• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manyan Abubuwan Da Sin Ta Fi Mayar Da Hankali A Kai A Shekarar 2023

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Kasar Sin
0
Manyan Abubuwan Da Sin Ta Fi Mayar Da Hankali A Kai A Shekarar 2023
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A shekarar 2023, an gamu da sauye-sauye da tashe-tashen hankula da dama, kamar rikicin da ya barke a tsakanin kasashen Rasha da Ukraine, da tsakanin Isra’ila da Falesdinu. Haka kuma annobar cutar numfashi ta COVID-19 da ta barke ta yi tasiri matuka ga tattalin arziki da zaman rayuwar al’ummar kasashen duniya a shekarar 2023. Mutane na ganin cewa, mun fuskanci manyan sauye-sauye da ba a taba ganin irinsu ba a duniyarmu. A sa’i daya kuma, a shekarar 2023 da ta wuce, al’ummar kasashen duniya sun ci gaba da yin kokari domin shimfida zaman lafiya, da neman ci gaba, da yin hadin gwiwa, da kuma cimma moriyar juna. Al’ummomin kasashen duniya sun ga yadda kasar Sin ta dukufa wajen inganta harkokin zamanintar da kasa, da yadda kasar Sin ta samar wa kasashen duniya sabbin damammaki da ba da tallafi ga jama’ar kasa da kasa a lokacin da take kokarin samun bunkasuwar tattalin arziki mai inganci. Kana, jama’ar kasashen duniya sun kara fahimtar shawarar “Ziri daya da hanya daya” da kuma dalilan da suka sa shawarar ta samu karbuwa daga bangarori daban daban na duniyarmu. Haka zalika, mutane sun ga muhimmin tasirin da sabon daftarin tafiyar da harkokin kasashen duniya da kasar Sin ta gabatar ya yi wa gamayyar kasa da kasa. Wannan ya sa, a karshen shekarar 2023, wakilan Babban Gidan Rediyo da Talabijin na Kasar Sin wato CMG suka zanta da ’yan siyasa da ’yan kasuwa da kuma kwararru a fannoni daban daban daga kasar Sin da ma kasashen waje, inda suka yaba wa kasar Sin game da kokarin da ta yi a fannoni daban daban a shekarar 2023.

A shekarar 2023, kasar Sin ta sami gagarumin ci gaba a fannin zamanintar da kasa. Kwararru da shugabannin kamfanoni da dama na kasashen duniya sun bayyana cewa, abu mai muhimmanci da zai taimaka mana wajen kara fahimtar kasar Sin, shi ne dabaru da manufofin kasar Sin ta fuskar zamanintar da kasa, da gane muhimmiyar ma’anar aiki ga kasa da kasa.

  • Manzon Musamman Na Shugaban Sin Zai Halarci Taron Koli Karo Na 19 Na Kungiyar Kasashe ‘Yan Ba-Ruwanmu
  • Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Da Su Goyi Bayan Kasashen Yammacin Afirka Da Na Sahel

Shugaban asusun kula da dangantakar dake tsakanin kasar Amurka da kasar Sin na George H. W. Bush, Neil Bush ya bayyana cewa, gwamnatin kasar Sin ta kware sosai wajen tsara shiri na dogon lokaci domin ba da jagoranci kan ayyukan neman ci gaba mai inganci. Ya ba da misali cewa, aikin zamanintar da kasar Sin ya mai da hankali kan yadda za a nemi bunkasuwa ta hanyar kare muhalli, don haka, gwamnatin tsakiyar kasar Sin da ma gwamnatocin sassan kasar sun tsara wani cikakken shirin neman bunkasuwa, inda suka ba da jagorancin raya fasahohin samar da makamashi masu tsabta, kamar amfani da hasken rana da karfin iska da sauransu, abin da ya sanya kasar zama a kan gaba a duniya a fannin nazarin fasahohin samar da motoci masu aiki da wutar lantarki.

2023
Kasar Sin ta kasance kasar da ta fi fitar da motoci zuwa kasashen waje a fadin duniya

Kamar yadda Neil Bush ya bayyana, a shekarar 2023, sana’o’in kere-kere masu amfani da fasahohin zamani kamar sana’ar sarrafa motoci sun bunkasa cikin sauri sosai, inda kasar Sin ta zarce kasar Japan a fannin fitar da motoci zuwa kasashen waje, lamarin da ya sa kasar Sin ta kasance ta farko a fannin sayar da motoci zuwa kasashen waje a fadin duniya. Kana, bunkasuwar aikin samar da motoci masu amfani da wutar lantarki ya zama daya daga cikin bangarorin da suka nuna bunkasuwar tattalin arzikin kasar Sin mai inganci. A shekarar 2023 da ta wuce, kasar Sin ta cimma nasarori da dama a fannin zamanintar da kasa, kamar samar da wayar salula masu amfani da fasahar IC kirar kasar Sin, da babban jiragen ruwan fasinjoji na farko da kasar Sin ta kera, da kuma samar da kumbon zirga-zirgar sararin samaniya da sauran harkokin da kasar Sin ba ta kware sosai ba a baya. Kuma, kasar Sin ta kai matsayin farko a fannonin raya fasahar kwaikwayon tunanin dan-Adam AI da fasahohin na’urar kididdiga ta Quantum da sauran sabbin fasahohi.

