ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Ta’asar Kungiyoyin Asiri Ke Neman Buwayar Jami’an Tsaro

by Rabi'u Ali Indabawa
3 years ago
Yadda

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Rikice-rikicen da ke da alaka da ayyukan kungiyoyin asiri yana haifar da babban kalubale ga harkar tsaro a makarantu, al’ummomi da harkokin kasuwanci, wanda ya yi sanadiyar mutuwar mutane da dama, ciki har da wani babban jami’in ‘yansanda dake aiki a yankin Niger Delta.

Binciken da LEADERSHIP ta gudanar ya nuna cewa tashe-tashen hankulan galibi sun shafi jihohin Kudancin Nijeriya ne, kuma suna lakume rayukan al’umma, sannan a wasu lokutan ya kan tilasta wa ‘yansanda da sauran jami’an tsaro janyewa daga bakin aiki.

  • NNPP Ta Bukaci Majalisar Shari’a Ta Kasa Ta Binciki Hukuncin Da Aka Yanke Wa  Gwamna Yusuf
  • Sanata Kaka Lawan Ya Gabatar Da Kudirin Tattara Dokokin Nijeriya Na Tsawon Shekara 19

Hakan dai na faruwa ne duk da irin namijin kokarin da ‘yan sandan ke yi na ganin an dakile lamarin, inda aka kama mutane da dama a ‘yan kwanakin nan.

Kuma bisa ga bayanan ‘yansanda da al’ummomi mazauna yankunan, rikicin da ke da alaka da kungiyoyin asiri ya zama ruwan dare, shirye-shiryen ‘yan daba na shiga aikata laifuka yana da alaka da ta’ammali da muggan kwayoyi. Abin da ya fi tsoratarwa shi ne yadda ’yan dabar suka samu hanyar shiga cikin makarantun sakandire a wasu jihohin inda hukumomi suka kasa tabuka komai.

A Akwa Ibom, al’amuran da suka shafi kungiyoyin asiri da matasa masu ta’ammali da miyagun kwayoyi ke kara ta’azzara tsawon shekaru, wanda a cewar jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yansandan jihar (PPRO), SP Odiko MacDon, shi ne babban dalilin kafa Kungiyar Anti-Cult (ACU) don yakar wannan muguwar dabi’a.

Rikicin da LEADERSHIP Sunday ta gano, ya yi sanadin mutuwar mutane da dama a jihar cikin shekara guda da ta wuce.

“Laifukan da aka samu a jihar da dama na da nasaba da kungiyar asiri kuma da yawa daga cikinsu (‘yan kungiyar asirin) suna tsare, yayin da wasu da dama ke fuskantar shari’o’i daban-daban a kotu, wadanda aka samu da laifi an daure su a gidan yari daban-daban, wasu daga cikinsu ma hukuncin kisa,” wani babban jami’in shigar da kara na hukumar binciken manyan laifuka (CID) da ke Ikot Akpanabia, shedikwatar jihar, ya shaida wa wakilinmu kan sharadin boye sunansa.

Ya ambaci sunan wani Akaniyene Isaac, mai shekaru 23, wanda ya kashe mahaifiyarsa mai shekaru 55 kwanan nan saboda ta ki ba shi kudi domin shan muggan kwayoyi da kuma biyansa wasu bukatu na kashin kansa, a halin yanzu yana fuskantar shari’a a kotu.

“Babban rikicin kungiyar asiri yana faru ne a makarantar Technical Ewet, Garuruwa Hudu da sauransu, inda hakan ya tilasta wa gwamnati shiga tsakani ta hanyar ba da umarnin kafa shingaye, tare da dakatar da wasu dalibai masu laifi, yayin da aka bukaci wasu su zo tare da iyayensu don sanya hannu kan wani aiki kafin su ci gaba da karatunsu.

Bayan haka, ma’aikatar ilimi karkashin jagorancin Kwamishina, Misis Idongesit Etiebet, ta samu ta haramta daukar dalibai ba tare da an shiga kakar karatu ba, a cewar Mis Agnes Thompson, wata malamar makarantar gwamnati a makarantar gwamnati, Iba Oku, “dubi dai yadda ake samun kwararowar dalibai da aka kore su daga wasu makarantu saboda halin daba da kuma yadda suke sake shiga wasu makarantun”.

A jami’ar Uyo (UNIUYO), wani jami’in tsaro Ime Edet ya bayyana cewa jami’o’in biyu da ke titin Ikpa da kuma babbar makarantar da ke Nwaniba, Uyo wanda a da ta kasance gidajen wasan kwaikwayo da ake fama da rikicin addini a tsawon shekaru, a cikin shekara daya da ta wuce, amma ta dawo hayyacinta saboda “ingartacciyar kulawa da saka hannun jari da kula da harkokin tsaro da ‘yan sanda suka yi, da hadin gwiwar hukumar gudanarwar makarantar karkashin jagorancin mataimakin shugaban jami’ar Farfesa Nyaudoh Ndaeyo.”

Amma a Jami’ar Jihar Akwa Ibom (AKSU), musamman babbar jami’ar da ke Ikot Akpaden da ke Karamar Hukumar Mkpat Enin, an samu kashe-kashen kungiyoyin asiri kamar yadda LEADERSHIP Sunday ta tabbatar, hakan kuma ya sanya tsoro a zukatan dalibai tare da samun wasu kashe-kashen shekarar karatu ta karshe a makarantun ilimi,har ma da cikin al’umma musamman a Kananan Hukumomin Ahoada- Gabas, Ahoada-West da kuma Birnin Fatakwal na jihar.

Wadannan ayyuka, LEADERSHIP Lahadi ta gano cewa, suna tsakanin gungun kungiyoyin asiri na Iceland da ke zaune cikin al’ummomi. Bugu da kari ayyukan wadannan kungiyoyi sun yi sanadiyyar mutuwar mutane da dama a jihar, ciki har da tsohon jami’in ‘yansanda na shiyya (DPO) mai kula da sashen ‘yansanda na Ahoada, Bako Angbashim.

Yadda
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
Babban Masallacin Adogba: Sultan Da Makinde Sun Kafa Turbar Kawar Da Bambancin Kabilanci Da Na Addini A Nijeriya

Babban Masallacin Adogba: Sultan Da Makinde Sun Kafa Turbar Kawar Da Bambancin Kabilanci Da Na Addini A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.