ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro

by Sulaiman
8 months ago
Sulhu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya gargaɗi shugabanni da hukumomin tsaro da su guji tattaunawa da ƙungiyoyi masu ɗauke da makamai idan har za a bar su da makaman nasu, yana mai cewa irin wannan salon sulhu ba ya kawo zaman lafiya, sai dai ya ƙara tashin hankali tare da raunana ikon gwamnati.

 

Gwamnan ya yi wannan jawabi ne a matsayin babban baƙo mai gabatar da lacca ga mahalarta taron Executive Intelligence Management Course (EIMC) na 18 a Cibiyar Nazarin Tsaro ta Ƙasa (NISS) da ke Abuja, ranar Laraba.

ADVERTISEMENT
  • COAS Shaibu Ya Sha Alwashin Murƙushe ‘Yan Ta’addar Lakurawa 
  • Afuwar Tinubu Ga Fursunoni: Saura Ƙasa Da Shekaru 6 Maryam Sanda Ta Shaƙi Iskar ‘Yanci

A cewar wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, taken laccar shi ne: “Rawar ’Yan Faɗa-da-Gwamnati a Harkokin Tsaro: Ƙalubale da Damar Zaman Lafiya da Ci Gaban Afrika – Salon Zamfara.”

 

LABARAI MASU NASABA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

An bayyana cewa mahalartan EIMC 18 sun fito ne daga hukumomin tsaron Nijeriya da kuma ƙasashen Afrika kamar Chadi, Ghana, Rwanda, Somalia, da Gambiya.

 

A cikin laccarsa, Gwamna Lawal ya bayyana cewa salon Zamfara ta zama abin koyi ga sauran sassan Afrika wajen nazarin yadda ake ƙoƙarin samar da zaman lafiya da ci gaba.

 

Ya ce, “A cikin shekaru 20 da suka wuce, tsarin tsaro a Afrika ya sauya sosai. Ra’ayin cewa gwamnati ita kaɗai ke da ikon amfani da ƙarfi yanzu ya fara fuskantar kalubale daga ƙungiyoyi marasa bin tsarin gwamnati – ciki har da ‘yan sa-kai, ƙungiyoyin kare kai, ‘yan ta’adda, barayin daji da kuma cibiyoyin aikata laifuka na ƙasa da ƙasa.”

 

Gwamnan ya bayyana cewa matsalolin tsaro a Zamfara sun samo asali ne daga rashin aikin yi, taƙaddamar albarkatun ƙasa, da canjin yanayi, tare da yawaitar makamai daga rikice-rikicen yankuna.

 

Ya ce, tun da suka hau mulki a 2023, gwamnatinsa ta mayar da hankali wajen kafa tsaro bisa ginshiƙai uku:

 

1. Haɗin gwiwar hukumomin tsaro ƙarƙashin kwamitin tsaro na jiha da gwamnan kansa ke jagoranta.

 

2. Ƙirƙirar Rundunar Kare Al’umma ta ‘Community Protection Guards’ (CPG) domin tallafawa jami’an tsaro.

 

3. Haɗa kai tsakanin sarakunan gargajiya, ƙananan hukumomi da hukumomin tsaro wajen raba bayanan sirri da saurin ɗaukar mataki kan barazanar tsaro.

 

Ya ƙara da cewa, an kafa kwamitocin sulhu a kowace ƙaramar hukuma da suka haɗa da sarakuna, malamai, mata da matasa domin sulhunta rikice-rikice da gina aminci.

 

Gwamnan ya ce, Zamfara na aiki tare da ofishin mai ba da shawara kan harkokin tsaro na ƙasa da kuma ƙasashen ƙetare kamar Kolombiya wajen shirin Preventing and Countering Violent Extremism (PCVE) — wanda ke mayar da hankali kan shirin gyarawa da dawo da masu tubabbun ‘yan ta’adda cikin al’umma.

 

A cewarsa, “Tattaunawar sulhu na iya taimaka wajen magance rikici, amma zaman lafiya na gaskiya ba zai samu ba sai an ajiye makamai. Sulhu ba tare da iko ba dai-dai yake da miƙa wuya gare su. Barin masu bindiga da makamai yayin da ake tsara sharuɗɗan zaman lafiya hanya ce ta sake janyo tashin hankali.”

 

Gwamna Lawal ya jaddada cewa duk wani yunƙurin sulhu dole ne ya zama mai tsari, ƙarƙashin jagorancin gwamnati, tare da cikakken iko na doka. “Zaman lafiya na gaskiya yana samuwa ne idan masu ɗauke da makamai sun amince da mulkin doka, kuma gwamnati ta tabbatar tana da ƙarfin kare jama’arta.”

 

A nasa jawabin, Kwamandan Cibiyar Tsaro ta Ƙasa, J.O. Odama (FSI+, FDC), ya yaba wa Gwamna Lawal bisa hangen nesan da ya gabatar, yana mai cewa, “Ya kawo mana cikakken haske kan gaskiyar lamura a Zamfara. Na tashi a can, na san irin ƙalubalen da ya fuskanta kafin ya zama gwamna. Amma yanzu ya sauya fasalin jihar daga fuskar rashin tsaro zuwa canjin na gaskiya da kyakkyawan fata ga al’umma.”

Sulhu
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya
  • Sulaiman
    Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari
  • Sulaiman
    Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana
  • Sulaiman
    Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

MASU ALAKA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF
Rahotonni

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin
Rahotonni

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026
Labarai

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
Next Post
Sabon Ingantaccen Hadin Gwiwar “Sin-ASEAN 3.0″ Ya Kafa Sabon Misali Na Hadin Kan Yanki

Sabon Ingantaccen Hadin Gwiwar “Sin-ASEAN 3.0" Ya Kafa Sabon Misali Na Hadin Kan Yanki

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.