shine su yi amfani da takardar da muka basu ranar 29 ga Mayu 2022, cewa Adamu Isma’ila Numun, bai cancanci takara ba, saboda sayen kuri’un da yayi, lokacin zabe.

“Wannan abin kunya ne ga jam’iyya, a kafa wani kwamitin da zai gudanar da sabon zabe, kuma a canja wurin gudanar da zaben, daga Numan zuwa inda ya dace a yankin.

LABARAI MASU NASABA

Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta

ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa

“Mun gaskata jam’iyyar APC zata gudanar mana da adalci, duk da ba’a da kaskancin da Adamu Isma’ila Numan, ya shigo dashi, bamu cire tsammani ga bukatunmu ba, muna zaman jiran mu bayyana gaban kwamitin amsar koke” inji Sanga.

‘Yan takaran sun kuma bayyana cewa ba’ayi zaben fidda gwani a yankin ba, ya kamata a gudanar da zaben a ranar 29 ga Mayu 2022, duk mu bama wurin, mu munyi imanin an tsara ne da raba mana kuri’un.

“Mafiya yawan masu zabenmu sun koma garuruwansu, kuma gurare ne mai nisa, kusan mutum zaiyi awa 4, abune da ba zai yiwu ba ka taro duka masu zabe, duk da babu masu zabemmu da masu sa mana ido, a zahiri ci gaba da zabe a haka abin kunya ne.

“A irin wannan zaben fidda gwanin da takardar kada kuri’a, da duk ‘yan takara, da masu sa ido, za su amince, mu ‘yan takara da masu sa mana ido bamu a wurin zabe, sunyi abinda ya musu ne kawai.

“Muna bukatar kwamitin sauraren koke-koken zabe ta lura da wadannan manyan batutuwa wadanda suke nuna makurar rashin adalci, an tura mana sako karfe 8:54 na safe cewa za’ayi zaben 12 na rana.

“Kawai awanni uku da mintuna 6 aka bamu, mu shirya a yi zaben fidda gwanin, yaushe zamu tattaro kan masu zabenmu? Wannan wani irin makoran rashin adalci ne” inji Sanga.

Da yake maida kalami kan zargin da ‘yan takaran sukayi Adamu Isma’ila Numan, yace “kawai don basu sukayi nasara bane, dabi’ace ta wanda ya fadi zabe

“Tunda farko mun yarda masu sa mana ido, su taimakawa wadanda basu iya rubutu ba, lokacin da mai sa mini ido zai taimaki mai zabena, suka fara cewa sayen kuri’u sayen kuri’u.

“Ni bansan komai akan haka ba, ni ban umurci wani ko wasu su dauki doka a hannu amadadina ba, amma aka dakatar da zaben.

“Lokacin da’aka sanar za’ayi zabe, na nemo masu sa mini ido da masu zabe, mun tafi wurin zabe mukayi zabe kuma munci zaben” inji Numun.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta
Siyasa

Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta

October 24, 2025
ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa
Siyasa

ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa

October 22, 2025
Babu Rikici A Jam’iyyar APC A Nasarawa — Shugaban Jam’iyya
Siyasa

Babu Rikici A Jam’iyyar APC A Nasarawa — Shugaban Jam’iyya

October 21, 2025
Next Post
Yadda Aka Yi Wa Wata Mata Yankan Rago A Hadejia

Yadda Aka Yi Wa Wata Mata Yankan Rago A Hadejia

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

October 25, 2025

Bankin Providus

October 25, 2025
Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki

Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki

October 25, 2025

Hukumar NASENI

October 25, 2025
An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 80 Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan Da Dawo Da Shi Kasar Sin A Beijing

An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 80 Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan Da Dawo Da Shi Kasar Sin A Beijing

October 25, 2025

Daɓid Adeyemi

October 25, 2025
Wakilin Sin: Shawarar GGI Ta Nuna Yadda Za A Jagoranci Bunkasa Makomar MDD

Wakilin Sin: Shawarar GGI Ta Nuna Yadda Za A Jagoranci Bunkasa Makomar MDD

October 25, 2025
Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka

Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka

October 25, 2025
Kasar Sin Ta Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Na 15

Kasar Sin Ta Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Na 15

October 25, 2025
Gwarzon Mai Koyar Da Wasanni Na Shekarar 2025 Justine Madugu

Gwarzon Mai Koyar Da Wasanni Na Shekarar 2025 Justine Madugu

October 25, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.