ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tudun Biri: Garin Harin Bam, Ya Shekara Fiye Da 200 Babu Asibiti Da Makarantar Boko

by Shehu Yahaya
3 years ago
Tudun Biri
  • Ba Ma Ganin ‘Yan Siyasa Sai Lokacin Zabe
  • Har Yanzu Muna Fuskantar Barazanar Tsaro, In Ji Mazauna Garin

Garin Tudun Biri, da ke Gundumar Afaka a Karamar Hukumar Igabi da ke jihar Kaduna, wanda ya karade kafafen yada labarai tun daga makon jiya saboda harim bam da sojoji suka kai, gari ne da ya kwashe fiye da shekaru 200 da kafuwa ba tare da samun asibiti ko makarantar boko ba.

Gari ne na manoma da ya kunshi Zallar Hausawa da tsirarun gwarawa mai makwabtaka da filin sauka da tashin jiragen sama na Kaduna amma abin mamaki garin duk da kasancewarsa mafi kusa da filin jiragen saman na Kaduna amma babu abubuwan more rayuwa.

  • Gwamnatin Kano Za Ta Biya Wadanda Ta Yi Wa Rusau Diyyar N3bn
  • Al’ummar Tudun Biri Sun Kai Karar Gwamnatin Tarayya Kan Biyan Su Diyya

Wani Dattijo mai shekara 74 a duniya, ya shaida wa wakilinmu cewa, Tudun Biri gari ne mai tsohon tarihi domin hatta kakansa ma a nan aka haife shi, sannan suna zaman lafiya a tsakanin Hausawa da Gwarawa da kuma Fulani da ke yankin.

ADVERTISEMENT

A wata ziyara da Wakilinmu ya kai garin, wani matashi ya dauke a babur inda suka kewaya garin tare da ganin yadda mazauna kauyen ke rayuwa babu asibiti ko da sha-ka-ta-fi, wutar lantarki ko makarantar boko, duk da cewa suna taka rawar gani wajen zaben shugabanni lokacin zabe.

Duk da cewa galibin mutanen Tudun Biri manoma ne amma ba su da hanyar da idan sun girbe amfanin gona za su fitar zuwa kasuwa ga kuma matsalar rashin tsaro na ‘yan bindiga da suke musu barazana.
Wakilinmu ya tarar da al’ummar garin suna zaman zullumi biyo bayan harin bam na makon jiya. Sai dai ya samu damar tattauawa da wasu mutanen garin. Na farko, wani matashin dattijo, Alhaji Ahmed Adamu, mai shekara 50 da haihuwa.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

Ya bayyana cewa, “Kakanninmu a wannan garin aka haife su, haka iyayenmu da mu kanmu duk a wannan garin aka haife mu Amma ni tun da na taso ba mu taba samun Asibiti ba ko dakin shan magani wanda idan muna da mara lafiya babu abin da muke yi sai mu shiga jeji mu sama masa maganin gargajiya idan abin yaki sai mu je Buruku ko mu je Mando domin neman maganin Bature hatta cikin filin jiragen sama na Kaduna babu asibiti.

“Har gobe ba mu da wata hanyar sama wa yaranmu magani wanda ya wuce na gargajiya, idan jikin mara lafiyar bai yi zafi ba, haka nan za mu dauke shi rigin-rigin mu kai Mando ko Buruku domin samun maganin bature. Toh yanzu kila da aka samu wannan iftila’in, kila a gina mana makaranta ko Asibiti.” In ji shi.

Shi ma, Malam Adamu Umar, magidanci a garin na Tudun Biri ya shaida cewa “Ba ma kwadayin barin wannan gari saboda kankanninmu a nan aka haife su saboda idan mun bar garin mutuwa zai yi, haka kuma idan mun bar shi to ina za mu?

“Mun sha kai kokenmu ga gwamnati amma ba a taba waiwayen mu ba saboda ga shi kun zo kun ga yadda garin yake da idonku.

“Ba mu da wutar lantarki; ba mu da hanya ba mu da da makaranta. Mu fa yanzu ta kai ba ma ta wutar lantarki muke ba, mu samu hanyar da za mu rinka bi da makarantun da za mu kai ‘ya’yanmu shi ne muka fi so, yanzu haka ‘ya’yanmu suke tashi babu makaranta. Idan ka ga yaro ya samu ilimi a wannan garin sai dai idan mahaifiyarshi za ta tashi da asuba ta dora masa ruwan wanka sannan a lallaba da shi a mashin rugu-rugu a je a kai shi makaranta a cikin gari, idan aka tashi a dawo da shi.” In ji shi.

Har ila yau, LEADERSHIP HAUSA ta zanta da wasu yaran kauyen da ba su wuce shekaru 12 zuwa 15 ba da haihuwa, inda suka bayyana takaicinsu na rashin zuwa makarantar boko ba duk da cewa tana ba su sha’awa.
Daya daga cikinsu, Umar dan shekara 12 ya ce a halin yanzu makarantar ta kara yi masa nisa saboda “ Babana ya rasu, su kuma duk yayuna an kashe su a wannan abin da ya faru. Babu wanda zai kai ni makaranta.”

Shi ma wani yaro, Muhammadu Jibril ya bayyana cewa, “Ba na zuwa makaranta amma dai na yi tunanin zan fara zuwa sai kuma wannan abun ya faru a garin.”

LEADERSHIP Hausa ta gano cewa,mafi yawan yaran da suke zuwa aikin gona a garin matasa ne wadanda ba su wuce shekaru 12 zuwa 18 kuma duk ba sa zuwa makarantar boko.
Sun nuna takaicinsu a kan yadda ba sa ganin wasu jami’an gwamnati ko ‘yan siyasa sai lokacin zabe kana suka yi kiran a kawo musu daukin gaggawa.

Wani magidanci, Malam Muhammadu Hamisu Aminu, ya yi kira ga musamman Gwamnatin Tarayya ta samar musu da tsaro a garin inda ya bayyana cewa bayan wannan harin bam da ya jefa su cikin alhini, har yanzu suna da fargabar rashin tsaro a yankin.

Wani abin da aka lura da shi har ila yau a garin na Tudun Biri dai, bayan aukuwar iftila’in harin na bam, kusan duk matan garin da tsofaffi da matasa sun sauya shigarsu inda suke sa tufafi masu kyau mata kuma na amfani da sabbin hijabai.

Tudun Biri
Shehu Yahaya
+ postsBio
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Gwamna Uba Sani Ya Yi Jimamin Rasuwar Dan Jarida Jafaru Yakubu Maitama
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Gwamnatin Kaduna Ta Fara Rabon Takin Zamani Kyauta Ga Manoma 150,000
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Zaka Iya Sayar da Takin Gwamnati Ka Sayawa Iyalinka Kaji — Imam Nuradden
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Rashin Tsaro: ACI Zata Kira Taron Gaggawa Na Masu Ruwa Da Tsaki A Kaduna

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
PDP

2027: PDP Ba Za Ta Tsayar Da Dan Arewa Takarar Shugaban Kasa Ba – George

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.