• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

CIIE Na Da Matukar Muhimmanci Ga Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya

by CGTN Hausa
2 years ago
CIIE

Tun lokacin da aka fara gudanar da baje kolin kayayyakin da ake shigowa da su kasar Sin ko CIIE a takaice a shekarar 2018, kasashe masu halartar baje kolin na shekara-shekara sun yi amfani da tasirin girmar kasuwar kasar Sin, wanda ya kasance dandalin hada-hadar cinikayya na kasa da kasa, da inganta zuba jari, da mu’amalar jama’a da yin hadin gwiwa, da ba da gudummawa mai kyau wajen samar da sabbin tsarin ci gaba, da sa kaimi ga bunkasuwar tattalin arzikin duniya.  

 

La’akari da tafiyar hawainiyar da tattalin arzikin duniya ke yi biyo bayan rashin cikakkiyar farfadowa daga tasirin annobar COVID 19, shugaba Xi Jinping a cikin wasikarsa na bikin bude baje kolin a jiya Lahadi ya ce, kasar Sin za ta kasance wata muhimmiyar dama ta ci gaban duniya a ko da yaushe, kuma za ta ci gaba da bude kofa ga kasashen waje, da kuma ci gaba da sa kaimi ga bunkasuwar tattalin arzikin duniya, ta hanyar ci gaba da inganta baje kolin na kayayyaki da ake shigowa da su kasar daga kasashen waje.

  • Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Yin Iyakar Kokarin Saukaka Rikicin Gaza
  • Xi Jinping Ya Taya Murnar Gudanar Da Babban Taron Birane Masu Sada Zumunta Na Sin Da Amurka

Baje kolin CIIE na bana ya jawo hankalin mahalarta daga kasashe, yankuna da kungiyoyin kasa da kasa 154. Sama da masu baje kolin 3,400 da kwararrun baki 394,000 suka yi rajista don halartar taron, wanda ke nuni da cikakkiyar karbuwar baje kolin.

Daga cikin kamfanoni 3,000 na duniya dake halartar baje kolin na wannan shekara, kusan kamfanoni 200 ne suka halarci baje kolin tun daga shekarar 2018 har ya zuwa yanzu, kuma kusan kamfanoni 400 ne ke dawowa baje kolin bayan duk shekaru biyu.

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

 

Yawancin kamfanonin kasashen waje da ke gudanar da kasuwanci a kasar Sin suna da kwarin gwiwa game da ci gaba da gudanar da kasuwancinsu a kasar, inda sama da kashi 90 cikin 100 na wadannan kamfanonin suna sa ran za su maido da jarinsu ko ribar da suke samu zai karu a cikin shekaru biyar masu zuwa ko kasa da haka, a cewar wani bincike na baya-bayan nan da Majalisar Bunkasa Harkokin Cinikayya ta Duniya ta gudanar a kasar Sin.

 

Binciken ya kuma nuna cewa, kamfanonin kasashen waje sun nuna kwarin gwiwar fadada hada-hadarsu na kasuwanci a kasar Sin, yayin da sama da kashi 70 cikin 100 na wadanda suka amsa tambayoyin binciken suka ce za su dawo da wasu sassan masana’antunsu kasar Sin.

 

Alkalumma a hukumance sun nuna cewa, hada-hadar kayayyakin da kasar Sin ke shigowa da su kasar na ci gaba da tafiya yadda ya kamata, inda yawan kayayyaki da take shigowa da su ya karu a kowane rubu’i na bana. Kasar Sin ta kasance kasa ta biyu a fannin shigo da kayayyaki a duniya tsawon shekaru 14 a jere.

“Baje kolin ya nuna cewa, kasar Sin a bude take don yin kasuwanci da sauran kasashen duniya. Wannan wata babbar dama ce ga kasashe daban-daban su yi baje kolin hajojinsu da fasahohinsu.”

 

Baya ga bayar da damammaki ga kasashe masu tasowa da kasuwanni masu tasowa, baje kolin CIIE ya kasance dandalin sada zumunta da kamfanonin kasar Sin ta hanyar yin hadin gwiwa da kamfanonin kasashen waje don samar da kayayyaki ko ayyuka ga kasuwannin kasar Sin ko na duniya baki daya. (Muhammed Yahaya)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko
Daga Birnin Sin

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan
Daga Birnin Sin

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana
Daga Birnin Sin

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Next Post
CIIE

Bikin CIIE Ya Sa Kayayyakin Kasashen Afirka Samun Karbuwa

LABARAI MASU NASABA

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.