ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya

by Rabilu Sanusi Bena and Sulaiman
7 months ago
Firimiyar Nijeriya

A ‘Yan kwanakin nan, kwamitin ladabtarwa na Gasar Firimiyar Nijeriya (NPFL) ta hukunta kungiyar kwallon kafa ta Katsina United bayan abinda ta kira rashin samar da jami’an tsaro a wasan da ta karbi bakuncin takwararta ta Barau Fc a wasan Mako na 12 na Gasar Firimiyar Nijeriya da suka buga a filin wasa na Muhammad Dikko dake birnin Katsina.

 

Kafin hukuncin na Katsina, kwamitin ya kuma hukunta kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars kwatankwacin hukuncin da ta yi wa Katsina United da ya hada da biyan tarar Naira miliyan 9 da kuma dakatar da wasanni a filin wasanta na Sani Abacha dake Kofar Mata a birnin Kano, hakan ya janyo cece-kuce a tsakanin masu sha’awar kallon wasan kwallon kafa musamman. a jihohin da abin ya shafa na Katsina da Kano.

ADVERTISEMENT

 

A yau Leadership Hausa ta zakulo maku wasu hanyoyin da ka iya takaita yawaitar fadace-fadace yayin buga wasannin Firimiyar Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

 

Amfani da jami’an tsaro:

Abu na farko dai dole ne kungiyoyi su yi aiki tare da yansanda, NSCDC, da jami’an tsaro na sirri wajen tsara tsare-tsaren tsaro a ranar da za su buga wasa, domin kuwa Bahaushe na cewa, “tun za a, ake shiri ba sai an dawo ba”, hakazalika yana da mahimmanci a tura isassun masu aikin kwantar da tarzoma (ba yansanda kawai ba) don sa ido kan magoya baya, lura da wuraren shiga/fita, da kuma taimakawa wajen rage turmutsitsi yayin wasa.

 

Amfani da CCTV:

Yawancin filayen wasa na gasar NPFL ba su da isasshen tsarin kyamarar CCTV, a cikin filayensu cewar bincike, samar da kyamarori masu sa ido na iya rage tashin hankali a cikin filayen wasa domin idan an ga wani motsi da ba a yarda dashi ba sai akai dauki da wuri.

 

Shingaye:

A tabbatar da cewa akwai shingen tsaro tsakanin yan kallo da cikin filin wanda ke hana saurin shiga filin wasa, bincike ya nuna wasu filayen gasar NPFL ba su da wani shamaki tsakanin yan kallo da filin wasa, hakazalika akwai bukatar raba magoya bayan kungiyoyin dake buga wasa zuwa mabanbantan wuraren zama, wannan yana rage rikici kai tsaye.

 

Matakan Ladabtarwa Masu Tsauri:

Hukumar NPFL ta riga ta sanya takunkumi mai tsanani ga Kano Pillars bayan wani tashin hankali da aka yi a wasanta da 3SC inda akaci kungiyar tarar Naira miliyan 9 da rabi, rage maki da kwallaye, da kuma rufe filin wasansu na gida a yanzu.

 

Hukunta Laifuka:

Ya kamata a gano wadanda suka mamaye filin wasa ko suka kai hari ga yan wasa da jami’ai (ta hanyar CCTV) kuma a gurfanar da su a gaban kuliya, wannan zai rage rikici a cikin filayen wasa.

 

Wayar Da Kai:

Akwai bukatar ci gaba da ilmantar da magoya baya kan halaye masu kyau, hatsarin tashin hankali, da kuma girmama jami’an wasa, kungiyoyi da NPFL za su iya gudanar da bita na magoya baya, amfani da kafofin sada zumunta, da kuma amfani da kungiyoyin magoya baya.

 

Rahoton Wasanni:

Bayan kowace wasa da aka buga akwai bukatar a gabatar da cikakken rahoto akan yadda wasan ya gudana, ta hakanan Za’a iya gano wuraren da suke bukatar gyara domin gyarawa kafin buga wasan gaba, hakazalika za a iya gano wanda ya nuna halayen rashin da’a a wasan domin a hukunta shi.

 

Jawo Hankalin Matasa:

Yawancin abubuwan tashin hankali suna faruwa ne da saka hannun matasa, saboda a cikinsu ne ake samun magoya baya masu zuciya da saurin fusata, akwai bukatar a nuna masu wasan kwallo WASANE BA FADA BA, mahukunta su shiga makarantu, majalisun matasa, da shugabannin al’umma domin sanar dasu ilimin kwallon kafa don koyar da girmamawa, wasa mai kyau, da kuma nusar dasu illolin tashin hankali.

 

Inganta Tsarin Shiga Filin Wasa:

Ayi amfani da hanyoyin zamani musamman na dijital wajen bayar da tikitin shiga filayen wasa da kuma guje wa cunkoso, idan da hali ana iya saka bayanan duk wanda ya shiga filin wasa wanda zai sa idan wani ya aikata laifi zai yi saukin kamawa ga hukuma.

 

Sakon Neman Afuwa Ga Jama’a Da Jagoranci:

Shugabannin kungiyoyi (kamar Ahmed Musa na Pillars) ya kamata su ci gaba da yin kira ga jama’a game da illar tashin hankali, amma kuma suyi hakan ta hanyar da magoya baya zasu gamsu kuma su fahimci abinda ake bukatar su Sani, Musa ya riga ya nemi afuwa a bainar jama’a kuma ya yi alkawarin daukar mataki.

Firimiyar Nijeriya
Rabilu Sanusi Bena
+ posts Bio
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Real Madrid Ta Kammala Ɗaukar Bernardo Silva Daga Man City
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Afirka Ta Kudu Ta Kafa Mummunan Tarihi A Gasar Kofin Duniya
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    An Rufe Makarantu A Mexico Saboda Fara Gasar Kofin Duniya
Firimiyar Nijeriya
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya
  • Sulaiman
    Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari
  • Sulaiman
    Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana
  • Sulaiman
    Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

MASU ALAKA

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar
Manyan Labarai

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé
Wasanni

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

June 13, 2026
Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?
Wasanni

Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

June 12, 2026
Next Post
APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

LABARAI MASU NASABA

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.