• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tudun Biri: Garin Harin Bam, Ya Shekara Fiye Da 200 Babu Asibiti Da Makarantar Boko

by Shehu Yahaya
1 year ago
in Labarai
0
Tudun Biri
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram
  • Ba Ma Ganin ‘Yan Siyasa Sai Lokacin Zabe
  • Har Yanzu Muna Fuskantar Barazanar Tsaro, In Ji Mazauna Garin

Garin Tudun Biri, da ke Gundumar Afaka a Karamar Hukumar Igabi da ke jihar Kaduna, wanda ya karade kafafen yada labarai tun daga makon jiya saboda harim bam da sojoji suka kai, gari ne da ya kwashe fiye da shekaru 200 da kafuwa ba tare da samun asibiti ko makarantar boko ba.

Gari ne na manoma da ya kunshi Zallar Hausawa da tsirarun gwarawa mai makwabtaka da filin sauka da tashin jiragen sama na Kaduna amma abin mamaki garin duk da kasancewarsa mafi kusa da filin jiragen saman na Kaduna amma babu abubuwan more rayuwa.

  • Gwamnatin Kano Za Ta Biya Wadanda Ta Yi Wa Rusau Diyyar N3bn
  • Al’ummar Tudun Biri Sun Kai Karar Gwamnatin Tarayya Kan Biyan Su Diyya

Wani Dattijo mai shekara 74 a duniya, ya shaida wa wakilinmu cewa, Tudun Biri gari ne mai tsohon tarihi domin hatta kakansa ma a nan aka haife shi, sannan suna zaman lafiya a tsakanin Hausawa da Gwarawa da kuma Fulani da ke yankin.

A wata ziyara da Wakilinmu ya kai garin, wani matashi ya dauke a babur inda suka kewaya garin tare da ganin yadda mazauna kauyen ke rayuwa babu asibiti ko da sha-ka-ta-fi, wutar lantarki ko makarantar boko, duk da cewa suna taka rawar gani wajen zaben shugabanni lokacin zabe.

Duk da cewa galibin mutanen Tudun Biri manoma ne amma ba su da hanyar da idan sun girbe amfanin gona za su fitar zuwa kasuwa ga kuma matsalar rashin tsaro na ‘yan bindiga da suke musu barazana.
Wakilinmu ya tarar da al’ummar garin suna zaman zullumi biyo bayan harin bam na makon jiya. Sai dai ya samu damar tattauawa da wasu mutanen garin. Na farko, wani matashin dattijo, Alhaji Ahmed Adamu, mai shekara 50 da haihuwa.

Labarai Masu Nasaba

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

Ya bayyana cewa, “Kakanninmu a wannan garin aka haife su, haka iyayenmu da mu kanmu duk a wannan garin aka haife mu Amma ni tun da na taso ba mu taba samun Asibiti ba ko dakin shan magani wanda idan muna da mara lafiya babu abin da muke yi sai mu shiga jeji mu sama masa maganin gargajiya idan abin yaki sai mu je Buruku ko mu je Mando domin neman maganin Bature hatta cikin filin jiragen sama na Kaduna babu asibiti.

“Har gobe ba mu da wata hanyar sama wa yaranmu magani wanda ya wuce na gargajiya, idan jikin mara lafiyar bai yi zafi ba, haka nan za mu dauke shi rigin-rigin mu kai Mando ko Buruku domin samun maganin bature. Toh yanzu kila da aka samu wannan iftila’in, kila a gina mana makaranta ko Asibiti.” In ji shi.

Shi ma, Malam Adamu Umar, magidanci a garin na Tudun Biri ya shaida cewa “Ba ma kwadayin barin wannan gari saboda kankanninmu a nan aka haife su saboda idan mun bar garin mutuwa zai yi, haka kuma idan mun bar shi to ina za mu?

“Mun sha kai kokenmu ga gwamnati amma ba a taba waiwayen mu ba saboda ga shi kun zo kun ga yadda garin yake da idonku.

“Ba mu da wutar lantarki; ba mu da hanya ba mu da da makaranta. Mu fa yanzu ta kai ba ma ta wutar lantarki muke ba, mu samu hanyar da za mu rinka bi da makarantun da za mu kai ‘ya’yanmu shi ne muka fi so, yanzu haka ‘ya’yanmu suke tashi babu makaranta. Idan ka ga yaro ya samu ilimi a wannan garin sai dai idan mahaifiyarshi za ta tashi da asuba ta dora masa ruwan wanka sannan a lallaba da shi a mashin rugu-rugu a je a kai shi makaranta a cikin gari, idan aka tashi a dawo da shi.” In ji shi.

Har ila yau, LEADERSHIP HAUSA ta zanta da wasu yaran kauyen da ba su wuce shekaru 12 zuwa 15 ba da haihuwa, inda suka bayyana takaicinsu na rashin zuwa makarantar boko ba duk da cewa tana ba su sha’awa.
Daya daga cikinsu, Umar dan shekara 12 ya ce a halin yanzu makarantar ta kara yi masa nisa saboda “ Babana ya rasu, su kuma duk yayuna an kashe su a wannan abin da ya faru. Babu wanda zai kai ni makaranta.”

Shi ma wani yaro, Muhammadu Jibril ya bayyana cewa, “Ba na zuwa makaranta amma dai na yi tunanin zan fara zuwa sai kuma wannan abun ya faru a garin.”

LEADERSHIP Hausa ta gano cewa,mafi yawan yaran da suke zuwa aikin gona a garin matasa ne wadanda ba su wuce shekaru 12 zuwa 18 kuma duk ba sa zuwa makarantar boko.
Sun nuna takaicinsu a kan yadda ba sa ganin wasu jami’an gwamnati ko ‘yan siyasa sai lokacin zabe kana suka yi kiran a kawo musu daukin gaggawa.

Wani magidanci, Malam Muhammadu Hamisu Aminu, ya yi kira ga musamman Gwamnatin Tarayya ta samar musu da tsaro a garin inda ya bayyana cewa bayan wannan harin bam da ya jefa su cikin alhini, har yanzu suna da fargabar rashin tsaro a yankin.

Wani abin da aka lura da shi har ila yau a garin na Tudun Biri dai, bayan aukuwar iftila’in harin na bam, kusan duk matan garin da tsofaffi da matasa sun sauya shigarsu inda suke sa tufafi masu kyau mata kuma na amfani da sabbin hijabai.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Harin BamSojojin NijeriyaYan bindiga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Da Gangan Aka Cire Aikin Mambilla A Kasafin 2024 – Ministan Lantarki

Next Post

2027: PDP Ba Za Ta Tsayar Da Dan Arewa Takarar Shugaban Kasa Ba – George

Related

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

2 hours ago
Tudun Biri
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

2 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

3 hours ago
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

6 hours ago
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC
Labarai

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

9 hours ago
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi
Labarai

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

10 hours ago
Next Post
PDP

2027: PDP Ba Za Ta Tsayar Da Dan Arewa Takarar Shugaban Kasa Ba – George

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Tudun Biri

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.