• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kafar Sadarwa Ta Karrama Fintiri, Bindow, Boss Mustapha Da Wasu 17 A Adamawa

by Muh'd Shafi'u Saleh
1 year ago
in Labarai
0
Kafar Sadarwa Ta Karrama Fintiri, Bindow, Boss Mustapha Da Wasu 17 A Adamawa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kafar sadarwa ta TGnews, ta karrama gwamnan Jihar Adamawa Ahmadu Umaru Fintiri, tsohon gwamnan jihar Umaru Jibrilla Bindow, da wasu mutum 18, ranar Asabar.

Kafar ta kuma karrama tsohon sakataren gwamnatin tarayya (SGF), Boss Mustapha, da Admiral Jamila Sadiq Malafa (mai ritaya), da dan majalisar wakilai mai wakiltar kananan hukumomin Song/Fufore a majalisar wakilai ta kasa Honorabul Aliyu Wakili Boya.

  • Gobara Ta Lalata Shaguna 10 A Adamawa
  • Isra’ila Na Kara Iza Wutar Rikici A Sassan Gabas Ta Tsakiya -Lebanon

Haka kuma kafar ta karrama mataimakin shugaban jami’ar tarayya da ke Kashere Jihar Gombe, Farfesa Umar Pate, Reberan Dakta Panti Filibus, LCCN. Arch Bishop, Sarkin Mubi Alhaji Abubakar Isa Ahmadu, sarkin Ganye Gangwari Ganye, Alhaji Adamu Sanda, Hama Bachama Homun Ismaila Daniel Shaga da Kwandi Nunguriya, Mai Martaba Kuruhaye Dishon Dansanda.

Sauran mutanen da kafar ta karrama su ne shugaban bangaren labarai na kafar sadarwar talabijin na TVC, Stella Din-Peters, Mal Hamisu Idris Medugu, Barista Shafari Shadrach Kanya, tsohon dan majalisar dokokin jihar Honarabul Hassan Mamman Barguma, Ardo Usman da Madam Celina Yakubu.

Da yake jawabi lokacin karbar lambar yabon, Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri, ya gode wa kafar sadarwar yada labarai ta TGNews, bisa yadda ya amince da kokarin gwamnatinsa na ganin an samar da shugabanci na gari ga jama’a.

Labarai Masu Nasaba

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Gwamnan wanda ya samu wakilcin mataimakiyarsa Farfesa Kaletapwa Farauta, ya yi alkawarin ci gaba da samar da ribar dimokuradiyya ga ’yan jihar, tare da gode wa wadanda su ka shirya taron bisa karramawar da aka masa.

Da shi ma ke jawabi a bikin mataimakin shugaban jami’ar fasaha ta gwamnatin tarayya dake Kashere, Farfesa Umar Pate, ya ce fasahar sadarwa ta kawo sauyi ba kawai a fannin aikin jarida ba, har ma a rayuwar dan adam baki daya.

Farfesa Pate ya yaba wa kamfanin dillancin labarai na TG game da shirya taron kuma ya bukaci ‘yan jarida da su rungumi gagarumin sauyin da fasahar sadarwa ta kawo, tare da baiwa jama’a bayanai da rahotanni na gaskiya.

A jawabinsa na maraba, Babban Edita/Mawallafin TG News, Tom Garba, ya yaba wa wadanda su ka samu kyautar da kuma wadanda su ka dauki lokaci na halartan taron, tare da nuna godiyarsa ga bikin karramawar da ya bayyana da “mai dimbin tarihi”

Haka kuma kafar TGNews, ta kaddamar da mujalla ta farko ta TGNews Magazine, da za ta rika fita wata-wata domin ci gaba da hidimta wa al’umma.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Hadin Garin Dilka Don Kawata Fata

Next Post

Majalisar Gudanarwar Sin Ta Yi Kira Da A Kara Bunkasa Tsarin Kula Da Tsoffi

Related

Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25
Labarai

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

5 hours ago
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa
Manyan Labarai

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

5 hours ago
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)
Labarai

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

6 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

7 hours ago
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu
Manyan Labarai

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

9 hours ago
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe
Manyan Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

10 hours ago
Next Post
Majalisar Gudanarwar Sin Ta Yi Kira Da A Kara Bunkasa Tsarin Kula Da Tsoffi

Majalisar Gudanarwar Sin Ta Yi Kira Da A Kara Bunkasa Tsarin Kula Da Tsoffi

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.