ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Ta’asar Kungiyoyin Asiri Ke Neman Buwayar Jami’an Tsaro

by Rabi'u Ali Indabawa
3 years ago
Yadda

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

Rikice-rikicen da ke da alaka da ayyukan kungiyoyin asiri yana haifar da babban kalubale ga harkar tsaro a makarantu, al’ummomi da harkokin kasuwanci, wanda ya yi sanadiyar mutuwar mutane da dama, ciki har da wani babban jami’in ‘yansanda dake aiki a yankin Niger Delta.

Binciken da LEADERSHIP ta gudanar ya nuna cewa tashe-tashen hankulan galibi sun shafi jihohin Kudancin Nijeriya ne, kuma suna lakume rayukan al’umma, sannan a wasu lokutan ya kan tilasta wa ‘yansanda da sauran jami’an tsaro janyewa daga bakin aiki.

  • NNPP Ta Bukaci Majalisar Shari’a Ta Kasa Ta Binciki Hukuncin Da Aka Yanke Wa  Gwamna Yusuf
  • Sanata Kaka Lawan Ya Gabatar Da Kudirin Tattara Dokokin Nijeriya Na Tsawon Shekara 19

Hakan dai na faruwa ne duk da irin namijin kokarin da ‘yan sandan ke yi na ganin an dakile lamarin, inda aka kama mutane da dama a ‘yan kwanakin nan.

Kuma bisa ga bayanan ‘yansanda da al’ummomi mazauna yankunan, rikicin da ke da alaka da kungiyoyin asiri ya zama ruwan dare, shirye-shiryen ‘yan daba na shiga aikata laifuka yana da alaka da ta’ammali da muggan kwayoyi. Abin da ya fi tsoratarwa shi ne yadda ’yan dabar suka samu hanyar shiga cikin makarantun sakandire a wasu jihohin inda hukumomi suka kasa tabuka komai.

A Akwa Ibom, al’amuran da suka shafi kungiyoyin asiri da matasa masu ta’ammali da miyagun kwayoyi ke kara ta’azzara tsawon shekaru, wanda a cewar jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yansandan jihar (PPRO), SP Odiko MacDon, shi ne babban dalilin kafa Kungiyar Anti-Cult (ACU) don yakar wannan muguwar dabi’a.

Rikicin da LEADERSHIP Sunday ta gano, ya yi sanadin mutuwar mutane da dama a jihar cikin shekara guda da ta wuce.

“Laifukan da aka samu a jihar da dama na da nasaba da kungiyar asiri kuma da yawa daga cikinsu (‘yan kungiyar asirin) suna tsare, yayin da wasu da dama ke fuskantar shari’o’i daban-daban a kotu, wadanda aka samu da laifi an daure su a gidan yari daban-daban, wasu daga cikinsu ma hukuncin kisa,” wani babban jami’in shigar da kara na hukumar binciken manyan laifuka (CID) da ke Ikot Akpanabia, shedikwatar jihar, ya shaida wa wakilinmu kan sharadin boye sunansa.

Ya ambaci sunan wani Akaniyene Isaac, mai shekaru 23, wanda ya kashe mahaifiyarsa mai shekaru 55 kwanan nan saboda ta ki ba shi kudi domin shan muggan kwayoyi da kuma biyansa wasu bukatu na kashin kansa, a halin yanzu yana fuskantar shari’a a kotu.

“Babban rikicin kungiyar asiri yana faru ne a makarantar Technical Ewet, Garuruwa Hudu da sauransu, inda hakan ya tilasta wa gwamnati shiga tsakani ta hanyar ba da umarnin kafa shingaye, tare da dakatar da wasu dalibai masu laifi, yayin da aka bukaci wasu su zo tare da iyayensu don sanya hannu kan wani aiki kafin su ci gaba da karatunsu.

Bayan haka, ma’aikatar ilimi karkashin jagorancin Kwamishina, Misis Idongesit Etiebet, ta samu ta haramta daukar dalibai ba tare da an shiga kakar karatu ba, a cewar Mis Agnes Thompson, wata malamar makarantar gwamnati a makarantar gwamnati, Iba Oku, “dubi dai yadda ake samun kwararowar dalibai da aka kore su daga wasu makarantu saboda halin daba da kuma yadda suke sake shiga wasu makarantun”.

A jami’ar Uyo (UNIUYO), wani jami’in tsaro Ime Edet ya bayyana cewa jami’o’in biyu da ke titin Ikpa da kuma babbar makarantar da ke Nwaniba, Uyo wanda a da ta kasance gidajen wasan kwaikwayo da ake fama da rikicin addini a tsawon shekaru, a cikin shekara daya da ta wuce, amma ta dawo hayyacinta saboda “ingartacciyar kulawa da saka hannun jari da kula da harkokin tsaro da ‘yan sanda suka yi, da hadin gwiwar hukumar gudanarwar makarantar karkashin jagorancin mataimakin shugaban jami’ar Farfesa Nyaudoh Ndaeyo.”

Amma a Jami’ar Jihar Akwa Ibom (AKSU), musamman babbar jami’ar da ke Ikot Akpaden da ke Karamar Hukumar Mkpat Enin, an samu kashe-kashen kungiyoyin asiri kamar yadda LEADERSHIP Sunday ta tabbatar, hakan kuma ya sanya tsoro a zukatan dalibai tare da samun wasu kashe-kashen shekarar karatu ta karshe a makarantun ilimi,har ma da cikin al’umma musamman a Kananan Hukumomin Ahoada- Gabas, Ahoada-West da kuma Birnin Fatakwal na jihar.

Wadannan ayyuka, LEADERSHIP Lahadi ta gano cewa, suna tsakanin gungun kungiyoyin asiri na Iceland da ke zaune cikin al’ummomi. Bugu da kari ayyukan wadannan kungiyoyi sun yi sanadiyyar mutuwar mutane da dama a jihar, ciki har da tsohon jami’in ‘yansanda na shiyya (DPO) mai kula da sashen ‘yansanda na Ahoada, Bako Angbashim.

Yadda
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Next Post
Babban Masallacin Adogba: Sultan Da Makinde Sun Kafa Turbar Kawar Da Bambancin Kabilanci Da Na Addini A Nijeriya

Babban Masallacin Adogba: Sultan Da Makinde Sun Kafa Turbar Kawar Da Bambancin Kabilanci Da Na Addini A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.