2023
Layin dogon tsakanin Jakarta da Bandung na kasar Indonesiya da aka kaddamar a watan Oktoba na shekarar 2023, wannan shi ne layin dogo mai saurin tafiya na farko da wani kamfanin kasar Sin ya shimfida a kudu maso gabashin Asiya.

Zamanintarwa iri na kasar Sin, ba kawai za ta tallafa wa kasar Sin ba, har ma za ta tallafa wa kasashen duniya. Shugaban reshen kamfanin Shiseido dake kasar Sin Umetsu Toshinobu ya bayyana cewa, hanyar da kasar Sin take bi wajen neman bunkasuwar tattalin arziki mai inganci, ta taimakawa jama’ar kasa wajen yin kirkire-kirkire, da samar da sabbin damammaki ga bunkasuwar tattalin arzikin duniya. A matsayinsa na kamfani mallakin kasar waje dake kasar Sin, kamfanin zai kuma ci gaba da amfana da zamanintarwar kasar Sin.

Labarai Masu Nasaba

Bude Kasar Sin Na Kyautata Ci Gaban Duniya

Mu Leka Jihar Mongolia Ta Gida Dake Arewacin Kasar Sin

2023
Wasu daga cikin wuraren diban ruwa da ma’aikatan kamfanin CCECC suka kafa a wasu kauyukan kasar Tanzaniya.

Masanin cibiyar kwararru ta Taihe Liu Yangsheng ya bayyana cewa, masana’antun kere-kere na kasar dake kan gaba suna da muhimmanci a fannin raya tattalin arzikin kasar Sin, suna kuma ba da gudummawa a fannin raya kasashe masu tasowa dake duniyarmu. Ya ce, a halin yanzu, akwai karin kasashen duniya dake koyon fasahohin kasar Sin wajen zamanintar da kasashensu, sabo da hanyar zamanintar da kasa ta sa kasar ta cimma nasarori. Kasar Sin na neman zamanintar da kanta bisa manyan tsare-tsare, lamarin da ya nuna hagen nesan kasar Sin da kuma yadda ta tsara shiri mai inganci, kamar sabunta ababen more rayuwa da dai sauransu. Hakan ya taiamakwa jama’ar kasar Sin wajen kafa wani cikakken tsarin samarwa da fitar da kayayyaki, wanda ya kasance mafi inganci a tarihin bil Adama.

2023
. Yadda ake raya aikin samar da wutar lantarki ta hasken rana a birnin Tangshan na lardin Hebei na kasar Sin, domin neman bunkasuwa ta hanyoyin kare muhalli.

A shekarar 2023 ne aka cika shekaru 10 da gabatar da shawarar “Ziri daya da hanya daya”. Shahararren masanin harkokin kasashen duniya na kasar Iran, kana shehun malami a jami’ar Tehran Seyed Mohammad Marandi ya bayyana cewa, tun bayan gabatar da shawarar “Ziri daya da hanya daya”, shekaru goma da suka wuce, cinikayyar dake tsakanin kasashen duniya cikin wadannan shekaru 10 ta sauya sosai, wasu kasashe sun rage dogaron da suke yi kan sufurin hajoji ta hanyoyin teku sakamakon bude hanyoyin jiragen kasa a tsakanin kasar Sin da kasashen Turai, matsayin kasashen dake yankin tsakiyar Asiya ya dagu sosai, lamarin da ya samar da tallafi ga wasu kasashe ciki har da kasar Iran da ma kasar Sin.

A shekarar 2023, an gudanar da taron kolin dandalin tattaunawar hadin gwiwar kasashen duniya bisa shawarar “Ziri daya da hanya daya” karo na uku a birnin Beijing, fadar mulkin kasar Sin. A yayin taron da ya samu mahalarta daga kasashe guda 151 da kungiyoyin kasa da kasa guda 41, an cimma sakamako guda 458, lamarin da ya nuna kwarin gwiwar kasashen duniya wajen gina shawarar “Ziri daya da hanya daya” cikin hadin gwiwa, da babban tasirin da shawarar ta kawowa kasashen duniya.

