ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

AGOA: Tallafi ko Makami?

by CGTN Hausa
3 years ago
AGOA

A farkon wannan mako ne, shugaban Uganda Yoweri Museveni, ya soki matakin Amurka na cire kasarsa daga yarjejeniyar cinikayya ta AGOA, saboda abun da Amurka ta kira “take hakkokin bil adama”.

AGOA, yarjejeniya ce da Amurka ta gabatar a shekarar 2000 domin ba kasashen kudu da hamadar Sahara damar shigar da wasu kayayyaki sama da 1,800 cikin Amurkar ba tare da biyan haraji ba.

  • Kalaman Amurka Zai Iya Shafar Tattalin Arzikin Nijeriya – Minista
  • Bikin CIIE Ya Sa Kayayyakin Kasashen Afirka Samun Karbuwa

Sai dai, matakin Amurka ya sa alamar tambaya kan me taimakonta ke nufi: tallafi domin ci gaban kasashe ko kuma makamin tilasta musu akidunta? Matakin Amurka ya bayyana karara yadda take mayar da hankali wajen neman kakabawa kasashe masu tasowa ra’ayoyi da akidunta, ko da kuwa ba su dace da bukatu ko muradun wadancan kasashe ba. Amurka ta kan yi amfani da karfinta da tallafin da take ba kasashe masu karancin kudin shiga a matsayin wani makami na juya su yadda ta ga dama. Ta manta cewa, su ma ’yantattun kasashe ne dake da ikon cin gashin kansu da zartar da dokokin da suka dace da su.

ADVERTISEMENT

Kasashen duniya sun bambanta da juna, al’adu ko addini ko kabila, ba za su taba zama iri daya ba. Kuma wannan bambancin shi ne ke kara kawata zaman rayuwa da koya mana yadda za mu zauna tare bisa girmamawa da hakuri da juna, kamar yadda shawarar kasar Sin ta wayewar kan duniya wato GCI ta gabatar, wato zaman jituwa da koyi da juna tsakanin mabanbanta al’ummomin duniya. Kowace kasa a duniya na da ikon zabarwa kanta dokokin da suka dace da ita. Uganda ta zabi zartar da dokar hana auren jinsi, abun da ya kamata Amurka ta yi shi ne, girmama zabin Uganda, da kaucewa tsoma baki cikin al’amuranta na ci gida. Cire sunan wasu kasashe da ta yi daga yarjejeniyar AGOA ya nuna cewa, ba ci gabansu take nema ba kamar yadda take ikirari, cin zali da yadda za ta kasance mai babakere a duniya, shi ne burinta.

Amurka ta kan zartar da dokoki ko aiwatar da ayyuka, amma wadannan kasashe ba sa tsoma baki cikin al’amuranta, maimakon ta girmama ’yancinsu kamar yadda suke girmama ta, sai take amfani da karfinta wajen danniya da cin zali. A lokaci guda kuma, take ganin laifinsu da neman haddasa fitina a dangantakarsu da kasar Sin.

LABARAI MASU NASABA

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

Sharadin huldar kasar Sin da kasashen ketare shi ne girmama juna da girmama cikakken ’yancin kasashe da moriyar juna ba tare da sharadi ba da kauracewa tsoma baki ko katsalandan cikin harkokinsu na gida, lamarin da ya sa take samun karbuwa a tsakanin kasashen duniya musamman masu tasowa.

Ya zama wajibi Amurka ta sake nazari ta sauya takunta domin kasancewarta daya tilo mai karfi a duniya, ba abu ne da zai yiwu ba, kana matakai maras dacewa da take dauka, suna kara rage kimarta a idon duniya.

AGOA
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

MASU ALAKA

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin
Daga Birnin Sin

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

July 6, 2026
Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya
Daga Birnin Sin

Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

July 6, 2026
Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela
Daga Birnin Sin

Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

July 6, 2026
Next Post
IMF: GDPn Sin Zai Karu Da Kashi 5.4 A Shekarar 2023

IMF: GDPn Sin Zai Karu Da Kashi 5.4 A Shekarar 2023

LABARAI MASU NASABA

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

July 6, 2026
Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

July 6, 2026
Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

July 6, 2026
Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

July 6, 2026
FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

July 6, 2026
Shugabannin Sin Da Madagascar Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 20 Da Kulla Alakar Diflomasiyya Tsakaninsu

Shugabannin Sin Da Madagascar Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 20 Da Kulla Alakar Diflomasiyya Tsakaninsu

July 6, 2026
Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

July 6, 2026
Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

July 6, 2026
ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

July 6, 2026
Rundunar Sojin Ruwan Sin Ta Yi Gwajin Makami Mai Linzami Ta Amfani Da Jirgin Ruwa Mai Nutso

Rundunar Sojin Ruwan Sin Ta Yi Gwajin Makami Mai Linzami Ta Amfani Da Jirgin Ruwa Mai Nutso

July 6, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.