• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Gano Ciwon Ciki Da Ke Turnuke Sojojin Isra’ila A Gaza

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Kimiyya Da Fasahar Sadarwa
0
Ciwon Ciki

Conceptual illustration of human microbiome microbes.

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwayar cutar bakteriya ta shigella na bazuwa ne ta hanyar taba dagwalon bayan gida
Likitoci sun ce wasu a cikin dakarun sojin Isra’ila da ke fada a mamaye ta kasa a Gaza, suna fama da wani matsanancin ciwon ciki sanadin wata cuta da ake kira “shigella”.

Ana jin cutar na bazuwa ne sakamakon rashin yanayi mai tsafta da kuma abinci maras aminci a fagen yaki.
Likitoci da yawa a Rundunar Sojin Isra’ila sun ba da rahoton bullar matsananciyar cutar ciwon ciki tsakanin dakarun da ke Gaza, a cewar Dakta Tal Brosh, daraktan Sashen Cutuka masu Yaduwa a Asibitin Koyarwa na Jami’ar Assuta Ashdod.

  • Gwamnatin Kano Za Ta Biya Wadanda Ta Yi Wa Rusau Diyyar N3bn
  • Hatsarin Jirgin Ruwa Ya Yi Ajalin Mutane 2 A Adamawa

Ya ce ya gano suna fama da cutar da ake kira shigella ne. Sojojin Isra’ila mai yiwuwa sun kamu da cutar shigella ne daga abincin da dangi da abokan arziki ke aika musu
Ana kebe sojojin da suka kamu, sannan a mayar da su gida don yi musu magani.

Dr Broch ya ce “fayyataccen sanadi” guda da ya janyo barkewar cutar shi ne abincin da fararen hula ‘yan Isra’ila suka girka kuma aka aikawa dakaru a Gaza.

Ya ce mai yiwuwa ne abincin ya gurbata da kwayar cutar shigella, da sauran miyagun kwayoyin bakteriya, saboda rashin sanyaya abincin a lokacin da ake tafiya da shi ko kuma rashin dumamawa sosai kafin a ci.
“Da zarar sojoji sun kamu da gudawa, larurorin rashin tsafta masu alaka da fagen yaki kan haddasa yaduwar cutar daga mutum zuwa wani,” ya ce. Dakta Broch ya kara da cewa kamata ya yi a aika wa dakarun soji kayan abincin da kawai aka kyafe kamar abincin gwangwani da nau’o’in biskit da gyada da sauransu, kamar yadda BBC ta labarto.

Labarai Masu Nasaba

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)

Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet

Shigella nau’in kwayar cutar bakteriya ce. Kuma idan ta shiga cikin jiki, tana janyo wani ciwon ciki mai haddasa kashin jini mai suna “shigellosis”.

Mutanen da ke cikin halin rashin lafiya ko kuma wadanda garkuwar jikinsu ta yi rauni sanadin cutuka kamar cutar kanjamau, na iya jin jiki daga wadannan alamomin cuta tsawon lokaci.

Matukar ba a yi magani ba, cutar shigella na iya kawo tsananin rashin lafiya, kai har ma da mutuwa.
Hatsarin mutuwar musamman, ya fi yawa idan kwayoyin cutar bakteriya suka shiga hanyoyin jini.
A cewar Cibiyar Dakile Cutuka masu Yaduwa ta Amurka, shigella na bazuwa “cikin sauki” ta hanyar hulda kai tsaye ko a kaikaice da bayan gidan mutumin da ya kamu.

Cibiyar Dakile Cutuka masu Yaduwa ta Amurka ta kiyasin cewa ana samun mutane tsakanin miliyan 80 zuwa miliyan 165 da ke kamuwa da cutar duk shekara a fadin duniya, inda take haddasa mutuwar mutum 600,000.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: GazaHamasIsra'ila
ShareTweetSendShare
Previous Post

NFF Ta Kaddamar Da Sabon Filin Wasan Kwallon Kafa A Birnin Kebbi

Next Post

An Cimma Yarjejeniyar Sauyin Yanayi Mai Ma’anar Tarihi

Related

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)

2 months ago
Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet

3 months ago
Hanyoyin Kare Kanka Daga Damfara Ta Intanet
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Hanyoyin Kare Kanka Daga Damfara Ta Intanet

3 months ago
Yadda Za A Kare Yara Daga Barazanar Intanet
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Yadda Za A Kare Yara Daga Barazanar Intanet

4 months ago
Mantuwa Na Matukar Taimakon Rayuwar Mutane – Masani
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Mantuwa Na Matukar Taimakon Rayuwar Mutane – Masani

8 months ago
Yadda Na Kirkiro ‘Brain-chip’ Da Ke Dawo Wa Wadanda Aka Haifa Da Makanta Ganinsu – Elon Musk
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Yadda Na Kirkiro ‘Brain-chip’ Da Ke Dawo Wa Wadanda Aka Haifa Da Makanta Ganinsu – Elon Musk

8 months ago
Next Post
An Cimma Yarjejeniyar Sauyin Yanayi Mai Ma’anar Tarihi

An Cimma Yarjejeniyar Sauyin Yanayi Mai Ma’anar Tarihi

LABARAI MASU NASABA

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.