• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Ta Sake Bukatar Sojin Nijar Su Saki Bazoum

by Sadiq
2 years ago
in Labarai
0
Nijeriya Ta Sake Bukatar Sojin Nijar Su Saki Bazoum
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan harkokin waje, Yusuf Maitama Tuggar, ya ce har yanzu ECOWAS a shirye ta ke domin tattauna da sojojin da suka yi juyin mulki a Nijar kan su saki Bazoum kafin a fara tattaunawar cire takunkumin da aka sanya wa Nijar.

Njeriya ta bukaci a saki hambararren shugaban kasar Nijar, Mohamed Bazoum sannan kuma gwamnatin mulkin sojin kasar ta ba shi damar zuwa wata kasa, in ji ministan harkokin wajen Nijeriya.

  • Kotu Ta Umarci Dawo Da Motoci 50 Da Tsohon Gwamnan Zamfara Ya Kwashe
  • Harin Jirgin Sojin Nijeriya Ya Haifar Da Rudani A Kaduna

A halin yanzu dai Nijeriya ce ke shugabantar kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afirka (ECOWAS), wacce ta kakaba wa Nijar takunkumi bayan juyin mulkin da ya kifar da gwamnatin Bazoum a watan Yuli.

ECOWAS dai ta yi ta kira a mayar da Bazoum kan karagar mulki ba tare da bata lokaci ba, amma gwamnatin sojin kasar ta ci gaba da tsare shi ta kuma ce tana bukatar shekaru uku kafin ta mayar da mulki ga farar hula.

“Muna bukatar su saki shugaba Bazoum domin a ba shi dama ya bar Nijar.

Labarai Masu Nasaba

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

“Ba za a ci gaba da tsare shi ba. Zai je wata kasa da ta amince ta karbe shi. Daga nan za mu fara magana kan cire takunkumin da aka sanya wa kasar,” a cewar Tuggar.

Ya kuma ce har yanzu kungiyar ECOWAS a shirye ta ke don tattauna da gwamnatin sojin Nijar.

A ranar 10 ga watan Disamba ne shugabannin ECOWAS za su gana a Abuja, domin tattaunawa kan yadda juyin mulki ke ta’azzara a yammacin Afirka, wanda tun a 2020 aka yi ta samun juyin mulkin da ya dora sojoji kan karagar mulki a kasashen Mali, Burkina Faso, Guinea da Nijar.

A watan Nuwamba, an samu wani yunkurin juyin mulki da bai yi nasara ba a kasar Saliyo, sai dai ya yi sanadin mutuwar mutane 21.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BazoumJuyin MulkiNijeriyaSojin Nijar
ShareTweetSendShare
Previous Post

Harin Jirgin Sojin Nijeriya A Kan Taron Maulidi Ya Tayar Da Hankali A Kaduna

Next Post

Kotu Ta Yi Wa Mutane 4 Daurin Rai Da Rai Bisa Samun Su Da Laifin Daukar Nauyin Boko Haram

Related

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote
Labarai

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

18 minutes ago
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

1 hour ago
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

6 hours ago
Nijar
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

6 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

7 hours ago
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

10 hours ago
Next Post
Matar Aure Ta Bukaci Kotu Ta Raba Aurenta Da Mijinta Saboda Yawan Jima’i

Kotu Ta Yi Wa Mutane 4 Daurin Rai Da Rai Bisa Samun Su Da Laifin Daukar Nauyin Boko Haram

LABARAI MASU NASABA

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Nijar

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.