ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Adawa Sun Dana Wa Ministar Mata Tarko – Gwamnatin Kaduna

by Sulaiman
3 years ago
Ministar mata

Gwamnatin Jihar Kaduna ta zargi ‘yan adawa da dana wa Ministar Harkokin Mata, Barista Uju Kennedy-Ohanenye tarko yayin da suka kitsa mata cewa, akwai rikicin da ya ki ci ya ki cinyewa tsawon shekara 20 a tsakanin Hausa/Fulani da kabilun Koro da Gbagyi a yankin Karamar Hukumar Kagarko da ke kudancin jihar.

Gwamnatin jihar ta fitar da sanarwa domin mayar da martani kan wasu rahotonni da kafafen yada laba-rai suka fitar da ke cewa, ministar ta yi wani taron sulhu da wasu kabilun karamar hukumar ta Kagarko domin wanzar da zaman lafiya tsakaninsu.

  • Gwamna Lawal Ya Nanata Bukatar Hadin Kai Tsakanin Hukumomin Tsaro
  • Gwamna Radda Ya Yi Allah Wadai Da Hare-haren ‘Yan Fashin Daji A Jihar Katsina 

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Babban Sakataren Yada Labarai na Gwamnan Jihar Kaduna, Muhammad Lawal Shehu ya fitar, inda ta bukaci al’ummar Jihar Kaduna da sauran ‘Yan Nijeriya su yi watsi da kalaman da suka ce babban kuskure ne mai hadari da wasu kafafen yada labarai suka yada.

ADVERTISEMENT

Gwamnatin ta yi takaicin yada irin wadannan labaran ba tare da tantance gaskiyar lamarin ba wanda a cewarta, ka iya haifar da rudani da tada zaune tsaye a Karamar Hukumar Kagarko.

“Domin kauce wa shakku, ya kamata jama’a su lura cewa, babu wani rikici a Karamar Hukumar Kagarko. Hasali ma, karamar hukumar ta samu zaman lafiya da kwanciyar hankali na tsawon shekaru kuma har yanzu tana daya daga cikin kananan hukumomin jihar da ke zaune cikin kwanciyar hankali.

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

“Gamnatin jihar Kaduna ta samu sahihan rahotanni da ke nuni da cewa, ‘yan babbar jam’iyyar adawa ne suka kitsa makircin da nufin zamba ga gwamnatin tarayya, inda suka dana wa ministar harkokin mata tarko kuma ta fada ta hanyar bijiro mata da labarai marasa tushe na rashin jituwa da rikici a tsakanin kabilun da ke Karamar Hukumar Kagarko.

“Ministar, ba tare da tantance ikirarin nasu na bogi ba, kuma ba tare da tuntubar jami’an Karamar Hukumar Kagarko da na Gwamnatin Jihar Kaduna ba, duk da kasancewarta Lauya, amma ta ta fitar da sanarwar alkawurran filayen noma ga mutanen yankin da ke rikici da juna.

In ba a manta ba, a ranar 2 ga watan Nuwamba ne, Ministar harkokin Mata ta kasa, Barista Uju Kenne-dy Ohanenye ta bayyana a shafin sada zumunta na D da akafi sani da twitter (@BarrUjuKennedy), inda ta ce, “Wannan babbar nasara ce da ma’aikatarta ta samu na samar da zaman lafiya a tsakanin al’umomin Koro da Hausawa da Fulani da ke rikici a Karamar Hukumar Kagarko a Jihar Kaduna, domin kawo karshen rikicin da aka kwashe shekaru 20 ana yi. Ma’aikatar za ta samar da fili Eka 100 don yin noma na zamani a yankin, wanda hakan zai taikamaka wa mutanen yankin su kaunaci juna maimakon ci gaba da yakar juna.”

A rahotannin da wasu gidajen talabijin na kasa suka yada, an ga ministar tare da wasu tsirarun mutanen da suka zama wakilan kabilun a wurin taron, suna bayani a kan cewa “bisa wannan tallafi da alheri da kika zo mana da shi, komai ya wuce, za mu zauna lafiya.”

Har zuwa lokacin hada wannan labari dai, minister ba ta ce uffan kan lamarin ba ko wata sanarwa daga ma’aikatarta.

Ministar mata
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
  • Sulaiman
    Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito
  • Sulaiman
    An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Next Post
Satar Danyen Mai

Satar Danyen Mai: Nijeriya Ta Yi Asarar Tiriliya 4.3 Cikin Shekaru 5

LABARAI MASU NASABA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.