ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Al’ajabi: Yadda Wani Maniyyaci Ya Fara Aikin Hajjinsa A Sansanin Alhazai Na Kano Bayan Rasa Kujerarsa

by Abdullahi Muh'd Sheka
4 years ago
Al'ajabi

Wani abu mai kama da wasan kwaikwayo da ya faru a Kano ranar Alhamis, inda wani Maniyyaci wanda bai samu shiga cikin jirgin karshe zuwa Saudiyya ba, ya kaddamar da fara aikin Hajjinsa a sansanin Alhazai da ke jihar Kano, wanda ya ce zai kuma kammala hajjin nasa a sansanin.

Maniyyacin, Malam Jibrin Abdu, daga karamar hukumar Gezawa ya dauki hankalin mutane bayan da aka hange shi sanye da harami wanda ya nuna fara aikin hajjinsa a sansanin alhazan.

  • Mahara Sun Sace Basarake Da Matar Aure A Kano
  • Hukumar Kashe Gobara A Jihar Kano Ta Ceto Mutum 135 A Watan Yuni

“Ni na fara aikin hajji na tunda akwai dukkan abubuwan da ake bukata a nan, na tabbata zan dawo na kammala aikin, na san yadda ake yi. Wannan ba shi ne zuwana na fari ba, na kuma tabbata ba zai zama na karshe ba,” Inji shi.

ADVERTISEMENT

Ya kara da cewa, “Na sayar da gonata domin samun zuwa aikin Hajjin, amma wasu shugabannin gangan sun haramta min zuwa hajji,” duk da ya aminta da cewar hakan nufin Allah ne.

Bayan Malam Abdu, ita ma wata mata, Suwaiba Sani, tare da wasu mutane masu yawa, sun yi Allah wadarai tare da dora wannan laifi kan wadanda suka yi sanadin hana su shiga jirgin, wanda cikin fushi suka bayyana cewa ba za su taba yafe wa duk wadanda suke da hannu wajen haramta masu zuwa aikin hajjin ba.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Ɗa Da Uwa Suka Ɗauki Hayar Wani Don Ya Kashe Mahaifinsa A Kano

Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

Wakilin LEADERSHIP Hausa a jihar Kano ya nakalto cewa, a kalla maniyyata 745 ne aka bari a kasa a filin sauka da tashin jiragen sama na Malam Aminu Kano a ranar Alhamis bayan da jirgin karshe ya tashi zuwa kasa mai tsarki da misalin karfe 3:45 na yammacin Alhamis din.

Babban sakataren hukumar Alhazai ta Jihar Kano, Muhammad Abba Danbatta, wanda shi ma bai samu tashi a wannan jirgin ba, tare da sauran daraktoci hukumar, ya alakanta wannan matsala da gazawar hukumar alhazan ta kasa bisa rashin cika alkawarin kamfanin da aka yi alkawarin jigilar alhazan na Azman wanda ya sa har sai da Gwamnatin Saudiyya ta kara tsawaita lokacin daukar alhazan amma duk da hakan sai da aka bar wasu da daman.

Kazalika, LEADERSHIP Hausa ta tabbatar da cewa, bayan jihar Kano din, a jihohin kasar nan da dama an samu matsalar jigilar Alhazai inda wasu maniyyata da dama suka rasa damar zuwa hajjin a bana.

Al'ajabi
Abdullahi Muh'd Sheka
+ postsBio
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Sakamakon Matsin Lambar Jami’an Tsaro, ‘Yan Ta’adda Na Fuskantar Ƙarancin Abinci
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Kisan Gillar Mutum 7 A Kano: Sarakuna Da Malamai Da Iyaye Sun Nemi A Gaggauta Yanke Wa Waɗanda Ake Zargi Hukunci
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    MACBAN Ta Nemi Amurka Ta Cire Sunanta Daga Jerin Waɗanda Ta Ƙaƙabawa Takunkumi
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Faɗace-Faɗacen Daba Da Ƙwacen Waya A Kano Ya Ɗauki Sabon Salo

MASU ALAKA

Yadda Ɗa Da Uwa Suka Ɗauki Hayar Wani Don Ya Kashe Mahaifinsa A Kano
Al'ajabi

Yadda Ɗa Da Uwa Suka Ɗauki Hayar Wani Don Ya Kashe Mahaifinsa A Kano

August 14, 2026
Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa
Al'ajabi

Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

June 9, 2026
EFCC Ta Cafke Lauyan Bogi Da Mallakar Hatimin Kungiyar Lauyoyi Ta Nijeriya Na Jabu A Legas
Al'ajabi

EFCC Ta Cafke Lauyan Bogi Da Mallakar Hatimin Kungiyar Lauyoyi Ta Nijeriya Na Jabu A Legas

April 21, 2026
Next Post
Sallah: Gwamnan Gombe Ya Gwangwaje Mata Da Matasa Da Naira Miliyan 114

Sallah: Gwamnan Gombe Ya Gwangwaje Mata Da Matasa Da Naira Miliyan 114

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

September 9, 2026
Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

September 9, 2026
“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

September 9, 2026
’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.