• English
  • Business News
Tuesday, July 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

AGOA: Tallafi ko Makami?

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
AGOA: Tallafi ko Makami?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A farkon wannan mako ne, shugaban Uganda Yoweri Museveni, ya soki matakin Amurka na cire kasarsa daga yarjejeniyar cinikayya ta AGOA, saboda abun da Amurka ta kira “take hakkokin bil adama”.

AGOA, yarjejeniya ce da Amurka ta gabatar a shekarar 2000 domin ba kasashen kudu da hamadar Sahara damar shigar da wasu kayayyaki sama da 1,800 cikin Amurkar ba tare da biyan haraji ba.

  • Kalaman Amurka Zai Iya Shafar Tattalin Arzikin Nijeriya – Minista
  • Bikin CIIE Ya Sa Kayayyakin Kasashen Afirka Samun Karbuwa

Sai dai, matakin Amurka ya sa alamar tambaya kan me taimakonta ke nufi: tallafi domin ci gaban kasashe ko kuma makamin tilasta musu akidunta? Matakin Amurka ya bayyana karara yadda take mayar da hankali wajen neman kakabawa kasashe masu tasowa ra’ayoyi da akidunta, ko da kuwa ba su dace da bukatu ko muradun wadancan kasashe ba. Amurka ta kan yi amfani da karfinta da tallafin da take ba kasashe masu karancin kudin shiga a matsayin wani makami na juya su yadda ta ga dama. Ta manta cewa, su ma ’yantattun kasashe ne dake da ikon cin gashin kansu da zartar da dokokin da suka dace da su.

Kasashen duniya sun bambanta da juna, al’adu ko addini ko kabila, ba za su taba zama iri daya ba. Kuma wannan bambancin shi ne ke kara kawata zaman rayuwa da koya mana yadda za mu zauna tare bisa girmamawa da hakuri da juna, kamar yadda shawarar kasar Sin ta wayewar kan duniya wato GCI ta gabatar, wato zaman jituwa da koyi da juna tsakanin mabanbanta al’ummomin duniya. Kowace kasa a duniya na da ikon zabarwa kanta dokokin da suka dace da ita. Uganda ta zabi zartar da dokar hana auren jinsi, abun da ya kamata Amurka ta yi shi ne, girmama zabin Uganda, da kaucewa tsoma baki cikin al’amuranta na ci gida. Cire sunan wasu kasashe da ta yi daga yarjejeniyar AGOA ya nuna cewa, ba ci gabansu take nema ba kamar yadda take ikirari, cin zali da yadda za ta kasance mai babakere a duniya, shi ne burinta.

Amurka ta kan zartar da dokoki ko aiwatar da ayyuka, amma wadannan kasashe ba sa tsoma baki cikin al’amuranta, maimakon ta girmama ’yancinsu kamar yadda suke girmama ta, sai take amfani da karfinta wajen danniya da cin zali. A lokaci guda kuma, take ganin laifinsu da neman haddasa fitina a dangantakarsu da kasar Sin.

Labarai Masu Nasaba

An Gudanar Da Taron Dandalin Tattaunawar Neman Sabon Tunani Na Asali Na 2025

Sin: Ya Kamata A Warware Sabanin Tattalin Arziki Da Cinikayya Ta Hanyar Tattaunawa

Sharadin huldar kasar Sin da kasashen ketare shi ne girmama juna da girmama cikakken ’yancin kasashe da moriyar juna ba tare da sharadi ba da kauracewa tsoma baki ko katsalandan cikin harkokinsu na gida, lamarin da ya sa take samun karbuwa a tsakanin kasashen duniya musamman masu tasowa.

