ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kiran Minista Ga VON: Ku Yaɗa Kyawawan Labarun Nijeriya Ga Duniya 

by yahuzajere
3 years ago
minista

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya umarci gidan rediyon Muryar Nijeriya (VON) da ya maida hankali wajen yaɗa kyawawan labarai da shirye-shirye game da irin gudunmawar da Nijeriya ke bayarwa ga cigaban duniya.

Mataimakin Daraktan yaɗa labarai a ma’aikatar, Malam Suleiman Haruna, ya ruwaito a cikin sanarwa ga manema labarai da ya bayar cewa ministan ya yi wannan umurnin ne a lokacin da hukumar gudanarwa ta gidan rediyon ta kai masa ziyarar aiki a ofishin sa a Abuja a ranar Talata, 19 ga Disamba, 2023.

Ministan ya yi kira ga VON da ta isar da saƙon damarmakin da ke akwai, da haɗin gwiwa, da ingantuwar ƙasar Nijeriya ta yadda Nijeriya za ta ci moriyar Zuba Jari Kai-tsaye daga Waje.

ADVERTISEMENT

Ya ce idan an samar da kyakkyawan yanayin yin kasuwanci, to gwamnati za ta samun ƙarin ayyukan yi da kuma kuɗin shiga.

Ya ce: “Ku na da rawar da za ku taka wajen aikin sauya fasalin zamantakewa da gwamnatin Tinubu ta sanya a gaba a yanzu.

LABARAI MASU NASABA

CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

“Tilas ne ku riƙa isar da saƙon mu na ƙaruwar arziki da damarmakin da ke akwai, tare da jama’a ƙwararru a fannoni daban-daban don a jawo ra’ayin masu zuba jari da kuma masu yawon shaƙatawa zuwa Nijeriya.

  • Kafafen Yaɗa Labarai Ne Manyan Dirkokin Dimokraɗiyyarmu – Minista

 

“Nijeriya ta na kan hanyar ta ta samun martaba; tilas mu ƙarfafa gwiwar masu harkokin kasuwanci su shigo ciki a dama da su domin su amfana.”

Ministan ya ce ya na sane sosai da cewa sassa da dama na Nijeriya su na buƙatar a tallafa masu domin su shigo cikin wannan tsarin na sauya fasalin zamantakewa. Ya ce duk da hakan, gwamnatin ta na yin bakin ƙoƙarin ta domin magance matsaloli.

Akwai buƙatar gidan rediyon Muryar Nijeriya (VON) ya isar da wannan saƙon ga duniya, inji shi.

Tun da farko a nasa jawabin, sai da Darakta-Janar na Muryar Nijeriya, Alhaji Jibrin Baba Ndace, ya bayyana cewa hukumar gudanarwa da ma’aikatan gidan rediyon sun kawo ziyarar ne domin su sanar da ministan irin tsarin aiki da su ka fito da shi kuma su shaida masa cewa su na bin dukkan tsare-tsaren gwamnatin Tinubu sosai da sosai.

Darakta-Janar ɗin ya ba ministan tabbacin cewa duk da yake su na watsa shirye-shirye cikin harsunan ƙasashen waje guda huɗu ne, yanzu su na da burin su faɗaɗa zuwa harsunan wasu manyan ƙasashen irin su Chaina da Indiya, waɗanda su na gudanar da harkokin kasuwanci a Nijeriya.

minista
yahuzajere
+ postsBio
  • yahuzajere
    Da Kujerar Mulki Gara Zaman Lafiyar Kano
  • yahuzajere
    Ya Kamata Amurka Ta San Ana Barin Halal Don Kunya
  • yahuzajere
    Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Ga Gwamnatin Tarayya A Kan Tozarta Marasa Lafiya Daga Jami’an FIRS A Kano
  • yahuzajere
    Sin Ta Kaddamar Da Gagarumin Bikin Ba Da Lambobin Yabo Na Kasar Sin

MASU ALAKA

CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036
Labarai

CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

July 4, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026
Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

July 4, 2026
Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina
Labarai

Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

July 4, 2026
Next Post
Majalisar Dokokin Sokoto Ta Amince Da Bukatar Gwamna Aliyu Na Kafa Jami’an Tsaron Jiha

Majalisar Dokokin Sokoto Ta Amince Da Bukatar Gwamna Aliyu Na Kafa Jami’an Tsaron Jiha

LABARAI MASU NASABA

Dakarun Tsaron Teku Na Sin Na Ci Gaba Da Sintirin Wanzar Da Doka A Yankunan Ruwa Na Gabashin Tsibirin Taiwan

Dakarun Tsaron Teku Na Sin Na Ci Gaba Da Sintirin Wanzar Da Doka A Yankunan Ruwa Na Gabashin Tsibirin Taiwan

July 4, 2026
Wasu Matasa Amurkawa Sun Ziyarci Sin Don Kara Fahimtar Kasar

Wasu Matasa Amurkawa Sun Ziyarci Sin Don Kara Fahimtar Kasar

July 4, 2026
Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu

Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu

July 4, 2026
CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

July 4, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

July 4, 2026
Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

July 4, 2026
Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

July 4, 2026
Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

July 4, 2026
Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

July 4, 2026
Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

July 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.