ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Gano Ciwon Ciki Da Ke Turnuke Sojojin Isra’ila A Gaza

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Ciwon Ciki

Conceptual illustration of human microbiome microbes.

Kwayar cutar bakteriya ta shigella na bazuwa ne ta hanyar taba dagwalon bayan gida
Likitoci sun ce wasu a cikin dakarun sojin Isra’ila da ke fada a mamaye ta kasa a Gaza, suna fama da wani matsanancin ciwon ciki sanadin wata cuta da ake kira “shigella”.

Ana jin cutar na bazuwa ne sakamakon rashin yanayi mai tsafta da kuma abinci maras aminci a fagen yaki.
Likitoci da yawa a Rundunar Sojin Isra’ila sun ba da rahoton bullar matsananciyar cutar ciwon ciki tsakanin dakarun da ke Gaza, a cewar Dakta Tal Brosh, daraktan Sashen Cutuka masu Yaduwa a Asibitin Koyarwa na Jami’ar Assuta Ashdod.

  • Gwamnatin Kano Za Ta Biya Wadanda Ta Yi Wa Rusau Diyyar N3bn
  • Hatsarin Jirgin Ruwa Ya Yi Ajalin Mutane 2 A Adamawa

Ya ce ya gano suna fama da cutar da ake kira shigella ne. Sojojin Isra’ila mai yiwuwa sun kamu da cutar shigella ne daga abincin da dangi da abokan arziki ke aika musu
Ana kebe sojojin da suka kamu, sannan a mayar da su gida don yi musu magani.

ADVERTISEMENT

Dr Broch ya ce “fayyataccen sanadi” guda da ya janyo barkewar cutar shi ne abincin da fararen hula ‘yan Isra’ila suka girka kuma aka aikawa dakaru a Gaza.

Ya ce mai yiwuwa ne abincin ya gurbata da kwayar cutar shigella, da sauran miyagun kwayoyin bakteriya, saboda rashin sanyaya abincin a lokacin da ake tafiya da shi ko kuma rashin dumamawa sosai kafin a ci.
“Da zarar sojoji sun kamu da gudawa, larurorin rashin tsafta masu alaka da fagen yaki kan haddasa yaduwar cutar daga mutum zuwa wani,” ya ce. Dakta Broch ya kara da cewa kamata ya yi a aika wa dakarun soji kayan abincin da kawai aka kyafe kamar abincin gwangwani da nau’o’in biskit da gyada da sauransu, kamar yadda BBC ta labarto.

LABARAI MASU NASABA

Zarewa Ta Ƙirƙiro Na’urar Gano Tsatsa Bayan Lashe Kyautar ‘Carbon Neutrality’ Ta Duniya

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

Shigella nau’in kwayar cutar bakteriya ce. Kuma idan ta shiga cikin jiki, tana janyo wani ciwon ciki mai haddasa kashin jini mai suna “shigellosis”.

Mutanen da ke cikin halin rashin lafiya ko kuma wadanda garkuwar jikinsu ta yi rauni sanadin cutuka kamar cutar kanjamau, na iya jin jiki daga wadannan alamomin cuta tsawon lokaci.

Matukar ba a yi magani ba, cutar shigella na iya kawo tsananin rashin lafiya, kai har ma da mutuwa.
Hatsarin mutuwar musamman, ya fi yawa idan kwayoyin cutar bakteriya suka shiga hanyoyin jini.
A cewar Cibiyar Dakile Cutuka masu Yaduwa ta Amurka, shigella na bazuwa “cikin sauki” ta hanyar hulda kai tsaye ko a kaikaice da bayan gidan mutumin da ya kamu.

Cibiyar Dakile Cutuka masu Yaduwa ta Amurka ta kiyasin cewa ana samun mutane tsakanin miliyan 80 zuwa miliyan 165 da ke kamuwa da cutar duk shekara a fadin duniya, inda take haddasa mutuwar mutum 600,000.

Ciwon Ciki
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

MASU ALAKA

Zarewa Ta Ƙirƙiro Na’urar Gano Tsatsa Bayan Lashe Kyautar ‘Carbon Neutrality’ Ta Duniya
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Zarewa Ta Ƙirƙiro Na’urar Gano Tsatsa Bayan Lashe Kyautar ‘Carbon Neutrality’ Ta Duniya

February 21, 2026
Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai
Da ɗumi-ɗuminsa

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

September 5, 2025
Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)

April 19, 2025
Next Post
An Cimma Yarjejeniyar Sauyin Yanayi Mai Ma’anar Tarihi

An Cimma Yarjejeniyar Sauyin Yanayi Mai Ma’anar Tarihi

LABARAI MASU NASABA

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.