• English
  • Business News
Friday, July 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Adawa Sun Dana Wa Ministar Mata Tarko – Gwamnatin Kaduna

by Sulaiman
2 years ago
in Manyan Labarai
0
‘Yan Adawa Sun Dana Wa Ministar Mata Tarko – Gwamnatin Kaduna
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Jihar Kaduna ta zargi ‘yan adawa da dana wa Ministar Harkokin Mata, Barista Uju Kennedy-Ohanenye tarko yayin da suka kitsa mata cewa, akwai rikicin da ya ki ci ya ki cinyewa tsawon shekara 20 a tsakanin Hausa/Fulani da kabilun Koro da Gbagyi a yankin Karamar Hukumar Kagarko da ke kudancin jihar.

Gwamnatin jihar ta fitar da sanarwa domin mayar da martani kan wasu rahotonni da kafafen yada laba-rai suka fitar da ke cewa, ministar ta yi wani taron sulhu da wasu kabilun karamar hukumar ta Kagarko domin wanzar da zaman lafiya tsakaninsu.

  • Gwamna Lawal Ya Nanata Bukatar Hadin Kai Tsakanin Hukumomin Tsaro
  • Gwamna Radda Ya Yi Allah Wadai Da Hare-haren ‘Yan Fashin Daji A Jihar Katsina 

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Babban Sakataren Yada Labarai na Gwamnan Jihar Kaduna, Muhammad Lawal Shehu ya fitar, inda ta bukaci al’ummar Jihar Kaduna da sauran ‘Yan Nijeriya su yi watsi da kalaman da suka ce babban kuskure ne mai hadari da wasu kafafen yada labarai suka yada.

Gwamnatin ta yi takaicin yada irin wadannan labaran ba tare da tantance gaskiyar lamarin ba wanda a cewarta, ka iya haifar da rudani da tada zaune tsaye a Karamar Hukumar Kagarko.

“Domin kauce wa shakku, ya kamata jama’a su lura cewa, babu wani rikici a Karamar Hukumar Kagarko. Hasali ma, karamar hukumar ta samu zaman lafiya da kwanciyar hankali na tsawon shekaru kuma har yanzu tana daya daga cikin kananan hukumomin jihar da ke zaune cikin kwanciyar hankali.

Labarai Masu Nasaba

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Okpebholo A Matsayin Zaɓaɓɓen Gwamnan Edo

“Gamnatin jihar Kaduna ta samu sahihan rahotanni da ke nuni da cewa, ‘yan babbar jam’iyyar adawa ne suka kitsa makircin da nufin zamba ga gwamnatin tarayya, inda suka dana wa ministar harkokin mata tarko kuma ta fada ta hanyar bijiro mata da labarai marasa tushe na rashin jituwa da rikici a tsakanin kabilun da ke Karamar Hukumar Kagarko.

“Ministar, ba tare da tantance ikirarin nasu na bogi ba, kuma ba tare da tuntubar jami’an Karamar Hukumar Kagarko da na Gwamnatin Jihar Kaduna ba, duk da kasancewarta Lauya, amma ta ta fitar da sanarwar alkawurran filayen noma ga mutanen yankin da ke rikici da juna.

In ba a manta ba, a ranar 2 ga watan Nuwamba ne, Ministar harkokin Mata ta kasa, Barista Uju Kenne-dy Ohanenye ta bayyana a shafin sada zumunta na D da akafi sani da twitter (@BarrUjuKennedy), inda ta ce, “Wannan babbar nasara ce da ma’aikatarta ta samu na samar da zaman lafiya a tsakanin al’umomin Koro da Hausawa da Fulani da ke rikici a Karamar Hukumar Kagarko a Jihar Kaduna, domin kawo karshen rikicin da aka kwashe shekaru 20 ana yi. Ma’aikatar za ta samar da fili Eka 100 don yin noma na zamani a yankin, wanda hakan zai taikamaka wa mutanen yankin su kaunaci juna maimakon ci gaba da yakar juna.”

A rahotannin da wasu gidajen talabijin na kasa suka yada, an ga ministar tare da wasu tsirarun mutanen da suka zama wakilan kabilun a wurin taron, suna bayani a kan cewa “bisa wannan tallafi da alheri da kika zo mana da shi, komai ya wuce, za mu zauna lafiya.”

Har zuwa lokacin hada wannan labari dai, minister ba ta ce uffan kan lamarin ba ko wata sanarwa daga ma’aikatarta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KadunaKudancin KadunaMinistar harkokin mata
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yawaitar Mutuwar Farad-daya A Nijeriya

Next Post

Satar Danyen Mai: Nijeriya Ta Yi Asarar Tiriliya 4.3 Cikin Shekaru 5

Related

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

4 hours ago
Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Okpebholo A Matsayin Zaɓaɓɓen Gwamnan Edo
Da ɗumi-ɗuminsa

Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Okpebholo A Matsayin Zaɓaɓɓen Gwamnan Edo

13 hours ago
Buhari Ba Mutum Ne Mai Son Abun Duniya Ba – Gowon
Manyan Labarai

Buhari Ba Mutum Ne Mai Son Abun Duniya Ba – Gowon

15 hours ago
Tinubu Bai Taɓa Ba Ni Umarnin Yin Ƙarya Ko Cin Zarafin ’Yan Jarida Ba – Minista
Manyan Labarai

Tinubu Bai Taɓa Ba Ni Umarnin Yin Ƙarya Ko Cin Zarafin ’Yan Jarida Ba – Minista

18 hours ago
Har Yanzu A Cikin PDP Nake, Ba Zan Koma APC Ko ADC Ba – Gwamnan Zamfara
Manyan Labarai

Har Yanzu A Cikin PDP Nake, Ba Zan Koma APC Ko ADC Ba – Gwamnan Zamfara

1 day ago
Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba
Manyan Labarai

Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

2 days ago
Next Post
Satar Danyen Mai

Satar Danyen Mai: Nijeriya Ta Yi Asarar Tiriliya 4.3 Cikin Shekaru 5

LABARAI MASU NASABA

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

July 10, 2025
Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

July 10, 2025
Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

July 10, 2025
Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

July 10, 2025
Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

July 10, 2025
An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

July 10, 2025
Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

July 10, 2025
Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

July 10, 2025
An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

July 10, 2025
Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

July 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.