ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Al’ajabi: Yadda Wani Maniyyaci Ya Fara Aikin Hajjinsa A Sansanin Alhazai Na Kano Bayan Rasa Kujerarsa

by Abdullahi Muh'd Sheka
4 years ago
Al'ajabi

Wani abu mai kama da wasan kwaikwayo da ya faru a Kano ranar Alhamis, inda wani Maniyyaci wanda bai samu shiga cikin jirgin karshe zuwa Saudiyya ba, ya kaddamar da fara aikin Hajjinsa a sansanin Alhazai da ke jihar Kano, wanda ya ce zai kuma kammala hajjin nasa a sansanin.

Maniyyacin, Malam Jibrin Abdu, daga karamar hukumar Gezawa ya dauki hankalin mutane bayan da aka hange shi sanye da harami wanda ya nuna fara aikin hajjinsa a sansanin alhazan.

  • Mahara Sun Sace Basarake Da Matar Aure A Kano
  • Hukumar Kashe Gobara A Jihar Kano Ta Ceto Mutum 135 A Watan Yuni

“Ni na fara aikin hajji na tunda akwai dukkan abubuwan da ake bukata a nan, na tabbata zan dawo na kammala aikin, na san yadda ake yi. Wannan ba shi ne zuwana na fari ba, na kuma tabbata ba zai zama na karshe ba,” Inji shi.

ADVERTISEMENT

Ya kara da cewa, “Na sayar da gonata domin samun zuwa aikin Hajjin, amma wasu shugabannin gangan sun haramta min zuwa hajji,” duk da ya aminta da cewar hakan nufin Allah ne.

Bayan Malam Abdu, ita ma wata mata, Suwaiba Sani, tare da wasu mutane masu yawa, sun yi Allah wadarai tare da dora wannan laifi kan wadanda suka yi sanadin hana su shiga jirgin, wanda cikin fushi suka bayyana cewa ba za su taba yafe wa duk wadanda suke da hannu wajen haramta masu zuwa aikin hajjin ba.

LABARAI MASU NASABA

Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

EFCC Ta Cafke Lauyan Bogi Da Mallakar Hatimin Kungiyar Lauyoyi Ta Nijeriya Na Jabu A Legas

Wakilin LEADERSHIP Hausa a jihar Kano ya nakalto cewa, a kalla maniyyata 745 ne aka bari a kasa a filin sauka da tashin jiragen sama na Malam Aminu Kano a ranar Alhamis bayan da jirgin karshe ya tashi zuwa kasa mai tsarki da misalin karfe 3:45 na yammacin Alhamis din.

Babban sakataren hukumar Alhazai ta Jihar Kano, Muhammad Abba Danbatta, wanda shi ma bai samu tashi a wannan jirgin ba, tare da sauran daraktoci hukumar, ya alakanta wannan matsala da gazawar hukumar alhazan ta kasa bisa rashin cika alkawarin kamfanin da aka yi alkawarin jigilar alhazan na Azman wanda ya sa har sai da Gwamnatin Saudiyya ta kara tsawaita lokacin daukar alhazan amma duk da hakan sai da aka bar wasu da daman.

Kazalika, LEADERSHIP Hausa ta tabbatar da cewa, bayan jihar Kano din, a jihohin kasar nan da dama an samu matsalar jigilar Alhazai inda wasu maniyyata da dama suka rasa damar zuwa hajjin a bana.

Al'ajabi
Abdullahi Muh'd Sheka
+ postsBio
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Sakamakon Matsin Lambar Jami’an Tsaro, ‘Yan Ta’adda Na Fuskantar Ƙarancin Abinci
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Kisan Gillar Mutum 7 A Kano: Sarakuna Da Malamai Da Iyaye Sun Nemi A Gaggauta Yanke Wa Waɗanda Ake Zargi Hukunci
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    MACBAN Ta Nemi Amurka Ta Cire Sunanta Daga Jerin Waɗanda Ta Ƙaƙabawa Takunkumi
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Faɗace-Faɗacen Daba Da Ƙwacen Waya A Kano Ya Ɗauki Sabon Salo

MASU ALAKA

Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa
Al'ajabi

Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

June 9, 2026
EFCC Ta Cafke Lauyan Bogi Da Mallakar Hatimin Kungiyar Lauyoyi Ta Nijeriya Na Jabu A Legas
Al'ajabi

EFCC Ta Cafke Lauyan Bogi Da Mallakar Hatimin Kungiyar Lauyoyi Ta Nijeriya Na Jabu A Legas

April 21, 2026
Yadda Aka Gano Ƙasusuwan Dabba Mai Shekara Miliyan 100 A Nijar
Al'ajabi

Yadda Aka Gano Ƙasusuwan Dabba Mai Shekara Miliyan 100 A Nijar

March 8, 2026
Next Post
Sallah: Gwamnan Gombe Ya Gwangwaje Mata Da Matasa Da Naira Miliyan 114

Sallah: Gwamnan Gombe Ya Gwangwaje Mata Da Matasa Da Naira Miliyan 114

LABARAI MASU NASABA

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.