ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, September 11, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

AGOA: Tallafi ko Makami?

by CGTN Hausa
3 years ago
AGOA

A farkon wannan mako ne, shugaban Uganda Yoweri Museveni, ya soki matakin Amurka na cire kasarsa daga yarjejeniyar cinikayya ta AGOA, saboda abun da Amurka ta kira “take hakkokin bil adama”.

AGOA, yarjejeniya ce da Amurka ta gabatar a shekarar 2000 domin ba kasashen kudu da hamadar Sahara damar shigar da wasu kayayyaki sama da 1,800 cikin Amurkar ba tare da biyan haraji ba.

  • Kalaman Amurka Zai Iya Shafar Tattalin Arzikin Nijeriya – Minista
  • Bikin CIIE Ya Sa Kayayyakin Kasashen Afirka Samun Karbuwa

Sai dai, matakin Amurka ya sa alamar tambaya kan me taimakonta ke nufi: tallafi domin ci gaban kasashe ko kuma makamin tilasta musu akidunta? Matakin Amurka ya bayyana karara yadda take mayar da hankali wajen neman kakabawa kasashe masu tasowa ra’ayoyi da akidunta, ko da kuwa ba su dace da bukatu ko muradun wadancan kasashe ba. Amurka ta kan yi amfani da karfinta da tallafin da take ba kasashe masu karancin kudin shiga a matsayin wani makami na juya su yadda ta ga dama. Ta manta cewa, su ma ’yantattun kasashe ne dake da ikon cin gashin kansu da zartar da dokokin da suka dace da su.

ADVERTISEMENT

Kasashen duniya sun bambanta da juna, al’adu ko addini ko kabila, ba za su taba zama iri daya ba. Kuma wannan bambancin shi ne ke kara kawata zaman rayuwa da koya mana yadda za mu zauna tare bisa girmamawa da hakuri da juna, kamar yadda shawarar kasar Sin ta wayewar kan duniya wato GCI ta gabatar, wato zaman jituwa da koyi da juna tsakanin mabanbanta al’ummomin duniya. Kowace kasa a duniya na da ikon zabarwa kanta dokokin da suka dace da ita. Uganda ta zabi zartar da dokar hana auren jinsi, abun da ya kamata Amurka ta yi shi ne, girmama zabin Uganda, da kaucewa tsoma baki cikin al’amuranta na ci gida. Cire sunan wasu kasashe da ta yi daga yarjejeniyar AGOA ya nuna cewa, ba ci gabansu take nema ba kamar yadda take ikirari, cin zali da yadda za ta kasance mai babakere a duniya, shi ne burinta.

Amurka ta kan zartar da dokoki ko aiwatar da ayyuka, amma wadannan kasashe ba sa tsoma baki cikin al’amuranta, maimakon ta girmama ’yancinsu kamar yadda suke girmama ta, sai take amfani da karfinta wajen danniya da cin zali. A lokaci guda kuma, take ganin laifinsu da neman haddasa fitina a dangantakarsu da kasar Sin.

LABARAI MASU NASABA

Sin Ce Ta Zo Ta Farko A Rahoton Yanayin Tsaron Jama’a Na Duniya

Sin Ta Ciri Tuta Game Da Rawar Gani Da Take Takawa A Fannin Warware Kalubalen Tsaro A Gabas Ta Tsakiya

Sharadin huldar kasar Sin da kasashen ketare shi ne girmama juna da girmama cikakken ’yancin kasashe da moriyar juna ba tare da sharadi ba da kauracewa tsoma baki ko katsalandan cikin harkokinsu na gida, lamarin da ya sa take samun karbuwa a tsakanin kasashen duniya musamman masu tasowa.

Ya zama wajibi Amurka ta sake nazari ta sauya takunta domin kasancewarta daya tilo mai karfi a duniya, ba abu ne da zai yiwu ba, kana matakai maras dacewa da take dauka, suna kara rage kimarta a idon duniya.

AGOA
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ce Ta Zo Ta Farko A Rahoton Yanayin Tsaron Jama’a Na Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

MASU ALAKA

Sin Ce Ta Zo Ta Farko A Rahoton Yanayin Tsaron Jama’a Na Duniya
Daga Birnin Sin

Sin Ce Ta Zo Ta Farko A Rahoton Yanayin Tsaron Jama’a Na Duniya

September 10, 2026
Sin Ta Ciri Tuta Game Da Rawar Gani Da Take Takawa A Fannin Warware Kalubalen Tsaro A Gabas Ta Tsakiya
Daga Birnin Sin

Sin Ta Ciri Tuta Game Da Rawar Gani Da Take Takawa A Fannin Warware Kalubalen Tsaro A Gabas Ta Tsakiya

September 10, 2026
Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30

September 10, 2026
Next Post
IMF: GDPn Sin Zai Karu Da Kashi 5.4 A Shekarar 2023

IMF: GDPn Sin Zai Karu Da Kashi 5.4 A Shekarar 2023

LABARAI MASU NASABA

AGOA

Dalilin Da Ya Sa Ba Zan Janye Wa Atiku Ba A Zaɓen 2027 – Peter Obi

September 11, 2026
Farashin Siminti Zai Ragu Idan Farashin Kayan Aiki Ya Sauka – BUA

Gwarzon Shekarar 2026 Abdulsamad Rabiu

September 11, 2026
Cutar Kwalara Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuƙe

Buƙatar Ɗaukar Matakan Daƙile Yaɗuwar Cutar Mashaƙo A Nijeriya

September 11, 2026
Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje

Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje

September 10, 2026
Sin Ce Ta Zo Ta Farko A Rahoton Yanayin Tsaron Jama’a Na Duniya

Sin Ce Ta Zo Ta Farko A Rahoton Yanayin Tsaron Jama’a Na Duniya

September 10, 2026
Sin Ta Ciri Tuta Game Da Rawar Gani Da Take Takawa A Fannin Warware Kalubalen Tsaro A Gabas Ta Tsakiya

Sin Ta Ciri Tuta Game Da Rawar Gani Da Take Takawa A Fannin Warware Kalubalen Tsaro A Gabas Ta Tsakiya

September 10, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Gwangwaje Tawagar Kwallon Kwando Ta Mata Da Dala 100,000 Kowace

Gwamnatin Tarayya Ta Gwangwaje Tawagar Kwallon Kwando Ta Mata Da Dala 100,000 Kowace

September 10, 2026
Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30

Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30

September 10, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar da Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC da NECO

Gwamnatin Tarayya Za Ta Rika Bai Wa Ɗalibai 100MB Na Data Kyauta Kullum

September 10, 2026
Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana

Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.