• English
  • Business News
Saturday, July 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Buhari Za Ta Yi Mai Yiwuwa Wajen Tabbatar Da Tsaro A Kasar Nan – Malami

by Umar Faruk
3 years ago
in Labarai
0
Gwamnatin Buhari Za Ta Yi Mai Yiwuwa Wajen Tabbatar Da Tsaro A Kasar Nan – Malami
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Shari’a Abubakar Malami (SAN), ya bayyana cewa gwamnatin Buhari za ta yi duk mai yiwuwa wajen tabbatar da tsaron kasar nan kafin karewar wa’adinsa.

Malami ya bayyana hakan ne a cikin sakon murnar sallar ga al’ummar Musulmin kasa da na Jihar Kebbi kan murnar zagayowar sallah.

  • Jaridar Daily Trust Ba Ta Yi Mana Adalci Ba- Fadar Shugaban Kasa 
  • Mataimaki: Gwamnonin APC Na Alfahari Da Zabin Tinubu – Bagudu

Bayanin hakan na kunshe ne a cikin wata takarar da sakataren yada labaransa, Ibrahim Abubakar Dakingari, na kungiyar Khadimmiya da ya sanyawa hannu aka kuma rabawa manema labarai a Brinin Kebbi.

Minista ya ce”Bikin sallah na tunatar da musulmi da su kasance masu biyayya da zuciya daya ga umarni da dokokin Allah madaukakin Sarki kamar yadda Annabi Ibrahim, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya yi.”

“Gudanar da wannan gagarumin biki, ya kamata mu yi tunani a kan darussa na asali na hakuri, sadaukarwa da mika wuya ga yardar Allah da Annabi Ibrahim ya nuna a lokacin da Allah ya umarce shi da ya yanka dansa tilo (Isma’ila), ta hanyar sadaukar da kanmu ga kara riko da dokokin Ubangiji da kuma nuna hakikanin ruhin Musulunci a cikin dukkan ayyukanmu.

Labarai Masu Nasaba

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

“Yayin da mu ke bikin babbar sallah, dole ne mu yi la’akari da duk abubuwan da ke faruwa a kasarmu, domin mu yi amfani da lokacin yin addu’a don Allah ya kawo mana dauki ga matsalolin tsaro da tattalin arziki da ke addabar kasar nan wanda gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari ke ciki, inji shi”.

Haka kuma ministan ya kuma yi kira ga ’yan uwanmu maza da mata a kasa mai tsarki da suke gudanar da aikin hajjin bana da su yi ta addu’a domin neman fansa.

“Ina kara sake tabbatar muku cewa gwamnatin Buhari za ta ci gaba da yin duk mai yiwuwa wajen tabbatar da tsaron kasar nan.

“Ina addu’ar Allah ya karbi addu’o’inmu na ganin an samu dawamammen zaman lafiya a jihar Kebbi da kasa baki daya tare da samar da zaman lafiya a siyasance,” in ji Malami.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BuhariKebbiMalamiMatsalar TsaroWa'adin Mulki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Jaridar Daily Trust Ba Ta Yi Mana Adalci Ba- Fadar Shugaban Kasa 

Next Post

Gwamnatin Tarayya Ba Ta Muhimmanta Tsaro Ba – Matawalle

Related

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai
Ra'ayi Riga

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

6 hours ago
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a
Rahotonni

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

7 hours ago
Illar Kakaba Wa Majalisa Ta 10 Shugabanni Ga Gwamnatin Tinubu – Dattawan Arewa
Labarai

Majalisar Tarayya Ta Karrama NPA Da Kyautar Gaskiya Da Riƙon Amana Ta 2025

9 hours ago
Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Mutum 2 Da AK-47 A Taraba

10 hours ago
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Labarai

Amurka Ta Rage Wa’adin Bizar ‘Yan Nijeriya Zuwa Wata Uku

11 hours ago
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna
Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna

12 hours ago
Next Post
Gwamnatin Tarayya Ba Ta Muhimmanta Tsaro Ba – Matawalle

Gwamnatin Tarayya Ba Ta Muhimmanta Tsaro Ba - Matawalle

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

July 11, 2025
Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

July 11, 2025
Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

July 11, 2025
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi

2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

July 11, 2025
“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

July 11, 2025
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

July 11, 2025
Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

July 11, 2025
Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

July 11, 2025
Illar Kakaba Wa Majalisa Ta 10 Shugabanni Ga Gwamnatin Tinubu – Dattawan Arewa

Majalisar Tarayya Ta Karrama NPA Da Kyautar Gaskiya Da Riƙon Amana Ta 2025

July 11, 2025
FRCN Ya Kaddamar Da Shirin Koyar Da Sinanci Mai Taken “Hello China”

FRCN Ya Kaddamar Da Shirin Koyar Da Sinanci Mai Taken “Hello China”

July 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.