ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ziyarar Ministocin Wajen Kasashen Larabawa Da Musulmi A Kasar Sin Ke Nufi?

by CGTN Hausa
3 years ago
Foreign Ministers from five Arab and Islamic countries From left, Egyptian Foreign Minister Sameh Shoukry, Jordanian Deputy Prime Minister and Foreign Minister Ayman Safadi, Palestine Foreign Minister Riyad al-Maliki, Saudi Arabia's Foreign Minister Faisal bin Farhan Al Saud and Indonesian Foreign Minister Retno Marsudi arrive to the Diaoyutai state guesthouse to meet with their Chinese Counterpart Wang Yi, in Beijing, Monday, Nov. 20, 2023. China's foreign minister welcomed five Arab and Islamic counterparts to Beijing on Monday, saying his country would work with "our brothers and sisters" in the Arab and Islamic world to try to end the fighting in Gaza as soon as possible. (AP Photo/Andy Wong)

Foreign Ministers from five Arab and Islamic countries From left, Egyptian Foreign Minister Sameh Shoukry, Jordanian Deputy Prime Minister and Foreign Minister Ayman Safadi, Palestine Foreign Minister Riyad al-Maliki, Saudi Arabia's Foreign Minister Faisal bin Farhan Al Saud and Indonesian Foreign Minister Retno Marsudi arrive to the Diaoyutai state guesthouse to meet with their Chinese Counterpart Wang Yi, in Beijing, Monday, Nov. 20, 2023. China's foreign minister welcomed five Arab and Islamic counterparts to Beijing on Monday, saying his country would work with "our brothers and sisters" in the Arab and Islamic world to try to end the fighting in Gaza as soon as possible. (AP Photo/Andy Wong)

A farkon wannan mako ne ministocin harkokin wajen kasashen Larabawa da na musulmi suka kawo ziyara kasar Sin domin tattaunawa da takwaransu na kasar Wang Yi, game da rikicin Palasdinu da Isra’ila. 

To me ya sa a duk cikin kasashen duniya da ma kasashen dake kiran kansu manya, wadannan kasashen Larabawa da Musulmi suka zabi kasar Sin da ta zama kasa ta farko cikin kasashen da za su kai ziyara?

  • Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Bukatar Raya Masanaantun Samar Da Fasahar Intanet Mai Karfin 5G
  • Xi Da Putin Sun Aike Da Sakon Taya Murna Ga Taron Tattaunawa Tsakanin Manyan Jami’yyun Siyasar Sin Da Rasha

Da farko dai, ya nuna yadda kasashen duniya ke ganin kima da darajar kasar Sin. Kuma kowa ya san cewa, ba haka kawai ake samun wadannan abubuwa ba, suna samuwa ne idan mutum ko wata kasa ta nuna cewa ita din ta san ya kamata, kuma ba ta nuna son kai ko fifiko ko danniya. Wadannan, dabi’u ne da Sin ke adawa da su, a don haka take mayar da hankali tare da yin kira da a yi hulda bisa mutuntawa da girmama juna tare da kauracewa yin katsalandan cikin harkokin gidan kasashe.

ADVERTISEMENT

Abu na biyu shi ne, wadannan kasashe sun kwana da sanin cewa, kasar Sin ba ta gindaya sharudda kafin ta bayar da taimako ko ta yi wani abu da zai amfanawa duniya. Burin kasar Sin har kullum shi ne, a gudu tare a tsira tare domin samun duniya mai zaman lafiya da ci gaba da kuma al’umma mai makoma ta bai daya.

Tun da dadewa kasar Sin ta yi ta bayyana cewa, hanya daya tilo ta warware rikicin Palasdinu da Isra’ila, shi ne aiwatar da kudurin majalisar dinkin duniya na kafa ’yantattun kasashe biyu. Tun farkon fara rikicin, a lokacin da kasashen dake kiran kansu manya suka fito daya bayan daya suna nuna bangaranci da rura wutar rikicin, kasar Sin ta yi abun da ya kamata babbar kasa ta yi, wato kira da a kai zuciya nesa ba tare da ta goyon bayan wani bangare ba. Shaidu sun riga sun tabbatar mana da cewa, ba kowacce matsala ba ce karfin soja ko yaki za ta iya warwarewa. Kamar yadda Sin din take kira a kullum, kwance damarar makamai da komawa teburin sulhu, su ne hanyoyi mafi dorewa na warware rikice-rikice cikin lumana. Don haka, ko shakka babu, wadannan kasashe na Larabawa, na da yakinin cewa, babu wata kasa da ta dace su yi shawarwari da ita don shawo kan matsalar kamar kasar Sin.

LABARAI MASU NASABA

Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

Shawarwari da manufofin da kasar Sin take gabatarwa a duniya sun nuna cewa, ita din ba ta kaunar rikici ko tashe-tashen hankula. Kuma wani kudurin MDD da aka kada a kwanakin baya da zummar tsaigata rikicin Palasdinu da Isra’ila, ya tabbatar mana da cewa, wannan ra’ayi na kasar Sin ya yi daidai da ra’ayin galibin kasahen duniya. (Fa’iza Mustapha)

Larabawa
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Xi Jinping Ya Taya Kim Jong-Un Murnar Cika Shekaru 78 Da Kafuwar Koriya Ta Arewa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

MASU ALAKA

Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen
Daga Birnin Sin

Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

September 10, 2026
Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki
Daga Birnin Sin

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna
Daga Birnin Sin

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
Next Post
Messi Da Ronado Za Su Hadu A Wani Wasan Sada Zumunci A Watan Fabrairu

Messi Da Ronado Za Su Hadu A Wani Wasan Sada Zumunci A Watan Fabrairu

LABARAI MASU NASABA

Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

September 10, 2026
Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

September 10, 2026
Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

September 10, 2026
Larabawa

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Larabawa

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.