• English
  • Business News
Saturday, September 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Ta’asar Kungiyoyin Asiri Ke Neman Buwayar Jami’an Tsaro

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Yadda Ta’asar Kungiyoyin Asiri Ke Neman Buwayar Jami’an Tsaro
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

Rikice-rikicen da ke da alaka da ayyukan kungiyoyin asiri yana haifar da babban kalubale ga harkar tsaro a makarantu, al’ummomi da harkokin kasuwanci, wanda ya yi sanadiyar mutuwar mutane da dama, ciki har da wani babban jami’in ‘yansanda dake aiki a yankin Niger Delta.

Binciken da LEADERSHIP ta gudanar ya nuna cewa tashe-tashen hankulan galibi sun shafi jihohin Kudancin Nijeriya ne, kuma suna lakume rayukan al’umma, sannan a wasu lokutan ya kan tilasta wa ‘yansanda da sauran jami’an tsaro janyewa daga bakin aiki.

  • NNPP Ta Bukaci Majalisar Shari’a Ta Kasa Ta Binciki Hukuncin Da Aka Yanke Wa  Gwamna Yusuf
  • Sanata Kaka Lawan Ya Gabatar Da Kudirin Tattara Dokokin Nijeriya Na Tsawon Shekara 19

Hakan dai na faruwa ne duk da irin namijin kokarin da ‘yan sandan ke yi na ganin an dakile lamarin, inda aka kama mutane da dama a ‘yan kwanakin nan.

Kuma bisa ga bayanan ‘yansanda da al’ummomi mazauna yankunan, rikicin da ke da alaka da kungiyoyin asiri ya zama ruwan dare, shirye-shiryen ‘yan daba na shiga aikata laifuka yana da alaka da ta’ammali da muggan kwayoyi. Abin da ya fi tsoratarwa shi ne yadda ’yan dabar suka samu hanyar shiga cikin makarantun sakandire a wasu jihohin inda hukumomi suka kasa tabuka komai.

A Akwa Ibom, al’amuran da suka shafi kungiyoyin asiri da matasa masu ta’ammali da miyagun kwayoyi ke kara ta’azzara tsawon shekaru, wanda a cewar jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yansandan jihar (PPRO), SP Odiko MacDon, shi ne babban dalilin kafa Kungiyar Anti-Cult (ACU) don yakar wannan muguwar dabi’a.

Rikicin da LEADERSHIP Sunday ta gano, ya yi sanadin mutuwar mutane da dama a jihar cikin shekara guda da ta wuce.

“Laifukan da aka samu a jihar da dama na da nasaba da kungiyar asiri kuma da yawa daga cikinsu (‘yan kungiyar asirin) suna tsare, yayin da wasu da dama ke fuskantar shari’o’i daban-daban a kotu, wadanda aka samu da laifi an daure su a gidan yari daban-daban, wasu daga cikinsu ma hukuncin kisa,” wani babban jami’in shigar da kara na hukumar binciken manyan laifuka (CID) da ke Ikot Akpanabia, shedikwatar jihar, ya shaida wa wakilinmu kan sharadin boye sunansa.

Ya ambaci sunan wani Akaniyene Isaac, mai shekaru 23, wanda ya kashe mahaifiyarsa mai shekaru 55 kwanan nan saboda ta ki ba shi kudi domin shan muggan kwayoyi da kuma biyansa wasu bukatu na kashin kansa, a halin yanzu yana fuskantar shari’a a kotu.

“Babban rikicin kungiyar asiri yana faru ne a makarantar Technical Ewet, Garuruwa Hudu da sauransu, inda hakan ya tilasta wa gwamnati shiga tsakani ta hanyar ba da umarnin kafa shingaye, tare da dakatar da wasu dalibai masu laifi, yayin da aka bukaci wasu su zo tare da iyayensu don sanya hannu kan wani aiki kafin su ci gaba da karatunsu.

Bayan haka, ma’aikatar ilimi karkashin jagorancin Kwamishina, Misis Idongesit Etiebet, ta samu ta haramta daukar dalibai ba tare da an shiga kakar karatu ba, a cewar Mis Agnes Thompson, wata malamar makarantar gwamnati a makarantar gwamnati, Iba Oku, “dubi dai yadda ake samun kwararowar dalibai da aka kore su daga wasu makarantu saboda halin daba da kuma yadda suke sake shiga wasu makarantun”.

A jami’ar Uyo (UNIUYO), wani jami’in tsaro Ime Edet ya bayyana cewa jami’o’in biyu da ke titin Ikpa da kuma babbar makarantar da ke Nwaniba, Uyo wanda a da ta kasance gidajen wasan kwaikwayo da ake fama da rikicin addini a tsawon shekaru, a cikin shekara daya da ta wuce, amma ta dawo hayyacinta saboda “ingartacciyar kulawa da saka hannun jari da kula da harkokin tsaro da ‘yan sanda suka yi, da hadin gwiwar hukumar gudanarwar makarantar karkashin jagorancin mataimakin shugaban jami’ar Farfesa Nyaudoh Ndaeyo.”

Amma a Jami’ar Jihar Akwa Ibom (AKSU), musamman babbar jami’ar da ke Ikot Akpaden da ke Karamar Hukumar Mkpat Enin, an samu kashe-kashen kungiyoyin asiri kamar yadda LEADERSHIP Sunday ta tabbatar, hakan kuma ya sanya tsoro a zukatan dalibai tare da samun wasu kashe-kashen shekarar karatu ta karshe a makarantun ilimi,har ma da cikin al’umma musamman a Kananan Hukumomin Ahoada- Gabas, Ahoada-West da kuma Birnin Fatakwal na jihar.

Wadannan ayyuka, LEADERSHIP Lahadi ta gano cewa, suna tsakanin gungun kungiyoyin asiri na Iceland da ke zaune cikin al’ummomi. Bugu da kari ayyukan wadannan kungiyoyi sun yi sanadiyyar mutuwar mutane da dama a jihar, ciki har da tsohon jami’in ‘yansanda na shiyya (DPO) mai kula da sashen ‘yansanda na Ahoada, Bako Angbashim.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Zargin Kafar Angulu Ga Dimokuradiyyar Nijeriya: Cacar Baki Ta Barke Tsakanin ‘Yan Adawa Da Gwamnati

Next Post

Babban Masallacin Adogba: Sultan Da Makinde Sun Kafa Turbar Kawar Da Bambancin Kabilanci Da Na Addini A Nijeriya

Related

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?
Manyan Labarai

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

11 hours ago
Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna
Manyan Labarai

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

11 hours ago
Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban
Manyan Labarai

Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban

22 hours ago
Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi
Manyan Labarai

Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

23 hours ago
NNPP
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

1 day ago
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna
Manyan Labarai

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

2 days ago
Next Post
Babban Masallacin Adogba: Sultan Da Makinde Sun Kafa Turbar Kawar Da Bambancin Kabilanci Da Na Addini A Nijeriya

Babban Masallacin Adogba: Sultan Da Makinde Sun Kafa Turbar Kawar Da Bambancin Kabilanci Da Na Addini A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

September 19, 2025
Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

September 19, 2025
An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

September 19, 2025
Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

September 19, 2025
Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

September 19, 2025
Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

September 19, 2025
Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

September 19, 2025
Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

September 19, 2025
Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

September 19, 2025
Yadda

Tarihin Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Firimiyan Arewa

September 19, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.