• English
  • Business News
Tuesday, November 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Ta’asar Kungiyoyin Asiri Ke Neman Buwayar Jami’an Tsaro

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Yadda

LABARAI MASU NASABA

Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 

Natasha Ta Zargi Akpabio Da Sanya Jami’an Tsaro Su Ƙwace Mata Fasfo A Filin Jirgin Saman Abuja 

Rikice-rikicen da ke da alaka da ayyukan kungiyoyin asiri yana haifar da babban kalubale ga harkar tsaro a makarantu, al’ummomi da harkokin kasuwanci, wanda ya yi sanadiyar mutuwar mutane da dama, ciki har da wani babban jami’in ‘yansanda dake aiki a yankin Niger Delta.

Binciken da LEADERSHIP ta gudanar ya nuna cewa tashe-tashen hankulan galibi sun shafi jihohin Kudancin Nijeriya ne, kuma suna lakume rayukan al’umma, sannan a wasu lokutan ya kan tilasta wa ‘yansanda da sauran jami’an tsaro janyewa daga bakin aiki.

  • NNPP Ta Bukaci Majalisar Shari’a Ta Kasa Ta Binciki Hukuncin Da Aka Yanke Wa  Gwamna Yusuf
  • Sanata Kaka Lawan Ya Gabatar Da Kudirin Tattara Dokokin Nijeriya Na Tsawon Shekara 19

Hakan dai na faruwa ne duk da irin namijin kokarin da ‘yan sandan ke yi na ganin an dakile lamarin, inda aka kama mutane da dama a ‘yan kwanakin nan.

Kuma bisa ga bayanan ‘yansanda da al’ummomi mazauna yankunan, rikicin da ke da alaka da kungiyoyin asiri ya zama ruwan dare, shirye-shiryen ‘yan daba na shiga aikata laifuka yana da alaka da ta’ammali da muggan kwayoyi. Abin da ya fi tsoratarwa shi ne yadda ’yan dabar suka samu hanyar shiga cikin makarantun sakandire a wasu jihohin inda hukumomi suka kasa tabuka komai.

A Akwa Ibom, al’amuran da suka shafi kungiyoyin asiri da matasa masu ta’ammali da miyagun kwayoyi ke kara ta’azzara tsawon shekaru, wanda a cewar jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yansandan jihar (PPRO), SP Odiko MacDon, shi ne babban dalilin kafa Kungiyar Anti-Cult (ACU) don yakar wannan muguwar dabi’a.

Rikicin da LEADERSHIP Sunday ta gano, ya yi sanadin mutuwar mutane da dama a jihar cikin shekara guda da ta wuce.

“Laifukan da aka samu a jihar da dama na da nasaba da kungiyar asiri kuma da yawa daga cikinsu (‘yan kungiyar asirin) suna tsare, yayin da wasu da dama ke fuskantar shari’o’i daban-daban a kotu, wadanda aka samu da laifi an daure su a gidan yari daban-daban, wasu daga cikinsu ma hukuncin kisa,” wani babban jami’in shigar da kara na hukumar binciken manyan laifuka (CID) da ke Ikot Akpanabia, shedikwatar jihar, ya shaida wa wakilinmu kan sharadin boye sunansa.

Ya ambaci sunan wani Akaniyene Isaac, mai shekaru 23, wanda ya kashe mahaifiyarsa mai shekaru 55 kwanan nan saboda ta ki ba shi kudi domin shan muggan kwayoyi da kuma biyansa wasu bukatu na kashin kansa, a halin yanzu yana fuskantar shari’a a kotu.

“Babban rikicin kungiyar asiri yana faru ne a makarantar Technical Ewet, Garuruwa Hudu da sauransu, inda hakan ya tilasta wa gwamnati shiga tsakani ta hanyar ba da umarnin kafa shingaye, tare da dakatar da wasu dalibai masu laifi, yayin da aka bukaci wasu su zo tare da iyayensu don sanya hannu kan wani aiki kafin su ci gaba da karatunsu.

