• English
  • Business News
Monday, August 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ziyarar Ministocin Wajen Kasashen Larabawa Da Musulmi A Kasar Sin Ke Nufi?

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Me Ziyarar Ministocin Wajen Kasashen Larabawa Da Musulmi A Kasar Sin Ke Nufi?

Foreign Ministers from five Arab and Islamic countries From left, Egyptian Foreign Minister Sameh Shoukry, Jordanian Deputy Prime Minister and Foreign Minister Ayman Safadi, Palestine Foreign Minister Riyad al-Maliki, Saudi Arabia's Foreign Minister Faisal bin Farhan Al Saud and Indonesian Foreign Minister Retno Marsudi arrive to the Diaoyutai state guesthouse to meet with their Chinese Counterpart Wang Yi, in Beijing, Monday, Nov. 20, 2023. China's foreign minister welcomed five Arab and Islamic counterparts to Beijing on Monday, saying his country would work with "our brothers and sisters" in the Arab and Islamic world to try to end the fighting in Gaza as soon as possible. (AP Photo/Andy Wong)

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A farkon wannan mako ne ministocin harkokin wajen kasashen Larabawa da na musulmi suka kawo ziyara kasar Sin domin tattaunawa da takwaransu na kasar Wang Yi, game da rikicin Palasdinu da Isra’ila. 

To me ya sa a duk cikin kasashen duniya da ma kasashen dake kiran kansu manya, wadannan kasashen Larabawa da Musulmi suka zabi kasar Sin da ta zama kasa ta farko cikin kasashen da za su kai ziyara?

  • Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Bukatar Raya Masanaantun Samar Da Fasahar Intanet Mai Karfin 5G
  • Xi Da Putin Sun Aike Da Sakon Taya Murna Ga Taron Tattaunawa Tsakanin Manyan Jami’yyun Siyasar Sin Da Rasha

Da farko dai, ya nuna yadda kasashen duniya ke ganin kima da darajar kasar Sin. Kuma kowa ya san cewa, ba haka kawai ake samun wadannan abubuwa ba, suna samuwa ne idan mutum ko wata kasa ta nuna cewa ita din ta san ya kamata, kuma ba ta nuna son kai ko fifiko ko danniya. Wadannan, dabi’u ne da Sin ke adawa da su, a don haka take mayar da hankali tare da yin kira da a yi hulda bisa mutuntawa da girmama juna tare da kauracewa yin katsalandan cikin harkokin gidan kasashe.

Abu na biyu shi ne, wadannan kasashe sun kwana da sanin cewa, kasar Sin ba ta gindaya sharudda kafin ta bayar da taimako ko ta yi wani abu da zai amfanawa duniya. Burin kasar Sin har kullum shi ne, a gudu tare a tsira tare domin samun duniya mai zaman lafiya da ci gaba da kuma al’umma mai makoma ta bai daya.

Tun da dadewa kasar Sin ta yi ta bayyana cewa, hanya daya tilo ta warware rikicin Palasdinu da Isra’ila, shi ne aiwatar da kudurin majalisar dinkin duniya na kafa ’yantattun kasashe biyu. Tun farkon fara rikicin, a lokacin da kasashen dake kiran kansu manya suka fito daya bayan daya suna nuna bangaranci da rura wutar rikicin, kasar Sin ta yi abun da ya kamata babbar kasa ta yi, wato kira da a kai zuciya nesa ba tare da ta goyon bayan wani bangare ba. Shaidu sun riga sun tabbatar mana da cewa, ba kowacce matsala ba ce karfin soja ko yaki za ta iya warwarewa. Kamar yadda Sin din take kira a kullum, kwance damarar makamai da komawa teburin sulhu, su ne hanyoyi mafi dorewa na warware rikice-rikice cikin lumana. Don haka, ko shakka babu, wadannan kasashe na Larabawa, na da yakinin cewa, babu wata kasa da ta dace su yi shawarwari da ita don shawo kan matsalar kamar kasar Sin.

