ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Adawa Sun Dana Wa Ministar Mata Tarko – Gwamnatin Kaduna

by Sulaiman
3 years ago
Ministar mata

Gwamnatin Jihar Kaduna ta zargi ‘yan adawa da dana wa Ministar Harkokin Mata, Barista Uju Kennedy-Ohanenye tarko yayin da suka kitsa mata cewa, akwai rikicin da ya ki ci ya ki cinyewa tsawon shekara 20 a tsakanin Hausa/Fulani da kabilun Koro da Gbagyi a yankin Karamar Hukumar Kagarko da ke kudancin jihar.

Gwamnatin jihar ta fitar da sanarwa domin mayar da martani kan wasu rahotonni da kafafen yada laba-rai suka fitar da ke cewa, ministar ta yi wani taron sulhu da wasu kabilun karamar hukumar ta Kagarko domin wanzar da zaman lafiya tsakaninsu.

  • Gwamna Lawal Ya Nanata Bukatar Hadin Kai Tsakanin Hukumomin Tsaro
  • Gwamna Radda Ya Yi Allah Wadai Da Hare-haren ‘Yan Fashin Daji A Jihar Katsina 

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Babban Sakataren Yada Labarai na Gwamnan Jihar Kaduna, Muhammad Lawal Shehu ya fitar, inda ta bukaci al’ummar Jihar Kaduna da sauran ‘Yan Nijeriya su yi watsi da kalaman da suka ce babban kuskure ne mai hadari da wasu kafafen yada labarai suka yada.

ADVERTISEMENT

Gwamnatin ta yi takaicin yada irin wadannan labaran ba tare da tantance gaskiyar lamarin ba wanda a cewarta, ka iya haifar da rudani da tada zaune tsaye a Karamar Hukumar Kagarko.

“Domin kauce wa shakku, ya kamata jama’a su lura cewa, babu wani rikici a Karamar Hukumar Kagarko. Hasali ma, karamar hukumar ta samu zaman lafiya da kwanciyar hankali na tsawon shekaru kuma har yanzu tana daya daga cikin kananan hukumomin jihar da ke zaune cikin kwanciyar hankali.

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

“Gamnatin jihar Kaduna ta samu sahihan rahotanni da ke nuni da cewa, ‘yan babbar jam’iyyar adawa ne suka kitsa makircin da nufin zamba ga gwamnatin tarayya, inda suka dana wa ministar harkokin mata tarko kuma ta fada ta hanyar bijiro mata da labarai marasa tushe na rashin jituwa da rikici a tsakanin kabilun da ke Karamar Hukumar Kagarko.

“Ministar, ba tare da tantance ikirarin nasu na bogi ba, kuma ba tare da tuntubar jami’an Karamar Hukumar Kagarko da na Gwamnatin Jihar Kaduna ba, duk da kasancewarta Lauya, amma ta ta fitar da sanarwar alkawurran filayen noma ga mutanen yankin da ke rikici da juna.

In ba a manta ba, a ranar 2 ga watan Nuwamba ne, Ministar harkokin Mata ta kasa, Barista Uju Kenne-dy Ohanenye ta bayyana a shafin sada zumunta na D da akafi sani da twitter (@BarrUjuKennedy), inda ta ce, “Wannan babbar nasara ce da ma’aikatarta ta samu na samar da zaman lafiya a tsakanin al’umomin Koro da Hausawa da Fulani da ke rikici a Karamar Hukumar Kagarko a Jihar Kaduna, domin kawo karshen rikicin da aka kwashe shekaru 20 ana yi. Ma’aikatar za ta samar da fili Eka 100 don yin noma na zamani a yankin, wanda hakan zai taikamaka wa mutanen yankin su kaunaci juna maimakon ci gaba da yakar juna.”

A rahotannin da wasu gidajen talabijin na kasa suka yada, an ga ministar tare da wasu tsirarun mutanen da suka zama wakilan kabilun a wurin taron, suna bayani a kan cewa “bisa wannan tallafi da alheri da kika zo mana da shi, komai ya wuce, za mu zauna lafiya.”

Har zuwa lokacin hada wannan labari dai, minister ba ta ce uffan kan lamarin ba ko wata sanarwa daga ma’aikatarta.

Ministar mata
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • Sulaiman
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • Sulaiman
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • Sulaiman
    Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

MASU ALAKA

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC
Manyan Labarai

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026
Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 3, Sun Ƙwato Makamai A Sakkwato
Manyan Labarai

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

July 14, 2026
Next Post
Satar Danyen Mai

Satar Danyen Mai: Nijeriya Ta Yi Asarar Tiriliya 4.3 Cikin Shekaru 5

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.