Ya zama wajibi Amurka ta sake nazari ta sauya takunta domin kasancewarta daya tilo mai karfi a duniya, ba abu ne da zai yiwu ba, kana matakai maras dacewa da take dauka, suna kara rage kimarta a idon duniya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaJoe BidenSin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Ya Jaddada Ci Gaba Da Inganta Aikin Gina Kyakkyawar Kasar Sin

Next Post

IMF: GDPn Sin Zai Karu Da Kashi 5.4 A Shekarar 2023

Related

An Gudanar Da Taron Dandalin Tattaunawar Neman Sabon Tunani Na Asali Na 2025
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Taron Dandalin Tattaunawar Neman Sabon Tunani Na Asali Na 2025

19 hours ago
Sin: Ya Kamata A Warware Sabanin Tattalin Arziki Da Cinikayya Ta Hanyar Tattaunawa
Daga Birnin Sin

Sin: Ya Kamata A Warware Sabanin Tattalin Arziki Da Cinikayya Ta Hanyar Tattaunawa

20 hours ago
An Fara Sabon Zagayen Tattaunawar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka A Sweden
Daga Birnin Sin

An Fara Sabon Zagayen Tattaunawar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka A Sweden

21 hours ago
Sin Ta Samu Iska Mai Ni’ima Da Ruwa Mai Inganci A Rabin Farko Na Bana
Daga Birnin Sin

Sin Ta Samu Iska Mai Ni’ima Da Ruwa Mai Inganci A Rabin Farko Na Bana

22 hours ago
Sin Za Ta Ba Da Tallafin Kula Da Yara A Fadin Kasar
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Ba Da Tallafin Kula Da Yara A Fadin Kasar

23 hours ago
Ana Ci Gaba Da Habaka Karfin Kudin Kasar Sin Tun Daga Shekarar 2021
Daga Birnin Sin

Ana Ci Gaba Da Habaka Karfin Kudin Kasar Sin Tun Daga Shekarar 2021

24 hours ago
Next Post
IMF: GDPn Sin Zai Karu Da Kashi 5.4 A Shekarar 2023

IMF: GDPn Sin Zai Karu Da Kashi 5.4 A Shekarar 2023

LABARAI MASU NASABA

Birtaniya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Mutane 33 A Zamfara

Birtaniya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Mutane 33 A Zamfara

July 29, 2025
Mai Cin Moriyar Kai Da Mai Cin Moriyar Juna

Mai Cin Moriyar Kai Da Mai Cin Moriyar Juna

July 29, 2025
Kar Ka Zuga Ƴan Arewa Kan Tinubu — Nabena Ya Gargaɗi Kwankwaso

Kar Ka Zuga Ƴan Arewa Kan Tinubu — Nabena Ya Gargaɗi Kwankwaso

July 29, 2025
Gwamnatin Katsina Ta Fara Bayar Da Maganin Zazzabi Kyauta A Asibitoci

Gwamnatin Katsina Ta Fara Bayar Da Maganin Zazzabi Kyauta A Asibitoci

July 29, 2025
NiMet Ta Yi Hasashen Samun Mamakon Ruwan Sama A Sassan Nijeriya Cikin Kwana 3

NiMet Ta Yi Hasashen Samun Mamakon Ruwan Sama A Sassan Nijeriya Cikin Kwana 3

July 29, 2025
Gwamnonin Nijeriya Sun Yi Ta’aziyyar Waɗanda Suka Rasu A Ambaliyar Ruwa A Adamawa

Gwamnonin Nijeriya Sun Yi Ta’aziyyar Waɗanda Suka Rasu A Ambaliyar Ruwa A Adamawa

July 29, 2025
Gwamnan Zamfara Ya Naɗa Abdulkadir Ibrahim A Matsayin Sabon Sarkin Katsinan Gusau Na 16

Gwamnan Zamfara Ya Naɗa Abdulkadir Ibrahim A Matsayin Sabon Sarkin Katsinan Gusau Na 16

July 29, 2025
Tsohon Ɗan Takarar Mataimakin Gwamnan Kaduna Na PDP Ya Koma ADC

Tsohon Ɗan Takarar Mataimakin Gwamnan Kaduna Na PDP Ya Koma ADC

July 29, 2025
EFCC Ta Kama Mutane 11 Kan Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Akwa Ibom

EFCC Ta Kama Mutane 11 Kan Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Akwa Ibom

July 29, 2025
Gwamna Dikko Zai Sake Tsarin Babbar Kasuwar Jihar Katsina

Jami’an Tsaron Katsina Sama Da 100 Sun Rasu A Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda – Gwamnati

July 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.