ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kafar Sadarwa Ta Karrama Fintiri, Bindow, Boss Mustapha Da Wasu 17 A Adamawa

by Muh'd Shafi'u Saleh
2 years ago
Fintiri

Kafar sadarwa ta TGnews, ta karrama gwamnan Jihar Adamawa Ahmadu Umaru Fintiri, tsohon gwamnan jihar Umaru Jibrilla Bindow, da wasu mutum 18, ranar Asabar.

Kafar ta kuma karrama tsohon sakataren gwamnatin tarayya (SGF), Boss Mustapha, da Admiral Jamila Sadiq Malafa (mai ritaya), da dan majalisar wakilai mai wakiltar kananan hukumomin Song/Fufore a majalisar wakilai ta kasa Honorabul Aliyu Wakili Boya.

  • Gobara Ta Lalata Shaguna 10 A Adamawa
  • Isra’ila Na Kara Iza Wutar Rikici A Sassan Gabas Ta Tsakiya -Lebanon

Haka kuma kafar ta karrama mataimakin shugaban jami’ar tarayya da ke Kashere Jihar Gombe, Farfesa Umar Pate, Reberan Dakta Panti Filibus, LCCN. Arch Bishop, Sarkin Mubi Alhaji Abubakar Isa Ahmadu, sarkin Ganye Gangwari Ganye, Alhaji Adamu Sanda, Hama Bachama Homun Ismaila Daniel Shaga da Kwandi Nunguriya, Mai Martaba Kuruhaye Dishon Dansanda.

ADVERTISEMENT

Sauran mutanen da kafar ta karrama su ne shugaban bangaren labarai na kafar sadarwar talabijin na TVC, Stella Din-Peters, Mal Hamisu Idris Medugu, Barista Shafari Shadrach Kanya, tsohon dan majalisar dokokin jihar Honarabul Hassan Mamman Barguma, Ardo Usman da Madam Celina Yakubu.

Da yake jawabi lokacin karbar lambar yabon, Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri, ya gode wa kafar sadarwar yada labarai ta TGNews, bisa yadda ya amince da kokarin gwamnatinsa na ganin an samar da shugabanci na gari ga jama’a.

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Gwamnan wanda ya samu wakilcin mataimakiyarsa Farfesa Kaletapwa Farauta, ya yi alkawarin ci gaba da samar da ribar dimokuradiyya ga ’yan jihar, tare da gode wa wadanda su ka shirya taron bisa karramawar da aka masa.

Da shi ma ke jawabi a bikin mataimakin shugaban jami’ar fasaha ta gwamnatin tarayya dake Kashere, Farfesa Umar Pate, ya ce fasahar sadarwa ta kawo sauyi ba kawai a fannin aikin jarida ba, har ma a rayuwar dan adam baki daya.

Farfesa Pate ya yaba wa kamfanin dillancin labarai na TG game da shirya taron kuma ya bukaci ‘yan jarida da su rungumi gagarumin sauyin da fasahar sadarwa ta kawo, tare da baiwa jama’a bayanai da rahotanni na gaskiya.

A jawabinsa na maraba, Babban Edita/Mawallafin TG News, Tom Garba, ya yaba wa wadanda su ka samu kyautar da kuma wadanda su ka dauki lokaci na halartan taron, tare da nuna godiyarsa ga bikin karramawar da ya bayyana da “mai dimbin tarihi”

Haka kuma kafar TGNews, ta kaddamar da mujalla ta farko ta TGNews Magazine, da za ta rika fita wata-wata domin ci gaba da hidimta wa al’umma.

Fintiri
Muh'd Shafi'u Saleh
+ postsBio
  • Muh'd Shafi'u Saleh
    https://hausa.leadership.ng/author/muhd-shafiu-saleh/
    Jami’in Tsaro Ya Mayar da Dala 505 Da Riyal 30 Da Ya Tsinta A Yola
  • Muh'd Shafi'u Saleh
    https://hausa.leadership.ng/author/muhd-shafiu-saleh/
    Shahararren Malamin Addinin Islama A Adamawa Sheikh Ibrahim Abubakar Daware Ya Rasu
  • Muh'd Shafi'u Saleh
    https://hausa.leadership.ng/author/muhd-shafiu-saleh/
    An Yi Wa ‘Yansanda 110 Ƙarin Girma A Adamawa
  • Muh'd Shafi'u Saleh
    https://hausa.leadership.ng/author/muhd-shafiu-saleh/
    Gwamna Fintiri Ya Nada Sabbin Sarakuna 7 A Jihar Adamawa

MASU ALAKA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato
Tsaro

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Next Post
Majalisar Gudanarwar Sin Ta Yi Kira Da A Kara Bunkasa Tsarin Kula Da Tsoffi

Majalisar Gudanarwar Sin Ta Yi Kira Da A Kara Bunkasa Tsarin Kula Da Tsoffi

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.