ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin Bayan Zabe: Bamu Amince Da Sakamakon Zaben Sanata A Adamawa Ba – ‘Yan Takara 5

by Muh'd Shafi'u Saleh
4 years ago
Zabe

Bisa zargin aikata ba daidai ba, lokacin gudanar da zaben kujerar dan majalisar dattawa mai wakiltar Adamawa ta kudu, ‘yan takara 5, sunki amincewa da sakamamon zaben fidda gwanin bisa zargin ba’abi ka’ida ba.

‘Yan takaran biyar, sun roki kwamitin gudanar da zaben da ta sanar da Adamu Isma’ila Numun da cewa ya lashe zaben, da ta soke takaransa, bisa cewa ya karya dokar zabe, da sayen kuri’u, don haka bai cancanci tsayawa takaran ba.

  • Kama Ta Ya Yi APC Ta Fitar Da Dan Takarar Shugaban Kasa Daga Kudu —Sanata Gaya

Da su ke magana da ‘yan jaridu a Yola, ‘yan takaran Baresta Bala Sanga, Bridget Zidon, Grace Bent, Sani Jada, Ahmad Abubakar, sun tabbatar da cewa basu shiga zaben da’akace Adamu Isma’ila ya lashe zaben ba.

ADVERTISEMENT

Da yake magana amadadin ‘yan takaran Baresta Sanga yace “bukatarmu shine su yi amfani da takardar da muka basu ranar 29 ga Mayu 2022, cewa Adamu Isma’ila Numun, bai cancanci takara ba, saboda sayen kuri’un da yayi, lokacin zabe.

“Wannan abin kunya ne ga jam’iyya, a kafa wani kwamitin da zai gudanar da sabon zabe, kuma a canja wurin gudanar da zaben, daga Numan zuwa inda ya dace a yankin.

LABARAI MASU NASABA

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

“Mun gaskata jam’iyyar APC zata gudanar mana da adalci, duk da ba’a da kaskancin da Adamu Isma’ila Numan, ya shigo dashi, bamu cire tsammani ga bukatunmu ba, muna zaman jiran mu bayyana gaban kwamitin amsar koke” inji Sanga.

‘Yan takaran sun kuma bayyana cewa ba’ayi zaben fidda gwani a yankin ba, ya kamata a gudanar da zaben a ranar 29 ga Mayu 2022, duk mu bama wurin, mu munyi imanin an tsara ne da raba mana kuri’un.

“Mafiya yawan masu zabenmu sun koma garuruwansu, kuma gurare ne mai nisa, kusan mutum zaiyi awa 4, abune da ba zai yiwu ba ka taro duka masu zabe, duk da babu masu zabemmu da masu sa mana ido, a zahiri ci gaba da zabe a haka abin kunya ne.

“A irin wannan zaben fidda gwanin da takardar kada kuri’a, da duk ‘yan takara, da masu sa ido, za su amince, mu ‘yan takara da masu sa mana ido bamu a wurin zabe, sunyi abinda ya musu ne kawai.

“Muna bukatar kwamitin sauraren koke-koken zabe ta lura da wadannan manyan batutuwa wadanda suke nuna makurar rashin adalci, an tura mana sako karfe 8:54 na safe cewa za’ayi zaben 12 na rana.

“Kawai awanni uku da mintuna 6 aka bamu, mu shirya a yi zaben fidda gwanin, yaushe zamu tattaro kan masu zabenmu? Wannan wani irin makoran rashin adalci ne” inji Sanga.

Da yake maida kalami kan zargin da ‘yan takaran sukayi Adamu Isma’ila Numan, yace “kawai don basu sukayi nasara bane, dabi’ace ta wanda ya fadi zabe

“Tunda farko mun yarda masu sa mana ido, su taimakawa wadanda basu iya rubutu ba, lokacin da mai sa mini ido zai taimaki mai zabena, suka fara cewa sayen kuri’u sayen kuri’u.

“Ni bansan komai akan haka ba, ni ban umurci wani ko wasu su dauki doka a hannu amadadina ba, amma aka dakatar da zaben.

“Lokacin da’aka sanar za’ayi zabe, na nemo masu sa mini ido da masu zabe, mun tafi wurin zabe mukayi zabe kuma munci zaben” inji Numun.

Zabe
Muh'd Shafi'u Saleh
+ postsBio
  • Muh'd Shafi'u Saleh
    https://hausa.leadership.ng/author/muhd-shafiu-saleh/
    Jami’in Tsaro Ya Mayar da Dala 505 Da Riyal 30 Da Ya Tsinta A Yola
  • Muh'd Shafi'u Saleh
    https://hausa.leadership.ng/author/muhd-shafiu-saleh/
    Shahararren Malamin Addinin Islama A Adamawa Sheikh Ibrahim Abubakar Daware Ya Rasu
  • Muh'd Shafi'u Saleh
    https://hausa.leadership.ng/author/muhd-shafiu-saleh/
    An Yi Wa ‘Yansanda 110 Ƙarin Girma A Adamawa
  • Muh'd Shafi'u Saleh
    https://hausa.leadership.ng/author/muhd-shafiu-saleh/
    Gwamna Fintiri Ya Nada Sabbin Sarakuna 7 A Jihar Adamawa

MASU ALAKA

2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa
Siyasa

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

June 22, 2026
Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP
Siyasa

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

June 22, 2026
ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027
Siyasa

ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027

June 21, 2026
Next Post
Yadda Aka Yi Wa Wata Mata Yankan Rago A Hadejia

Yadda Aka Yi Wa Wata Mata Yankan Rago A Hadejia

LABARAI MASU NASABA

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.