• English
  • Business News
Wednesday, August 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Adawa Sun Dana Wa Ministar Mata Tarko – Gwamnatin Kaduna

by Sulaiman
2 years ago
in Manyan Labarai
0
‘Yan Adawa Sun Dana Wa Ministar Mata Tarko – Gwamnatin Kaduna
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Jihar Kaduna ta zargi ‘yan adawa da dana wa Ministar Harkokin Mata, Barista Uju Kennedy-Ohanenye tarko yayin da suka kitsa mata cewa, akwai rikicin da ya ki ci ya ki cinyewa tsawon shekara 20 a tsakanin Hausa/Fulani da kabilun Koro da Gbagyi a yankin Karamar Hukumar Kagarko da ke kudancin jihar.

Gwamnatin jihar ta fitar da sanarwa domin mayar da martani kan wasu rahotonni da kafafen yada laba-rai suka fitar da ke cewa, ministar ta yi wani taron sulhu da wasu kabilun karamar hukumar ta Kagarko domin wanzar da zaman lafiya tsakaninsu.

  • Gwamna Lawal Ya Nanata Bukatar Hadin Kai Tsakanin Hukumomin Tsaro
  • Gwamna Radda Ya Yi Allah Wadai Da Hare-haren ‘Yan Fashin Daji A Jihar Katsina 

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Babban Sakataren Yada Labarai na Gwamnan Jihar Kaduna, Muhammad Lawal Shehu ya fitar, inda ta bukaci al’ummar Jihar Kaduna da sauran ‘Yan Nijeriya su yi watsi da kalaman da suka ce babban kuskure ne mai hadari da wasu kafafen yada labarai suka yada.

Gwamnatin ta yi takaicin yada irin wadannan labaran ba tare da tantance gaskiyar lamarin ba wanda a cewarta, ka iya haifar da rudani da tada zaune tsaye a Karamar Hukumar Kagarko.

“Domin kauce wa shakku, ya kamata jama’a su lura cewa, babu wani rikici a Karamar Hukumar Kagarko. Hasali ma, karamar hukumar ta samu zaman lafiya da kwanciyar hankali na tsawon shekaru kuma har yanzu tana daya daga cikin kananan hukumomin jihar da ke zaune cikin kwanciyar hankali.

Labarai Masu Nasaba

Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano

Remi Tinubu Ta Bada Gudunmawar Naira Biliyan 1 Ga Wadanda Ambaliyar Ruwan Neja Ta Shafa

“Gamnatin jihar Kaduna ta samu sahihan rahotanni da ke nuni da cewa, ‘yan babbar jam’iyyar adawa ne suka kitsa makircin da nufin zamba ga gwamnatin tarayya, inda suka dana wa ministar harkokin mata tarko kuma ta fada ta hanyar bijiro mata da labarai marasa tushe na rashin jituwa da rikici a tsakanin kabilun da ke Karamar Hukumar Kagarko.

“Ministar, ba tare da tantance ikirarin nasu na bogi ba, kuma ba tare da tuntubar jami’an Karamar Hukumar Kagarko da na Gwamnatin Jihar Kaduna ba, duk da kasancewarta Lauya, amma ta ta fitar da sanarwar alkawurran filayen noma ga mutanen yankin da ke rikici da juna.

In ba a manta ba, a ranar 2 ga watan Nuwamba ne, Ministar harkokin Mata ta kasa, Barista Uju Kenne-dy Ohanenye ta bayyana a shafin sada zumunta na D da akafi sani da twitter (@BarrUjuKennedy), inda ta ce, “Wannan babbar nasara ce da ma’aikatarta ta samu na samar da zaman lafiya a tsakanin al’umomin Koro da Hausawa da Fulani da ke rikici a Karamar Hukumar Kagarko a Jihar Kaduna, domin kawo karshen rikicin da aka kwashe shekaru 20 ana yi. Ma’aikatar za ta samar da fili Eka 100 don yin noma na zamani a yankin, wanda hakan zai taikamaka wa mutanen yankin su kaunaci juna maimakon ci gaba da yakar juna.”

A rahotannin da wasu gidajen talabijin na kasa suka yada, an ga ministar tare da wasu tsirarun mutanen da suka zama wakilan kabilun a wurin taron, suna bayani a kan cewa “bisa wannan tallafi da alheri da kika zo mana da shi, komai ya wuce, za mu zauna lafiya.”

