• English
  • Business News
Sunday, August 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnonin Arewa Na Kokarin Farfado Da Hadin Kan Yankin

by Bello Hamza
2 years ago
in Labarai
0
Gwamnonin Arewa Na Kokarin Farfado Da Hadin Kan Yankin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnoni 19 na Arewacin Nijeriya a karkashin kungiyar gwamnonin arewa sun bayyana aniyarsu ta tabbatar da dunkulewar yankin domin cin cikakkiyar gajiyar albarkatun kasa da na al’umma da Allah ya shinfida a yankin.

A kan haka suka dawo da taken shugabanin yankin na farko suke yi ma yankin na “Kasa Daya Makoma Daya”. Hadin kai da aiki tare da zai taimaka wajen fuskantar dukkan kalubalen da yankin ke fuskanta. Gwamnonin sun kuma nemi a hada kai a fuskanci matsalar tsaron da ta addabi yankin.

Kiran Minista Ga VON: Ku Yaɗa Kyawawan Labarun Nijeriya Ga Duniya 

Gwamnati Ta Shirya Fatattakar ‘Yan Bindiga A Duk Inda Suke – Ministan Tsaro

Shugaban kungiyar gwamnonin arewa kuma Gamnan Jihar Gombe, Alhaji Muhammadu Inuwa Yahaya ya bayyana haka a taron da kungiyar ta gudanar a Kaduna a makon jiya.

Labarai Masu Nasaba

Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina

Sanata Shehu Buba Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Da Rigakafin Shanu A Bauchi

“Tabbatar da hadin kai shi ne mabudin ci gaban yankin Arewacin Nijeriya, za mu dawo da akidar Arewa Daya Makoma Daya kamar yadda iyayenmu suka shimfida don samar da cikakkiyar hadin kai da soyayyar juna ba tare nuna banbancin siyasa, kabilanci ko addini ba” in ji shi.

Shugaban kungiyar gwamnonin ya kuma yi kira ga ‘yan siyasa, sarakunan gargajiya, malaman addini da dukkan masu ruwa da tsaki su rungumi juna da nufin samar da ci gaban da ake bukata a sassa daban-daban na tattalin arzikin yankin.

Ya kuma ce, “A mastayimu na gwamnaonin yankin arewa 19 muna yaba wa yukurin gwamnatin tarayya na kokarin kawo karshen matsalar tsaron da ta addabi yankin musamman ayyukan masu garkuwa da mutane, da ayyukan ‘yan bindiga a sassan yankin”.

“Tsaro da ci gaban al’umma abu ne da suke tafiya tare in har babu tsaro to lalai babu ci gaba don masu zuba jari ba za su shigo ba har a samu ayyukan yi ga matasanmu.”

Ya kuma ce, ba za a samu damar gudanar da ayyukan hanyoyi da gadoji ba da sauran ayyukan raya kasa ba har sai an samu tsaro da zaman lafiya, da wannan ne manoman mu za su saki jiki su noma abincin da za a ciyar da Nijeriya.

A nasa jawabin, Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani ya lura da cewa, matsalar tsaro ta dade tana ci wa yankin arewa tuwo a kwarya, a kan haka ya nemi shugabanin yankin su hada kai tare da fito da dabaru iri daya wajen tunkarar matsalar tsaro bai-daya a yankin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Dalilinmu Na Karkata Ga Cin Bashin Cibiyoyin Kudi Na Musulunci – Ministan Kudi

Next Post

Wasanni Na Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Ci Gaban Matasa — Gidauniyar Bukola Saraki 

Related

Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina
Labarai

Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina

1 hour ago
Sanata Shehu Buba Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Da Rigakafin Shanu A Bauchi
Labarai

Sanata Shehu Buba Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Da Rigakafin Shanu A Bauchi

2 hours ago
Dangote Ya Ɗauki Nauyin Bikin Baje Kolin Gidajen Afrika Da Mahalarta Ƙasashe 21
Labarai

Dangote Ya Ɗauki Nauyin Bikin Baje Kolin Gidajen Afrika Da Mahalarta Ƙasashe 21

4 hours ago
Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci A Kwantar Da Hankali Kan Dakatar Da Gidan Rediyon Badeggi FM
Labarai

ADC Ta Yi Allah-wadai Da Rufe Gidan Rediyon Badeggi FM A Neja

9 hours ago
Gwamnatin Katsina Ta Gabatar Da Matsayarta A Taron Jin Ra’ayiyin Jama’a
Labarai

Gwamnatin Katsina Ta Gabatar Da Matsayarta A Taron Jin Ra’ayiyin Jama’a

10 hours ago
Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare
Manyan Labarai

Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare

11 hours ago
Next Post
Wasanni Na Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Ci Gaban Matasa — Gidauniyar Bukola Saraki 

Wasanni Na Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Ci Gaban Matasa — Gidauniyar Bukola Saraki 

LABARAI MASU NASABA

Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina

Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina

August 3, 2025
Sanata Shehu Buba Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Da Rigakafin Shanu A Bauchi

Sanata Shehu Buba Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Da Rigakafin Shanu A Bauchi

August 3, 2025
Waɗanne Ƙasashe Ne Suka Amince Da Kafa Ƙasar Falasɗinu?

Waɗanne Ƙasashe Ne Suka Amince Da Kafa Ƙasar Falasɗinu?

August 3, 2025
Dangote Ya Ɗauki Nauyin Bikin Baje Kolin Gidajen Afrika Da Mahalarta Ƙasashe 21

Dangote Ya Ɗauki Nauyin Bikin Baje Kolin Gidajen Afrika Da Mahalarta Ƙasashe 21

August 3, 2025
An Fara Bayar Da Hidimomin Da Suka Shafi Sauka Da Tashi Domin Gasar Wasanni Ta Duniya Ta Chengdu

An Fara Bayar Da Hidimomin Da Suka Shafi Sauka Da Tashi Domin Gasar Wasanni Ta Duniya Ta Chengdu

August 3, 2025
Rikici Ya Ɓarke A Zaɓen Ribas, Ƴan PDP Sun Fito A Matsayin Ƴan Takarar APC

Rikici Ya Ɓarke A Zaɓen Ribas, Ƴan PDP Sun Fito A Matsayin Ƴan Takarar APC

August 3, 2025
Ana Gaggauta Ayyukan Gyara Tituna Da Gadojin Da Ambaliya Ta Lalata A Arewacin Kasar Sin

Ana Gaggauta Ayyukan Gyara Tituna Da Gadojin Da Ambaliya Ta Lalata A Arewacin Kasar Sin

August 3, 2025
Shugabar Tanzania Ta Kaddamar Da Cibiyar Cinikayya Da Jigila Da Sin Ta Gina A Kasar

Shugabar Tanzania Ta Kaddamar Da Cibiyar Cinikayya Da Jigila Da Sin Ta Gina A Kasar

August 3, 2025
Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje

Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje

August 3, 2025
Amurka Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Zuwa Ƙasarta Domin Haihuwa

Amurka Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Zuwa Ƙasarta Domin Haihuwa

August 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.