Da karfe 9 na safiyar Litinin din nan ne kasar Sin ta yi nasarar harba wasu taurarin dan Adam guda 4, na binciken yanayi zuwa samaniya, daga cibiyar harba kumbuna ta Jiuquan dake arewa maso yammacin kasar.
Taurarin dan Adam din, na cikin rukunin Tianmu-1 na binciken yanayi, an kuma harba su ne ta amfani da rokar Kuaizhou-1A, kuma sun shiga falakin su cikin nasara.
Muhimmin aikin su shi ne samar da nau’o’in bayanai, don hidimomin hasashen yanayi na kasuwanci. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp