• English
  • Business News
Wednesday, October 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kirismeti: Kukah Ya Bukaci Tinubu Ya Kawo Karshen Kisan Al’umma

by Sulaiman and Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
2 years ago
Kukah

Shugaban Cocin Katolika na Sakkwato, Mathiew Kukah ya bukaci Shugaba Bola Tinubu da ya samar da tabbataccen mataki mai dorewa na kawo karshen kashe-kashen al’umma da ya zama ruwan dare, inda ya ce, “Ubangiji ba zai yafe masa ba idan ya kasa sauke nauyin da ke kan sa”.

Kukah a sakonsa na bikin Kirismeti da ya raba wa manema labarai a ranar Litinin, ya bayyana cewa, Shugaban Kasa Tinubu, a matsayinsa na jagora, ya dace ya yi amfani da kwarewa da gogewarsa wajen kawo karshen rikice-rikicen da suka addabi al’ummar kasa na daga bambancin addini, kabilanci ko na yanki.

  • Na Yi Iya Bakin Ƙokarina Lokacin Da Nake Riƙe Da Shugabancin Nijeriya — IBB
  • Wadanda Suka Jikkata Yayin Girgizar Kasa A Kasar Sin Sun Samu Kulawar Da Ta Dace

Ya kuma yi magana kan zaben 2023 da sakamakon da ya biyo baya tare da kira ga shugabanni da su dauki matakin daidaita al’amurra a cikin matakin gaggawa. Ya ce shekaru kadan da suka gabata tamkar gwaji ne kan hadin kan kasa da dorewarta.

“Mai girma Shugaban Kasa, a yanzu ka samu abin da ka nema kuma kake mafalki, wanda ka jima ka na muradi. A sama da shekaru 20 ka daura damarar zama Shugaban Kasa, ka yi yekuwar neman zaben kafa sabuwar Nijeriya ta hanyar canza fasalin kasa, a tsawon shekaru, ka yi gwagwarmayar kafa Dimokuradiyya ta hanyar yaki da mulkin soji, don haka a yanzu lokaci ya yi da za ka kawo karshen matsalolin al’umma.

“A yanzu kai ne matuki a gidan gaba, a karkashin ikonka, wajibi ne Nijeriya ta dawo saman turba, a bisa ga jagorancinka, ya zama dole mu kawo karshen rikice-rikicen addini, kabilanci da na yanki. Ka samu cikakken lokacin tunanin amsa tambayoyin al’umma wadanda ke kukan samun amsa. A yanzu makomar ka da ta ‘yan kasa ta na a hannunka.” In ji shi.

LABARAI MASU NASABA

Afuwar Tinubu Ga Fursunoni: Saura Ƙasa Da Shekaru 6 Maryam Sanda Ta Shaƙi Iskar ‘Yanci

Ba Matakan Tinubu Ne Suka Karyar Da Farashin Kayan Abinci Ba – ADC

Kukah ya bayyana cewar Tinubu ba ya da kowane irin uzuri a wajen ubangiji ko ga al’umma, ya ce ubangiji ko tarihi ba za su taba yi masa afuwa ba idan ya kasa sauke nauyi, don haka, a yanzu dukkanin idanu da kunnuwa suna a kansa.

Kukah ya kara da cewa, suna yi masa addu’ar samun kasa mai cike da hadin kai.

“Mun ga wasu matakan farko na tsare-tsare wadanda suka haifar da rudani, fargaba da yabo wanda abin da aka yi tsammani ne. Muna fatan ganin alkawalin sauyi da ka yi mana.” Kukah ya bayyana.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Afuwar Tinubu Ga Fursunoni: Saura Ƙasa Da Shekaru 6 Maryam Sanda Ta Shaƙi Iskar ‘Yanci
Manyan Labarai

Afuwar Tinubu Ga Fursunoni: Saura Ƙasa Da Shekaru 6 Maryam Sanda Ta Shaƙi Iskar ‘Yanci

October 29, 2025
ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa
Manyan Labarai

Ba Matakan Tinubu Ne Suka Karyar Da Farashin Kayan Abinci Ba – ADC

October 29, 2025
‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa
Manyan Labarai

‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa

October 29, 2025
Next Post
An Wallafa Littafin Xi Jinping Game Da BRI Bugun Shekarar 2023

An Wallafa Littafin Xi Jinping Game Da BRI Bugun Shekarar 2023

LABARAI MASU NASABA

Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro

Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro

October 29, 2025
An Yi Taron Tataunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Moscow, Manama, Da Budapest

An Yi Taron Tataunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Moscow, Manama, Da Budapest

October 29, 2025
majalisar kasa

Majalisar Wakilai Ta Amince Da Bukatar Amso Bashin Dala Biliyan 2.34 A Kasuwar Jari Ta Duniya

October 29, 2025
An Samu Ingantuwar Yanayin Iska Da Ruwa Cikin Watanni 9 Na Farkon Bana A Sin

An Samu Ingantuwar Yanayin Iska Da Ruwa Cikin Watanni 9 Na Farkon Bana A Sin

October 29, 2025
Kotu Ta Umarci Ƙwace Dala 49,700 Daga Tsohon Jami’in INEC

Kotu Ta Umarci Ƙwace Dala 49,700 Daga Tsohon Jami’in INEC

October 29, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kara Kyautata Tsarin Kare Muradun Al’umma A Bangaren Shari’a

Yadda Kasar Sin Ke Kara Kyautata Tsarin Kare Muradun Al’umma A Bangaren Shari’a

October 29, 2025
COAS Shaibu Ya Sha Alwashin Murƙushe ‘Yan Ta’addar Lakurawa 

COAS Shaibu Ya Sha Alwashin Murƙushe ‘Yan Ta’addar Lakurawa 

October 29, 2025
Binciken ‘Yan Sanda Kan Wanda Ake Zargi Da Tawayen “‘Yancin Kan Taiwan” Mataki Ne Na Adalci Don Kare Hadin Kan Kasa

Binciken ‘Yan Sanda Kan Wanda Ake Zargi Da Tawayen “‘Yancin Kan Taiwan” Mataki Ne Na Adalci Don Kare Hadin Kan Kasa

October 29, 2025
Afuwar Tinubu Ga Fursunoni: Saura Ƙasa Da Shekaru 6 Maryam Sanda Ta Shaƙi Iskar ‘Yanci

Afuwar Tinubu Ga Fursunoni: Saura Ƙasa Da Shekaru 6 Maryam Sanda Ta Shaƙi Iskar ‘Yanci

October 29, 2025
Xi Jinping Zai Gana Da Donald Trump

Xi Jinping Zai Gana Da Donald Trump

October 29, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.