2023
Cibiyar samar da iskar hydrogen ga manyan motoci da aka kafa a birnin Chongqing na kasar.

A yayin bikin bude taron, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya sanar da cewa, kasar Sin ta fitar da manyan matakai guda 8 domin gina shawarar “Ziri daya da hanya daya” cikin hadin gwiwa kamar yadda ake fata, inda ta ba da jagora ga ci gaban ayyukan da abin ya shafa cikin shekaru 10 masu zuwa.

A matsayin muhimmin mataki cikin wadannan manyan matakai guda 8, shirin tallafawa al’umma mai taken “kanana kuma da kyau” da wasu muhimman harkokin gine-gine za su kara karfin kasashen da shawarar “Ziri daya da hanya daya” ta shafa wajen inganta hadin gwiwar dake tsakaninsu yadda ya kamata.

Mataimakin shugaban kwalejin nazarin shawarar “Ziri daya da hanya daya” da tafiyar da harkokin duniya na jami’ar Fudan dake birnin Shanghai na kasar Sin, Huang Renwei ya bayyana cewa, kananan shirye-shiryen tallafawa jama’a guda 1000 da kasar Sin ta yi alkawarin aiwatarwa, za su taimaka wajen raya kasuwanni, da shigar da Karin kamfanoni da hukumomi cikin shirin tallafawa al’umma mai taken “kanana kuma da kyau”, harkar da za ta kasance abin koyi cikin ayyukan gina shawarar “Ziri daya da hanya daya” cikin hadin gwiwa. Sabo muhimmancin matakin aiwatar da shirye-shiryen da aka tsara bisa shawarar, lamarin zai yi muhimmin tasiri ga kasashen da suka yi hadin gwiwar gina shawarar “Ziri daya da hanya daya” cikin shekaru 10 masu zuwa.

Kamar yadda shugaban kasar Sin Xi Jinping ya bayyana, makomar kasar Sin da ta dukkanin bil Adama a hade suke. Kasar Sin tana tsayawa tsayin daka wajen habaka moriyar bai daya dake tsakaninta da sauran kasashen duniya, da samar da sabbin damammaki da kwarin gwiwa ga kasashen duniya bisa sabuwar bunkasuwar da ta samu. Kasar Sin na sa ran karfafa hadin gwiwar dake tsakaninta da sauran kasashen duniya, domin zamanintar da kasashen duniya baki daya, ta yadda za a samu ci gaba cikin lumana da yin hadin gwiwa da cimma moriyar juna, da kuma samun wadata tare. (Maryam Yang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kasashen yammaNATORashaTattalin arzikin kasar Sin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Bankin Duniya Ya Yi Hasashen Bunkasar Tattalin Arzikin Nijeriya Da Kashi 3.3 A 2024

Next Post

NERC Ta Kori Dukkan Daraktocin Wutar Lantarki Na Jihar Kaduna 

Related

Bude Kasar Sin Na Kyautata Ci Gaban Duniya
Daga Kasar Sin

Bude Kasar Sin Na Kyautata Ci Gaban Duniya

3 months ago
Mu Leka Jihar Mongolia Ta Gida Dake Arewacin Kasar Sin
Daga Kasar Sin

Mu Leka Jihar Mongolia Ta Gida Dake Arewacin Kasar Sin

10 months ago
wang lili
Daga Kasar Sin

Yadda Wang Lili Ke Kiyaye Neman Cimma Nasara A Wasan Kwallon Kwando

10 months ago
Kumbon Sin Ya Tashi Daga Bangaren Duniyar Wata Mai Nisa Dauke Samfura
Daga Kasar Sin

Kumbon Sin Ya Tashi Daga Bangaren Duniyar Wata Mai Nisa Dauke Samfura

12 months ago
Zambiya
Daga Kasar Sin

’Yar Kasar Zambiya: A Nan Kasar Sin, Ina Jin Tamkar Ina Gida!

1 year ago
Ba Shakka Kamfanonin Ketare Za Su Ci Riba In Suka Zuba Jari Da Aiwatar Da Ayyukansu A Sin
Daga Kasar Sin

Ba Shakka Kamfanonin Ketare Za Su Ci Riba In Suka Zuba Jari Da Aiwatar Da Ayyukansu A Sin

1 year ago
Next Post
Wutar lantarki

NERC Ta Kori Dukkan Daraktocin Wutar Lantarki Na Jihar Kaduna 

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

May 15, 2025
An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe

An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe

May 15, 2025
HOTO: Ofishin Tsohon Shugaban Kasa Shagari Bayan Shekara 42

HOTO: Ofishin Tsohon Shugaban Kasa Shagari Bayan Shekara 42

May 15, 2025
Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

May 15, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

May 15, 2025
Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

May 15, 2025
An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

May 15, 2025
NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

May 15, 2025
Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

May 15, 2025
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.