• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mun Biya Miliyan 250 Don Ceto Dalibai 121 Da Aka Sace A Kaduna – CAN

by Sadiq
2 years ago
in Labarai
0
Mun Biya Miliyan 250 Don Ceto Dalibai 121 Da Aka Sace A Kaduna – CAN
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kungiyar Kiristocin Nijeriya (CAN) reshen Jihar Kaduna, Rabaran John Joseph Hayab, ya bayyana cewa sun biya kudin fansa Naira miliyan 250 domin a sako dalibai 121 na makarantar sakandare ta Bethel Baptist da aka yi garkuwa da su a watan Yuli 2021.

Rabaran Hayab ya bayyana haka ne a wata ziyarar ban girma da ya kai wa Gwamna Uba Sani a Kaduna.

Ya kuma bayyana cewa Treasure Ayuba, dalibin Bethel na karshe da ya tsere daga hannun wadanda suka yi garkuwa da su kimanin mako daya da ya wuce,ya musanta rade-radin da ake na cewar dalibin ya nuna sha’awar zama a hannun maharan.

Shugaban na CAN ya bayyana cewa an yi kokarin ganin an sako Treasure, ciki har da aika kudin fansa ga maharan har sau biyu, ya kara da cewa jimillar kudaden da aka biya domin a sako su a karshe ya kai Naira miliyan 250.

“A yau, mun taru a nan don nuna godiya. Muna maraba da dawowar Treasure Ayuba, dalibi na karshe da ya rage a hannun ‘yan bindiga na makarantar sakandaren Bethel Baptist da ke nan Kaduna.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

Ya bayyana irin kalubalen da ‘yan uwan Treasure suka fuskanta wajen ganin an sako shi da kuma sace-sacen da aka yi a lokacin da aka kai kudin fansa.

Da yake mayar da martani, Gwamna Uba Sani ya ba iwa Treasure Ayuba tabbacin goyon bayan gwamnatin jihar tare da bayyana cewa ana daukar matakan inganta lafiyar dalibai a makarantun jihar.

Uba Sani ya ce kafa kwamitocin tsaro a makarantu, tura jami’an ‘yan banga na Kaduna (KADVIS), da kuma tabbatar da harabar makarantu ta hanyar gina shinge na daga cikin matakan tabbatar da tsaron dalibai da kuma inganta yanayin karatu.

“Mun dauki matakin kare makarantunmu da kuma tabbatar da cewa yaranmu sun samu ilimi a yanayi mai kyau. Za mu kafa kwamitocin tsaro a dukkan makarantu, mu tabbatar da tura jami’an tsaro na KADVIS (Kaduna Vigilance Service) zuwa dukkan makarantunmu, tare da tabbatar da tsaron makarantunmu ta hanyar gina katanga a kewayen makarantun, da sauran matakan da za mu dauka,” in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: CANDalibaiKadunaKudin FansaRabaranUba SaniYan bindiga
ShareTweetSendShare
Previous Post

NLC Da TUC Sun Rufe Titin Zuwa Filin Jirgin Saman Abuja, Sun Bukaci A Hana Zuwa Imo

Next Post

Kasar Sin Za Ta Inganta Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Gabatar Da Karin Damarmaki Ga Duniya

Related

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

18 minutes ago
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano
Manyan Labarai

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

1 hour ago
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji
Kotu Da Ɗansanda

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

2 hours ago
Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara
Tsaro

Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

3 hours ago
Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru
Labarai

Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

3 hours ago
Minista Ya Buƙaci Kafafen Yaɗa Labarai Da Su Guji Tallata ’Yan Ta’adda Da ’Yan Bindiga
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Sha Alwashin Kama Waɗanda Suka Kashe Masallata A Malumfashi 

3 hours ago
Next Post
Kasar Sin Za Ta Inganta Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Gabatar Da Karin Damarmaki Ga Duniya

Kasar Sin Za Ta Inganta Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Gabatar Da Karin Damarmaki Ga Duniya

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

August 23, 2025
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

August 23, 2025
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

August 23, 2025
Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

August 23, 2025
Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

August 23, 2025
Minista Ya Buƙaci Kafafen Yaɗa Labarai Da Su Guji Tallata ’Yan Ta’adda Da ’Yan Bindiga

Gwamnatin Tarayya Ta Sha Alwashin Kama Waɗanda Suka Kashe Masallata A Malumfashi 

August 23, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

August 23, 2025
Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

August 23, 2025
2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe

2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe

August 23, 2025
Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.