Bayan haka, ma’aikatar ilimi karkashin jagorancin Kwamishina, Misis Idongesit Etiebet, ta samu ta haramta daukar dalibai ba tare da an shiga kakar karatu ba, a cewar Mis Agnes Thompson, wata malamar makarantar gwamnati a makarantar gwamnati, Iba Oku, “dubi dai yadda ake samun kwararowar dalibai da aka kore su daga wasu makarantu saboda halin daba da kuma yadda suke sake shiga wasu makarantun”.

A jami’ar Uyo (UNIUYO), wani jami’in tsaro Ime Edet ya bayyana cewa jami’o’in biyu da ke titin Ikpa da kuma babbar makarantar da ke Nwaniba, Uyo wanda a da ta kasance gidajen wasan kwaikwayo da ake fama da rikicin addini a tsawon shekaru, a cikin shekara daya da ta wuce, amma ta dawo hayyacinta saboda “ingartacciyar kulawa da saka hannun jari da kula da harkokin tsaro da ‘yan sanda suka yi, da hadin gwiwar hukumar gudanarwar makarantar karkashin jagorancin mataimakin shugaban jami’ar Farfesa Nyaudoh Ndaeyo.”

Amma a Jami’ar Jihar Akwa Ibom (AKSU), musamman babbar jami’ar da ke Ikot Akpaden da ke Karamar Hukumar Mkpat Enin, an samu kashe-kashen kungiyoyin asiri kamar yadda LEADERSHIP Sunday ta tabbatar, hakan kuma ya sanya tsoro a zukatan dalibai tare da samun wasu kashe-kashen shekarar karatu ta karshe a makarantun ilimi,har ma da cikin al’umma musamman a Kananan Hukumomin Ahoada- Gabas, Ahoada-West da kuma Birnin Fatakwal na jihar.

Wadannan ayyuka, LEADERSHIP Lahadi ta gano cewa, suna tsakanin gungun kungiyoyin asiri na Iceland da ke zaune cikin al’ummomi. Bugu da kari ayyukan wadannan kungiyoyi sun yi sanadiyyar mutuwar mutane da dama a jihar, ciki har da tsohon jami’in ‘yansanda na shiyya (DPO) mai kula da sashen ‘yansanda na Ahoada, Bako Angbashim.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 
Manyan Labarai

Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 

November 4, 2025
Jami’an Tsaro Sun Dawo Da Fasfo Ɗin Sanata Natasha Bayan Ƙwace Shi A Abuja
Manyan Labarai

Natasha Ta Zargi Akpabio Da Sanya Jami’an Tsaro Su Ƙwace Mata Fasfo A Filin Jirgin Saman Abuja 

November 4, 2025
Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo
Manyan Labarai

Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo

November 4, 2025
Next Post
Babban Masallacin Adogba: Sultan Da Makinde Sun Kafa Turbar Kawar Da Bambancin Kabilanci Da Na Addini A Nijeriya

Babban Masallacin Adogba: Sultan Da Makinde Sun Kafa Turbar Kawar Da Bambancin Kabilanci Da Na Addini A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 

Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 

November 4, 2025
Jami’an Tsaro Sun Dawo Da Fasfo Ɗin Sanata Natasha Bayan Ƙwace Shi A Abuja

Natasha Ta Zargi Akpabio Da Sanya Jami’an Tsaro Su Ƙwace Mata Fasfo A Filin Jirgin Saman Abuja 

November 4, 2025
Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo

Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo

November 4, 2025
Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

November 4, 2025
Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

November 3, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

November 3, 2025
An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

November 3, 2025
“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

November 3, 2025
Shugabannin Wasu Kasashe Za Su Halarci Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas A Birnin Shanghai

Shugabannin Wasu Kasashe Za Su Halarci Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas A Birnin Shanghai

November 3, 2025
Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka

Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka

November 3, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.