ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, November 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Ta Shafe Shekaru 60 Tana Aikewa Da Ma’aikatan Agajin Jinya Zuwa Kasashen Waje

by Sulaiman
2 years ago
Sin

A farkon shekarun 1960, ba da jimawa ba da kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Kasar Sin, wadda ke bukatar ci gaba, kuma ba ta da arziki sosai. Amma a lokacin, kasar Aljeriya da ta samu ‘yanci bada dadewa ba, ta yi kira ga sassan kasa da kasa ta kungiyar bada agaji ta Red Cross ta duniya, da su samar mata da tallafin jinya na gaggawa. Sin ce kasa ta farko da ta fito fili ta sanar da tura kwararrun likitocinta zuwa Aljeriya. Watakila kasashen duniya ba su taba tsammanin cewa, kasar Sin za ta shafe tsawon shekaru 60 tana gudanar da wannan aiki ba.

Nasarorin da kasar Sin ta samu cikin shekaru 60 a fannin samar da agajin jinya ga kasashen waje, sun baiwa dukkanin duniya zarafin fahimtar nauyin dake wuyan kasar. Sin kasa ce daya kadai a duk fadin duniya, da ke tsayawa wajen aikewa da tawagogin ma’aikatan agajin jinya zuwa kasashe masu tasowa cikin dogon lokaci.

  • Shugabannin Sin Sun Kalli Wasan Gargajiya Na Opera Domin Maraba Da Sabuwar Shekarar 2024
  • Samar Da Tsaro: Ribadu Ya Yaba Wa Sarakunan Gargajiya A Adamawa

Kawo yanzu, kasar Sin ta riga ta tura ma’aikatan samar da agajin jinya sama da dubu 30 zuwa kasashe da yankuna 76, da bada tallafin gina cibiyoyin likitanci da kiwon lafiya sama da 130, kuma adadin marasa lafiyar da likitocin kasar Sin suka kula da su ya tasam ma miliyan 300.

ADVERTISEMENT

Bugu da kari, ma’aikatan samar da agajin jinya na kasar Sin suna himmatuwa wajen fadada ayyukan da suke yi a kasashen waje, musamman a wadannan shekaru 10, tun bayan da kasar ta bullo da ra’ayin gina al’umma mai kyakkyawar makoma ta bai daya a fannin kiwon lafiya, ayyukan likitocin kasar Sin sun fadada daga ceton rayuka da kulawa da marasa lafiya, har zuwa taimakawa kasashe wajen inganta tsarin kiwon lafiya, da karfafa kwarewarsu wajen samar da hidimomin kiwon lafiya. Wato daga samar da agaji, har zuwa inganta hadin-gwiwa mai dorewa, kasar Sin tana kokarin marawa kasashe daban-daban baya, don samun babban ci gaba.

Kasar Sin na kokarin zamanantar da kanta a halin yanzu, kuma a matsayinta na kasa mai tasowa mafi girma a duniya, a yayin da take raya kanta, tana kuma tsayawa ga taimakawa zamanantar da sauran kasashe.

LABARAI MASU NASABA

Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

Tsawon shekaru 60 ba karshe ne ba, akasin haka, sabon mafari ne. (Murtala Zhang)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku
Daga Birnin Sin

Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

November 16, 2025
Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta
Daga Birnin Sin

Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

November 16, 2025
An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing
Daga Birnin Sin

An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

November 16, 2025
Next Post
Dabarun Gyaran Gashin Kai A Gida

Dabarun Gyaran Gashin Kai A Gida

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

November 16, 2025
Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

November 16, 2025
Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

November 16, 2025
An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

November 16, 2025
Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

November 16, 2025
Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

November 16, 2025
DSS

Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato

November 16, 2025
ECOWAS

A Zamanantar Da Tsarin Karatu A Makarantun Koyar Da Ilimin Addinin Musulunci – ECOWAS

November 16, 2025
APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

November 16, 2025
Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya

Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya

November 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.