Labarai Masu Nasaba

An Fara Bayar Da Hidimomin Da Suka Shafi Sauka Da Tashi Domin Gasar Wasanni Ta Duniya Ta Chengdu

Ana Gaggauta Ayyukan Gyara Tituna Da Gadojin Da Ambaliya Ta Lalata A Arewacin Kasar Sin

Shawarwari da manufofin da kasar Sin take gabatarwa a duniya sun nuna cewa, ita din ba ta kaunar rikici ko tashe-tashen hankula. Kuma wani kudurin MDD da aka kada a kwanakin baya da zummar tsaigata rikicin Palasdinu da Isra’ila, ya tabbatar mana da cewa, wannan ra’ayi na kasar Sin ya yi daidai da ra’ayin galibin kasahen duniya. (Fa’iza Mustapha)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: SinXi JinpingXinhua
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Na Gayyatar ‘Yan Kasuwa Daga Fadin Duniya Don Su Zuba Jari Da Ma Cin Gajiyar Nasarorin Da Ta Samu

Next Post

Messi Da Ronado Za Su Hadu A Wani Wasan Sada Zumunci A Watan Fabrairu

Related

An Fara Bayar Da Hidimomin Da Suka Shafi Sauka Da Tashi Domin Gasar Wasanni Ta Duniya Ta Chengdu
Daga Birnin Sin

An Fara Bayar Da Hidimomin Da Suka Shafi Sauka Da Tashi Domin Gasar Wasanni Ta Duniya Ta Chengdu

17 hours ago
Ana Gaggauta Ayyukan Gyara Tituna Da Gadojin Da Ambaliya Ta Lalata A Arewacin Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Ana Gaggauta Ayyukan Gyara Tituna Da Gadojin Da Ambaliya Ta Lalata A Arewacin Kasar Sin

18 hours ago
Shugabar Tanzania Ta Kaddamar Da Cibiyar Cinikayya Da Jigila Da Sin Ta Gina A Kasar
Daga Birnin Sin

Shugabar Tanzania Ta Kaddamar Da Cibiyar Cinikayya Da Jigila Da Sin Ta Gina A Kasar

19 hours ago
Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya
Daga Birnin Sin

Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya

2 days ago
Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya
Daga Birnin Sin

Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

2 days ago
Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya
Daga Birnin Sin

Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya

2 days ago
Next Post
Messi Da Ronado Za Su Hadu A Wani Wasan Sada Zumunci A Watan Fabrairu

Messi Da Ronado Za Su Hadu A Wani Wasan Sada Zumunci A Watan Fabrairu

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Dan Majalisar Taraba Usman Ya Fice Daga APC

Tsohon Dan Majalisar Taraba Usman Ya Fice Daga APC

August 4, 2025
Yadda Al’ummar Da Ke Zaune Da ‘Yan Bindiga Ke Rayuwa A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane Da Dama A Kauyukan Zamfara

August 4, 2025
Gwamnatin Kano Za Ta Mayar Da Gidan Gyaran Hali Na Kurmawa Gidan Tarihi

Gwamnatin Kano Za Ta Mayar Da Gidan Gyaran Hali Na Kurmawa Gidan Tarihi

August 4, 2025
Kashe N712bn Kan Gyaran Filin Jiragen Saman Legas Rashin Sanin Ya Kamata Ne – ADC 

Kashe N712bn Kan Gyaran Filin Jiragen Saman Legas Rashin Sanin Ya Kamata Ne – ADC 

August 4, 2025
Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina

Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina

August 3, 2025
Sanata Shehu Buba Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Da Rigakafin Shanu A Bauchi

Sanata Shehu Buba Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Da Rigakafin Shanu A Bauchi

August 3, 2025
Wasu Kungiyoyi Sun Yi Kira Ga Dan Majalisa Aminu Sani Jaji Ya Fito Takarar Gwamnan Zamfara 

Wasu Kungiyoyi Sun Yi Kira Ga Dan Majalisa Aminu Sani Jaji Ya Fito Takarar Gwamnan Zamfara 

August 4, 2025
Waɗanne Ƙasashe Ne Suka Amince Da Kafa Ƙasar Falasɗinu?

Waɗanne Ƙasashe Ne Suka Amince Da Kafa Ƙasar Falasɗinu?

August 3, 2025
Dangote Ya Ɗauki Nauyin Bikin Baje Kolin Gidajen Afrika Da Mahalarta Ƙasashe 21

Dangote Ya Ɗauki Nauyin Bikin Baje Kolin Gidajen Afrika Da Mahalarta Ƙasashe 21

August 3, 2025
An Fara Bayar Da Hidimomin Da Suka Shafi Sauka Da Tashi Domin Gasar Wasanni Ta Duniya Ta Chengdu

An Fara Bayar Da Hidimomin Da Suka Shafi Sauka Da Tashi Domin Gasar Wasanni Ta Duniya Ta Chengdu

August 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.