ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsalolin Da Za Su Dabaibaye Harkokin Masana’antu A 2024

by Bello Hamza
2 years ago
2024

A yayin da muke shiga sabuwar shekara 2024, harkokin kasuwanci na fuskantar manyan matsaloli da barazanar da za su bayar da gudummamwar durkusherwar su da hana su walwala.

Shugaban kungiyar masu masana’antu ta kasa, (MAN), Segun Ajayi-Kadir, ya yi hasashen cewa, shekarar 2024 za ta zo da manyan kalubale ga masu masana’antu saboda alamu sun nuna babu kyakyawar fata musamman a cikin watanni 6 na farkon shekarar.

  • Jihar Kaduna Za Ta Ƙarfafa Ƙawancen Tattalin Arziki Da Ƙasar Jamus
  • ‘Yansanda Sun Cafke Wasu Mutane Biyu Da Ake Zargi Da Satar Keke-napep A Kano

Nazari ya nuna cewa, matsalolin za su addabi kanana da manyan masana’natu wadanda za su taso daga harkokin tattalin arziki na ciki da wajen Nijeriya.

ADVERTISEMENT

Musamman ma kungiyar MAN ta bayyana cewa, za a samu nakasu a bunkasar masana’antu daga kashi 2.4 a shekarar 2021 zuwa kashi 0.48 a zango na uku na shekarar 2023.

Ana iya ganin irin wannan ci bayan a manyan kamfanonin kasashe irin su Chana da Amurka, Nijeriya kuma ba za ta iya kare kanta daga wadannan abubuwan ba.

LABARAI MASU NASABA

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho

Yana da matukar muhimmanci a fahimci cewa, matsalolin cikin gida kama daga karyewar darajar Naira da tashin kudin ruwa suna kawo cikas ga bunkasar kamfanonin kasuwanci da kashi 50 a cikin dai.

Za kuma a iya tuna manyan kamfanoni 6 da suka fice daga Nijeriya a cikin wata shida da suka wuce, wadanda suka hada da kamfanin samar da abinci na ‘Procter & Gamble’, Unileber, GladoSmithKline Consumer Nigeria Plc, Sanofi, French pharmaceutical multinational, Bolt Food da kuma kamfanin hada allura na ‘Jubilee Syringe Manufacturing’.

A ra’ayinmu, tsare-tsaren Babban Bankin Nijeriya CBN a ‘yan shekarun nan bai taimaka ba wajen zaburar da bunkasar kamfanoni da tattalin arzikin Nijeriya ba.

Masu harkokin fitar da kayyakin da ake sarrafawa a Nijeriya suna fuskanta rashin tabbas, basu da damar samun kudaden kasashen waje don gudanar da harkokin kasuwancinsu wanda haka ya taimaka wajen durkushewarsu.

Wani abin takaicin kuma shi ne tsaretsaren da aka samar don dakile hauhawar farashi ya taimaka ne kawai weajen takura kanana da mastaikaitun kamfanoni a fadin tarayyar kasar nan.

A irin wannan yanayin harkokin kasuwanci ba za su samu kwarin gwiwar ci gaba ba, kamar yadda kungiyar masu masana’antu ta zayyana a wani taron shugabannin kamfanoni da aka yi kwanakin baya ta yi.

Kungiyar ta yi hasashen wadannan kalubalen za su ta’azzara har zuwa zango na biyu na sabuwar shekara 2024, ana kuma iya samun farfadowa dan kadan daga baya. A hasashen nasu bangaren masana’antu zai samu bunkasar kasa da kashi 3.2 a wannan shdekarar, yayin da gudumawar bangaren ga tattalin arzikin kasa zai gaza kashi 10.

In har ana son kauce wa fadawa wadannan mastalolin dole a canza tsare-tsaren tattalin arzikin kasa ta yadda zai taimakawa bunkasar harkokin kasuwanci a Nijeriya. Muna bayar da shawara ga Babban Bankin Nijeriya ya bar matsayin harkokin kasuwanci ta nema wa naira daraja, a kuma dawo da ba masu masana’antu muhimmanci a wajen bayar da kudaden kasashen waje. Ya kuma kamata a rage ruwan da ake dorawa basukan da ake ba masu kanana da manyan masana’antu, hakan zai kara jawo masu zuba jari na ciki daga kasashen waje.

Samar da ingantaccen wutar lantarki, ta hanyar sake yi wa sashin garambawul zai matukar taimakawa zai kuma karfafa bunkasar masana’antunmu a cikin wannan shekarar.

Haka kuma ya kamata gwamnatin shugaba Tinubu ta ta tabbatar da an aiwatar da tanade tanaden da ke cikin kasafin kudin 2024 musamman bagarorin da suka nemi ba masu masana’antu tallafin kudade don samar da daidaito ga tattalin arzkin Nijeriya.

Muna kuma karfafa bukatar ‘yan Nijeriya su rika amfani da kayyakin da aka sarrafa a cikin gida, ya kuma kamata gwamnati ta jagoranci wannan yunkurin ta hanyar umartar hukumomi da ma’aikatun gwamnati su rika sayen kayayyakin da aka sarrafa a cikin gida, ta haka za a iya kauce wa durkushewar kamfanoni a wannan shekarar ta 2024.

2024
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Amfani Da Matar Soja Wajen Isar Da Sakon Bukata

MASU ALAKA

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
Tattalin Arziki

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

June 20, 2026
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho
Tattalin Arziki

NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho

June 20, 2026
Yawan Man Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Da Ganga 177,000 A Janairu
Tattalin Arziki

Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur

June 13, 2026
Next Post
Rikici Ya Ɓarke Bayan Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Sule A Gwamnan Nasarawa

Rikici Ya Ɓarke Bayan Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Sule A Gwamnan Nasarawa

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.