• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsalolin Da Za Su Dabaibaye Harkokin Masana’antu A 2024

by Bello Hamza
2 years ago
in Tattalin Arziki
0
Matsalolin Da Za Su Dabaibaye Harkokin Masana’antu A 2024
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yayin da muke shiga sabuwar shekara 2024, harkokin kasuwanci na fuskantar manyan matsaloli da barazanar da za su bayar da gudummamwar durkusherwar su da hana su walwala.

Shugaban kungiyar masu masana’antu ta kasa, (MAN), Segun Ajayi-Kadir, ya yi hasashen cewa, shekarar 2024 za ta zo da manyan kalubale ga masu masana’antu saboda alamu sun nuna babu kyakyawar fata musamman a cikin watanni 6 na farkon shekarar.

  • Jihar Kaduna Za Ta Ƙarfafa Ƙawancen Tattalin Arziki Da Ƙasar Jamus
  • ‘Yansanda Sun Cafke Wasu Mutane Biyu Da Ake Zargi Da Satar Keke-napep A Kano

Nazari ya nuna cewa, matsalolin za su addabi kanana da manyan masana’natu wadanda za su taso daga harkokin tattalin arziki na ciki da wajen Nijeriya.

Musamman ma kungiyar MAN ta bayyana cewa, za a samu nakasu a bunkasar masana’antu daga kashi 2.4 a shekarar 2021 zuwa kashi 0.48 a zango na uku na shekarar 2023.

Ana iya ganin irin wannan ci bayan a manyan kamfanonin kasashe irin su Chana da Amurka, Nijeriya kuma ba za ta iya kare kanta daga wadannan abubuwan ba.

Labarai Masu Nasaba

NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya

Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci Bunkasa Fannin Mai Da Ake Hakowa A Teku

Yana da matukar muhimmanci a fahimci cewa, matsalolin cikin gida kama daga karyewar darajar Naira da tashin kudin ruwa suna kawo cikas ga bunkasar kamfanonin kasuwanci da kashi 50 a cikin dai.

Za kuma a iya tuna manyan kamfanoni 6 da suka fice daga Nijeriya a cikin wata shida da suka wuce, wadanda suka hada da kamfanin samar da abinci na ‘Procter & Gamble’, Unileber, GladoSmithKline Consumer Nigeria Plc, Sanofi, French pharmaceutical multinational, Bolt Food da kuma kamfanin hada allura na ‘Jubilee Syringe Manufacturing’.

A ra’ayinmu, tsare-tsaren Babban Bankin Nijeriya CBN a ‘yan shekarun nan bai taimaka ba wajen zaburar da bunkasar kamfanoni da tattalin arzikin Nijeriya ba.

Masu harkokin fitar da kayyakin da ake sarrafawa a Nijeriya suna fuskanta rashin tabbas, basu da damar samun kudaden kasashen waje don gudanar da harkokin kasuwancinsu wanda haka ya taimaka wajen durkushewarsu.

Wani abin takaicin kuma shi ne tsaretsaren da aka samar don dakile hauhawar farashi ya taimaka ne kawai weajen takura kanana da mastaikaitun kamfanoni a fadin tarayyar kasar nan.

A irin wannan yanayin harkokin kasuwanci ba za su samu kwarin gwiwar ci gaba ba, kamar yadda kungiyar masu masana’antu ta zayyana a wani taron shugabannin kamfanoni da aka yi kwanakin baya ta yi.

Kungiyar ta yi hasashen wadannan kalubalen za su ta’azzara har zuwa zango na biyu na sabuwar shekara 2024, ana kuma iya samun farfadowa dan kadan daga baya. A hasashen nasu bangaren masana’antu zai samu bunkasar kasa da kashi 3.2 a wannan shdekarar, yayin da gudumawar bangaren ga tattalin arzikin kasa zai gaza kashi 10.

In har ana son kauce wa fadawa wadannan mastalolin dole a canza tsare-tsaren tattalin arzikin kasa ta yadda zai taimakawa bunkasar harkokin kasuwanci a Nijeriya. Muna bayar da shawara ga Babban Bankin Nijeriya ya bar matsayin harkokin kasuwanci ta nema wa naira daraja, a kuma dawo da ba masu masana’antu muhimmanci a wajen bayar da kudaden kasashen waje. Ya kuma kamata a rage ruwan da ake dorawa basukan da ake ba masu kanana da manyan masana’antu, hakan zai kara jawo masu zuba jari na ciki daga kasashen waje.

Samar da ingantaccen wutar lantarki, ta hanyar sake yi wa sashin garambawul zai matukar taimakawa zai kuma karfafa bunkasar masana’antunmu a cikin wannan shekarar.

Haka kuma ya kamata gwamnatin shugaba Tinubu ta ta tabbatar da an aiwatar da tanade tanaden da ke cikin kasafin kudin 2024 musamman bagarorin da suka nemi ba masu masana’antu tallafin kudade don samar da daidaito ga tattalin arzkin Nijeriya.

Muna kuma karfafa bukatar ‘yan Nijeriya su rika amfani da kayyakin da aka sarrafa a cikin gida, ya kuma kamata gwamnati ta jagoranci wannan yunkurin ta hanyar umartar hukumomi da ma’aikatun gwamnati su rika sayen kayayyakin da aka sarrafa a cikin gida, ta haka za a iya kauce wa durkushewar kamfanoni a wannan shekarar ta 2024.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

AFCON 2023: ‘Yan Wasan Da Tauraruwarsu Ke Haskawa

Next Post

Rikici Ya Ɓarke Bayan Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Sule A Gwamnan Nasarawa

Related

NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya
Tattalin Arziki

NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya

4 days ago
Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci Bunkasa Fannin Mai Da Ake Hakowa A Teku
Tattalin Arziki

Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci Bunkasa Fannin Mai Da Ake Hakowa A Teku

4 days ago
Dalilin Da Ya Sa Gwamnatin Jihar Kuros Ribas Ta Yi Hadaka Da Hukumar NPA
Tattalin Arziki

Dalilin Da Ya Sa Gwamnatin Jihar Kuros Ribas Ta Yi Hadaka Da Hukumar NPA

4 days ago
Ma’aikatan Sufurin Jiregen Sama Sun Bukaci Tinubu Ya Janye Shirin Sayar Da Filayen Jiragen Sama
Tattalin Arziki

Ma’aikatan Sufurin Jiregen Sama Sun Bukaci Tinubu Ya Janye Shirin Sayar Da Filayen Jiragen Sama

2 weeks ago
NPA Ta Fito Da Sabuwar Doka Kan Kayan Da Ake Ajiyewa A Tashoshinta
Tattalin Arziki

NPA Ta Fito Da Sabuwar Doka Kan Kayan Da Ake Ajiyewa A Tashoshinta

2 weeks ago
Shirin Iskar Gas Na CNG Abin A Yaba Wa Shugaba Tinubu Ne -Shugaban IPMAN Na Ƙasa
Tattalin Arziki

Shirin Iskar Gas Na CNG Abin A Yaba Wa Shugaba Tinubu Ne -Shugaban IPMAN Na Ƙasa

2 weeks ago
Next Post
Rikici Ya Ɓarke Bayan Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Sule A Gwamnan Nasarawa

Rikici Ya Ɓarke Bayan Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Sule A Gwamnan Nasarawa

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

August 25, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

August 25, 2025
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

August 25, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

August 25, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

August 25, 2025
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

August 25, 2025
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.