• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kafar Sadarwa Ta Karrama Fintiri, Bindow, Boss Mustapha Da Wasu 17 A Adamawa

by Muh'd Shafi'u Saleh
2 years ago
Fintiri

Kafar sadarwa ta TGnews, ta karrama gwamnan Jihar Adamawa Ahmadu Umaru Fintiri, tsohon gwamnan jihar Umaru Jibrilla Bindow, da wasu mutum 18, ranar Asabar.

Kafar ta kuma karrama tsohon sakataren gwamnatin tarayya (SGF), Boss Mustapha, da Admiral Jamila Sadiq Malafa (mai ritaya), da dan majalisar wakilai mai wakiltar kananan hukumomin Song/Fufore a majalisar wakilai ta kasa Honorabul Aliyu Wakili Boya.

  • Gobara Ta Lalata Shaguna 10 A Adamawa
  • Isra’ila Na Kara Iza Wutar Rikici A Sassan Gabas Ta Tsakiya -Lebanon

Haka kuma kafar ta karrama mataimakin shugaban jami’ar tarayya da ke Kashere Jihar Gombe, Farfesa Umar Pate, Reberan Dakta Panti Filibus, LCCN. Arch Bishop, Sarkin Mubi Alhaji Abubakar Isa Ahmadu, sarkin Ganye Gangwari Ganye, Alhaji Adamu Sanda, Hama Bachama Homun Ismaila Daniel Shaga da Kwandi Nunguriya, Mai Martaba Kuruhaye Dishon Dansanda.

Sauran mutanen da kafar ta karrama su ne shugaban bangaren labarai na kafar sadarwar talabijin na TVC, Stella Din-Peters, Mal Hamisu Idris Medugu, Barista Shafari Shadrach Kanya, tsohon dan majalisar dokokin jihar Honarabul Hassan Mamman Barguma, Ardo Usman da Madam Celina Yakubu.

Da yake jawabi lokacin karbar lambar yabon, Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri, ya gode wa kafar sadarwar yada labarai ta TGNews, bisa yadda ya amince da kokarin gwamnatinsa na ganin an samar da shugabanci na gari ga jama’a.

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar

Jami’an Tsaro Sun Cafke Ɓarayin Kayayyakin Turakun Wutar Lantarki Na Hanyar Mando Zuwa Jos

Gwamnan wanda ya samu wakilcin mataimakiyarsa Farfesa Kaletapwa Farauta, ya yi alkawarin ci gaba da samar da ribar dimokuradiyya ga ’yan jihar, tare da gode wa wadanda su ka shirya taron bisa karramawar da aka masa.

Da shi ma ke jawabi a bikin mataimakin shugaban jami’ar fasaha ta gwamnatin tarayya dake Kashere, Farfesa Umar Pate, ya ce fasahar sadarwa ta kawo sauyi ba kawai a fannin aikin jarida ba, har ma a rayuwar dan adam baki daya.

Farfesa Pate ya yaba wa kamfanin dillancin labarai na TG game da shirya taron kuma ya bukaci ‘yan jarida da su rungumi gagarumin sauyin da fasahar sadarwa ta kawo, tare da baiwa jama’a bayanai da rahotanni na gaskiya.

A jawabinsa na maraba, Babban Edita/Mawallafin TG News, Tom Garba, ya yaba wa wadanda su ka samu kyautar da kuma wadanda su ka dauki lokaci na halartan taron, tare da nuna godiyarsa ga bikin karramawar da ya bayyana da “mai dimbin tarihi”

Haka kuma kafar TGNews, ta kaddamar da mujalla ta farko ta TGNews Magazine, da za ta rika fita wata-wata domin ci gaba da hidimta wa al’umma.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar

October 9, 2025
TCN
Labarai

Jami’an Tsaro Sun Cafke Ɓarayin Kayayyakin Turakun Wutar Lantarki Na Hanyar Mando Zuwa Jos

October 9, 2025
Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI
Labarai

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

October 9, 2025
Next Post
Majalisar Gudanarwar Sin Ta Yi Kira Da A Kara Bunkasa Tsarin Kula Da Tsoffi

Majalisar Gudanarwar Sin Ta Yi Kira Da A Kara Bunkasa Tsarin Kula Da Tsoffi

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar

‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar

October 9, 2025
Sin Na Ci Gaba Da Goyon Bayan Kawo Karshen Rikicin Gaza

Sin Na Ci Gaba Da Goyon Bayan Kawo Karshen Rikicin Gaza

October 9, 2025
TCN

Jami’an Tsaro Sun Cafke Ɓarayin Kayayyakin Turakun Wutar Lantarki Na Hanyar Mando Zuwa Jos

October 9, 2025
An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar 

An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar 

October 9, 2025
Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

October 9, 2025
Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

October 9, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

Batun Umarnin Kotu Na Kama Tsohon Shugaban INEC Ƙage Ne Kawai – Shugaban Jam’iyyar AA 

October 9, 2025
An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

October 9, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

October 9, 2025
Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

October 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.