Har zuwa lokacin hada wannan labari dai, minister ba ta ce uffan kan lamarin ba ko wata sanarwa daga ma’aikatarta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KadunaKudancin KadunaMinistar harkokin mata
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yawaitar Mutuwar Farad-daya A Nijeriya

Next Post

Satar Danyen Mai: Nijeriya Ta Yi Asarar Tiriliya 4.3 Cikin Shekaru 5

Related

Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano
Da ɗumi-ɗuminsa

Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano

12 minutes ago
Remi Tinubu Ta Bada Gudunmawar Naira Biliyan 1 Ga Wadanda Ambaliyar Ruwan Neja Ta Shafa
Manyan Labarai

Remi Tinubu Ta Bada Gudunmawar Naira Biliyan 1 Ga Wadanda Ambaliyar Ruwan Neja Ta Shafa

7 hours ago
Shugaban ‘Yan Bindiga A Zamfara, Bello Turji, Ya Ajiye Makamai, Ya Saki Mutane 32
Manyan Labarai

Shugaban ‘Yan Bindiga A Zamfara, Bello Turji, Ya Ajiye Makamai, Ya Saki Mutane 32

8 hours ago
Ƴansanda Sun Kama Ƴan Uwa da Wasu Biyu Kan Ƙirkirar Garkuwa Da Kansu A Abuja
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Kama Ƴan Uwa da Wasu Biyu Kan Ƙirkirar Garkuwa Da Kansu A Abuja

15 hours ago
Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano
Manyan Labarai

Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

1 day ago
Kashe N712bn Kan Gyaran Filin Jiragen Saman Legas Rashin Sanin Ya Kamata Ne – ADC 
Manyan Labarai

Kashe N712bn Kan Gyaran Filin Jiragen Saman Legas Rashin Sanin Ya Kamata Ne – ADC 

2 days ago
Next Post
Satar Danyen Mai

Satar Danyen Mai: Nijeriya Ta Yi Asarar Tiriliya 4.3 Cikin Shekaru 5

LABARAI MASU NASABA

Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano

Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano

August 6, 2025
Hare-haren Boko Haram Da ‘Yan Bindiga Ya Ragu A Cikin Shekaru Biyu – Ribadu

Hare-haren Boko Haram Da ‘Yan Bindiga Ya Ragu A Cikin Shekaru Biyu – Ribadu

August 5, 2025
Kasar Sin Ta Sanar Da Matakan Fara Bayar Da Ilimin Kafin Firamare Kyauta

Kasar Sin Ta Sanar Da Matakan Fara Bayar Da Ilimin Kafin Firamare Kyauta

August 5, 2025
Shugaban IWGA: Birnin Chengdu Zai Karbi Bakuncin Gasar Wasanni Mafi Kyau A Tarihi

Shugaban IWGA: Birnin Chengdu Zai Karbi Bakuncin Gasar Wasanni Mafi Kyau A Tarihi

August 5, 2025
Jigawa Ta Fitar Da ₦1.5bn Na Lamunin Noma Ga Ma’aikatan Gwamnati Kashi Na Biyu

Jigawa Ta Fitar Da ₦1.5bn Na Lamunin Noma Ga Ma’aikatan Gwamnati Kashi Na Biyu

August 5, 2025
Matakin Baiwa Kansa Hakuri Ba Zai Kawar Da Matsayin Gwamnatin Lai Ching-te Na Kasancewa ’Yar Dara A Hannun Amurka Ba

Matakin Baiwa Kansa Hakuri Ba Zai Kawar Da Matsayin Gwamnatin Lai Ching-te Na Kasancewa ’Yar Dara A Hannun Amurka Ba

August 5, 2025
Sin Ta Fitar Da Shirin Kyautata Muhalli Domin Inganta Kiwon Lafiya Na Shekaru Biyar

Sin Ta Fitar Da Shirin Kyautata Muhalli Domin Inganta Kiwon Lafiya Na Shekaru Biyar

August 5, 2025
Ruftawar Gini Ya Kashe Uwa Da ‘Ya’yanta Biyar A Katsina

Ruftawar Gini Ya Kashe Uwa Da ‘Ya’yanta Biyar A Katsina

August 5, 2025
Sashen Cinikayyar Samar Da Hidimomi Na Sin Ya Bunkasa Da Kaso Takwas A Rabin Farko Na Shekarar 2025

Sashen Cinikayyar Samar Da Hidimomi Na Sin Ya Bunkasa Da Kaso Takwas A Rabin Farko Na Shekarar 2025

August 5, 2025
Gwamnatin Sin: Gwamnatin Jama’a Domin Jama’a

Gwamnatin Sin: Gwamnatin Jama’a Domin Jama’a

August 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.