ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tudun Biri: Garin Harin Bam, Ya Shekara Fiye Da 200 Babu Asibiti Da Makarantar Boko

by Shehu Yahaya
2 years ago
Tudun Biri
  • Ba Ma Ganin ‘Yan Siyasa Sai Lokacin Zabe
  • Har Yanzu Muna Fuskantar Barazanar Tsaro, In Ji Mazauna Garin

Garin Tudun Biri, da ke Gundumar Afaka a Karamar Hukumar Igabi da ke jihar Kaduna, wanda ya karade kafafen yada labarai tun daga makon jiya saboda harim bam da sojoji suka kai, gari ne da ya kwashe fiye da shekaru 200 da kafuwa ba tare da samun asibiti ko makarantar boko ba.

Gari ne na manoma da ya kunshi Zallar Hausawa da tsirarun gwarawa mai makwabtaka da filin sauka da tashin jiragen sama na Kaduna amma abin mamaki garin duk da kasancewarsa mafi kusa da filin jiragen saman na Kaduna amma babu abubuwan more rayuwa.

  • Gwamnatin Kano Za Ta Biya Wadanda Ta Yi Wa Rusau Diyyar N3bn
  • Al’ummar Tudun Biri Sun Kai Karar Gwamnatin Tarayya Kan Biyan Su Diyya

Wani Dattijo mai shekara 74 a duniya, ya shaida wa wakilinmu cewa, Tudun Biri gari ne mai tsohon tarihi domin hatta kakansa ma a nan aka haife shi, sannan suna zaman lafiya a tsakanin Hausawa da Gwarawa da kuma Fulani da ke yankin.

ADVERTISEMENT

A wata ziyara da Wakilinmu ya kai garin, wani matashi ya dauke a babur inda suka kewaya garin tare da ganin yadda mazauna kauyen ke rayuwa babu asibiti ko da sha-ka-ta-fi, wutar lantarki ko makarantar boko, duk da cewa suna taka rawar gani wajen zaben shugabanni lokacin zabe.

Duk da cewa galibin mutanen Tudun Biri manoma ne amma ba su da hanyar da idan sun girbe amfanin gona za su fitar zuwa kasuwa ga kuma matsalar rashin tsaro na ‘yan bindiga da suke musu barazana.
Wakilinmu ya tarar da al’ummar garin suna zaman zullumi biyo bayan harin bam na makon jiya. Sai dai ya samu damar tattauawa da wasu mutanen garin. Na farko, wani matashin dattijo, Alhaji Ahmed Adamu, mai shekara 50 da haihuwa.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Ya bayyana cewa, “Kakanninmu a wannan garin aka haife su, haka iyayenmu da mu kanmu duk a wannan garin aka haife mu Amma ni tun da na taso ba mu taba samun Asibiti ba ko dakin shan magani wanda idan muna da mara lafiya babu abin da muke yi sai mu shiga jeji mu sama masa maganin gargajiya idan abin yaki sai mu je Buruku ko mu je Mando domin neman maganin Bature hatta cikin filin jiragen sama na Kaduna babu asibiti.

“Har gobe ba mu da wata hanyar sama wa yaranmu magani wanda ya wuce na gargajiya, idan jikin mara lafiyar bai yi zafi ba, haka nan za mu dauke shi rigin-rigin mu kai Mando ko Buruku domin samun maganin bature. Toh yanzu kila da aka samu wannan iftila’in, kila a gina mana makaranta ko Asibiti.” In ji shi.

Shi ma, Malam Adamu Umar, magidanci a garin na Tudun Biri ya shaida cewa “Ba ma kwadayin barin wannan gari saboda kankanninmu a nan aka haife su saboda idan mun bar garin mutuwa zai yi, haka kuma idan mun bar shi to ina za mu?

“Mun sha kai kokenmu ga gwamnati amma ba a taba waiwayen mu ba saboda ga shi kun zo kun ga yadda garin yake da idonku.

“Ba mu da wutar lantarki; ba mu da hanya ba mu da da makaranta. Mu fa yanzu ta kai ba ma ta wutar lantarki muke ba, mu samu hanyar da za mu rinka bi da makarantun da za mu kai ‘ya’yanmu shi ne muka fi so, yanzu haka ‘ya’yanmu suke tashi babu makaranta. Idan ka ga yaro ya samu ilimi a wannan garin sai dai idan mahaifiyarshi za ta tashi da asuba ta dora masa ruwan wanka sannan a lallaba da shi a mashin rugu-rugu a je a kai shi makaranta a cikin gari, idan aka tashi a dawo da shi.” In ji shi.

Har ila yau, LEADERSHIP HAUSA ta zanta da wasu yaran kauyen da ba su wuce shekaru 12 zuwa 15 ba da haihuwa, inda suka bayyana takaicinsu na rashin zuwa makarantar boko ba duk da cewa tana ba su sha’awa.
Daya daga cikinsu, Umar dan shekara 12 ya ce a halin yanzu makarantar ta kara yi masa nisa saboda “ Babana ya rasu, su kuma duk yayuna an kashe su a wannan abin da ya faru. Babu wanda zai kai ni makaranta.”

Shi ma wani yaro, Muhammadu Jibril ya bayyana cewa, “Ba na zuwa makaranta amma dai na yi tunanin zan fara zuwa sai kuma wannan abun ya faru a garin.”

LEADERSHIP Hausa ta gano cewa,mafi yawan yaran da suke zuwa aikin gona a garin matasa ne wadanda ba su wuce shekaru 12 zuwa 18 kuma duk ba sa zuwa makarantar boko.
Sun nuna takaicinsu a kan yadda ba sa ganin wasu jami’an gwamnati ko ‘yan siyasa sai lokacin zabe kana suka yi kiran a kawo musu daukin gaggawa.

Wani magidanci, Malam Muhammadu Hamisu Aminu, ya yi kira ga musamman Gwamnatin Tarayya ta samar musu da tsaro a garin inda ya bayyana cewa bayan wannan harin bam da ya jefa su cikin alhini, har yanzu suna da fargabar rashin tsaro a yankin.

Wani abin da aka lura da shi har ila yau a garin na Tudun Biri dai, bayan aukuwar iftila’in harin na bam, kusan duk matan garin da tsofaffi da matasa sun sauya shigarsu inda suke sa tufafi masu kyau mata kuma na amfani da sabbin hijabai.

Tudun Biri
Shehu Yahaya
+ postsBio
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Bayan Shehu Sani Ya Ƙalubalanci Zailani, Rikicin APC Ya Ƙara Zafi A Kaduna
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Ya Dace ‘Yan Arewa Su Ƙara Marawa Tinubu Baya Domin Kammala Wa’adi Na Biyu — Shehu Sani
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Zargin Ware Ɓangaren El-rufa’i: Rikicin Cikin Gida Ya Kaure A Jam’iyyar ADC, Kaduna

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
PDP

2027: PDP Ba Za Ta Tsayar Da Dan Arewa Takarar Shugaban Kasa Ba – George

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.