• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Al’ajabi: Yadda Wani Maniyyaci Ya Fara Aikin Hajjinsa A Sansanin Alhazai Na Kano Bayan Rasa Kujerarsa

byAbdullahi Muh'd Sheka
3 years ago
Al'ajabi

Wani abu mai kama da wasan kwaikwayo da ya faru a Kano ranar Alhamis, inda wani Maniyyaci wanda bai samu shiga cikin jirgin karshe zuwa Saudiyya ba, ya kaddamar da fara aikin Hajjinsa a sansanin Alhazai da ke jihar Kano, wanda ya ce zai kuma kammala hajjin nasa a sansanin.

Maniyyacin, Malam Jibrin Abdu, daga karamar hukumar Gezawa ya dauki hankalin mutane bayan da aka hange shi sanye da harami wanda ya nuna fara aikin hajjinsa a sansanin alhazan.

  • Mahara Sun Sace Basarake Da Matar Aure A Kano
  • Hukumar Kashe Gobara A Jihar Kano Ta Ceto Mutum 135 A Watan Yuni

“Ni na fara aikin hajji na tunda akwai dukkan abubuwan da ake bukata a nan, na tabbata zan dawo na kammala aikin, na san yadda ake yi. Wannan ba shi ne zuwana na fari ba, na kuma tabbata ba zai zama na karshe ba,” Inji shi.

Ya kara da cewa, “Na sayar da gonata domin samun zuwa aikin Hajjin, amma wasu shugabannin gangan sun haramta min zuwa hajji,” duk da ya aminta da cewar hakan nufin Allah ne.

Bayan Malam Abdu, ita ma wata mata, Suwaiba Sani, tare da wasu mutane masu yawa, sun yi Allah wadarai tare da dora wannan laifi kan wadanda suka yi sanadin hana su shiga jirgin, wanda cikin fushi suka bayyana cewa ba za su taba yafe wa duk wadanda suke da hannu wajen haramta masu zuwa aikin hajjin ba.

LABARAI MASU NASABA

Matashi Ya Kashe Kakanninsa Kan Abinci A Kano

Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

Wakilin LEADERSHIP Hausa a jihar Kano ya nakalto cewa, a kalla maniyyata 745 ne aka bari a kasa a filin sauka da tashin jiragen sama na Malam Aminu Kano a ranar Alhamis bayan da jirgin karshe ya tashi zuwa kasa mai tsarki da misalin karfe 3:45 na yammacin Alhamis din.

Babban sakataren hukumar Alhazai ta Jihar Kano, Muhammad Abba Danbatta, wanda shi ma bai samu tashi a wannan jirgin ba, tare da sauran daraktoci hukumar, ya alakanta wannan matsala da gazawar hukumar alhazan ta kasa bisa rashin cika alkawarin kamfanin da aka yi alkawarin jigilar alhazan na Azman wanda ya sa har sai da Gwamnatin Saudiyya ta kara tsawaita lokacin daukar alhazan amma duk da hakan sai da aka bar wasu da daman.

Kazalika, LEADERSHIP Hausa ta tabbatar da cewa, bayan jihar Kano din, a jihohin kasar nan da dama an samu matsalar jigilar Alhazai inda wasu maniyyata da dama suka rasa damar zuwa hajjin a bana.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano
Al'ajabi

Matashi Ya Kashe Kakanninsa Kan Abinci A Kano

September 25, 2025
Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye
Al'ajabi

Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

September 17, 2025
Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi
Al'ajabi

Wata Ta Kashe ’Yar Uwarta Kan Bashin Naira 800 A Ondo

September 16, 2025
Next Post
Sallah: Gwamnan Gombe Ya Gwangwaje Mata Da Matasa Da Naira Miliyan 114

Sallah: Gwamnan Gombe Ya Gwangwaje Mata Da Matasa Da Naira Miliyan 114

LABARAI MASU NASABA

A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version