ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

CIIE Na Da Matukar Muhimmanci Ga Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya

by CGTN Hausa
3 years ago
CIIE

Tun lokacin da aka fara gudanar da baje kolin kayayyakin da ake shigowa da su kasar Sin ko CIIE a takaice a shekarar 2018, kasashe masu halartar baje kolin na shekara-shekara sun yi amfani da tasirin girmar kasuwar kasar Sin, wanda ya kasance dandalin hada-hadar cinikayya na kasa da kasa, da inganta zuba jari, da mu’amalar jama’a da yin hadin gwiwa, da ba da gudummawa mai kyau wajen samar da sabbin tsarin ci gaba, da sa kaimi ga bunkasuwar tattalin arzikin duniya.  

 

La’akari da tafiyar hawainiyar da tattalin arzikin duniya ke yi biyo bayan rashin cikakkiyar farfadowa daga tasirin annobar COVID 19, shugaba Xi Jinping a cikin wasikarsa na bikin bude baje kolin a jiya Lahadi ya ce, kasar Sin za ta kasance wata muhimmiyar dama ta ci gaban duniya a ko da yaushe, kuma za ta ci gaba da bude kofa ga kasashen waje, da kuma ci gaba da sa kaimi ga bunkasuwar tattalin arzikin duniya, ta hanyar ci gaba da inganta baje kolin na kayayyaki da ake shigowa da su kasar daga kasashen waje.

ADVERTISEMENT
  • Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Yin Iyakar Kokarin Saukaka Rikicin Gaza
  • Xi Jinping Ya Taya Murnar Gudanar Da Babban Taron Birane Masu Sada Zumunta Na Sin Da Amurka

Baje kolin CIIE na bana ya jawo hankalin mahalarta daga kasashe, yankuna da kungiyoyin kasa da kasa 154. Sama da masu baje kolin 3,400 da kwararrun baki 394,000 suka yi rajista don halartar taron, wanda ke nuni da cikakkiyar karbuwar baje kolin.

Daga cikin kamfanoni 3,000 na duniya dake halartar baje kolin na wannan shekara, kusan kamfanoni 200 ne suka halarci baje kolin tun daga shekarar 2018 har ya zuwa yanzu, kuma kusan kamfanoni 400 ne ke dawowa baje kolin bayan duk shekaru biyu.

LABARAI MASU NASABA

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

 

Yawancin kamfanonin kasashen waje da ke gudanar da kasuwanci a kasar Sin suna da kwarin gwiwa game da ci gaba da gudanar da kasuwancinsu a kasar, inda sama da kashi 90 cikin 100 na wadannan kamfanonin suna sa ran za su maido da jarinsu ko ribar da suke samu zai karu a cikin shekaru biyar masu zuwa ko kasa da haka, a cewar wani bincike na baya-bayan nan da Majalisar Bunkasa Harkokin Cinikayya ta Duniya ta gudanar a kasar Sin.

 

Binciken ya kuma nuna cewa, kamfanonin kasashen waje sun nuna kwarin gwiwar fadada hada-hadarsu na kasuwanci a kasar Sin, yayin da sama da kashi 70 cikin 100 na wadanda suka amsa tambayoyin binciken suka ce za su dawo da wasu sassan masana’antunsu kasar Sin.

 

Alkalumma a hukumance sun nuna cewa, hada-hadar kayayyakin da kasar Sin ke shigowa da su kasar na ci gaba da tafiya yadda ya kamata, inda yawan kayayyaki da take shigowa da su ya karu a kowane rubu’i na bana. Kasar Sin ta kasance kasa ta biyu a fannin shigo da kayayyaki a duniya tsawon shekaru 14 a jere.

“Baje kolin ya nuna cewa, kasar Sin a bude take don yin kasuwanci da sauran kasashen duniya. Wannan wata babbar dama ce ga kasashe daban-daban su yi baje kolin hajojinsu da fasahohinsu.”

 

Baya ga bayar da damammaki ga kasashe masu tasowa da kasuwanni masu tasowa, baje kolin CIIE ya kasance dandalin sada zumunta da kamfanonin kasar Sin ta hanyar yin hadin gwiwa da kamfanonin kasashen waje don samar da kayayyaki ko ayyuka ga kasuwannin kasar Sin ko na duniya baki daya. (Muhammed Yahaya)

CIIE
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

MASU ALAKA

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
Daga Birnin Sin

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
Daga Birnin Sin

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Next Post
CIIE

Bikin CIIE Ya Sa Kayayyakin Kasashen Afirka Samun Karbuwa

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.