ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsalolin Da Za Su Dabaibaye Harkokin Masana’antu A 2024

by Bello Hamza
2 years ago
2024

A yayin da muke shiga sabuwar shekara 2024, harkokin kasuwanci na fuskantar manyan matsaloli da barazanar da za su bayar da gudummamwar durkusherwar su da hana su walwala.

Shugaban kungiyar masu masana’antu ta kasa, (MAN), Segun Ajayi-Kadir, ya yi hasashen cewa, shekarar 2024 za ta zo da manyan kalubale ga masu masana’antu saboda alamu sun nuna babu kyakyawar fata musamman a cikin watanni 6 na farkon shekarar.

  • Jihar Kaduna Za Ta Ƙarfafa Ƙawancen Tattalin Arziki Da Ƙasar Jamus
  • ‘Yansanda Sun Cafke Wasu Mutane Biyu Da Ake Zargi Da Satar Keke-napep A Kano

Nazari ya nuna cewa, matsalolin za su addabi kanana da manyan masana’natu wadanda za su taso daga harkokin tattalin arziki na ciki da wajen Nijeriya.

ADVERTISEMENT

Musamman ma kungiyar MAN ta bayyana cewa, za a samu nakasu a bunkasar masana’antu daga kashi 2.4 a shekarar 2021 zuwa kashi 0.48 a zango na uku na shekarar 2023.

Ana iya ganin irin wannan ci bayan a manyan kamfanonin kasashe irin su Chana da Amurka, Nijeriya kuma ba za ta iya kare kanta daga wadannan abubuwan ba.

LABARAI MASU NASABA

Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar

Rage Farashin Mai Na Ɗangote: Dillalan Man Fetur Sun Yi Burus Da Sauya Nasu Farashin

Yana da matukar muhimmanci a fahimci cewa, matsalolin cikin gida kama daga karyewar darajar Naira da tashin kudin ruwa suna kawo cikas ga bunkasar kamfanonin kasuwanci da kashi 50 a cikin dai.

Za kuma a iya tuna manyan kamfanoni 6 da suka fice daga Nijeriya a cikin wata shida da suka wuce, wadanda suka hada da kamfanin samar da abinci na ‘Procter & Gamble’, Unileber, GladoSmithKline Consumer Nigeria Plc, Sanofi, French pharmaceutical multinational, Bolt Food da kuma kamfanin hada allura na ‘Jubilee Syringe Manufacturing’.

A ra’ayinmu, tsare-tsaren Babban Bankin Nijeriya CBN a ‘yan shekarun nan bai taimaka ba wajen zaburar da bunkasar kamfanoni da tattalin arzikin Nijeriya ba.

Masu harkokin fitar da kayyakin da ake sarrafawa a Nijeriya suna fuskanta rashin tabbas, basu da damar samun kudaden kasashen waje don gudanar da harkokin kasuwancinsu wanda haka ya taimaka wajen durkushewarsu.

Wani abin takaicin kuma shi ne tsaretsaren da aka samar don dakile hauhawar farashi ya taimaka ne kawai weajen takura kanana da mastaikaitun kamfanoni a fadin tarayyar kasar nan.

A irin wannan yanayin harkokin kasuwanci ba za su samu kwarin gwiwar ci gaba ba, kamar yadda kungiyar masu masana’antu ta zayyana a wani taron shugabannin kamfanoni da aka yi kwanakin baya ta yi.

Kungiyar ta yi hasashen wadannan kalubalen za su ta’azzara har zuwa zango na biyu na sabuwar shekara 2024, ana kuma iya samun farfadowa dan kadan daga baya. A hasashen nasu bangaren masana’antu zai samu bunkasar kasa da kashi 3.2 a wannan shdekarar, yayin da gudumawar bangaren ga tattalin arzikin kasa zai gaza kashi 10.

In har ana son kauce wa fadawa wadannan mastalolin dole a canza tsare-tsaren tattalin arzikin kasa ta yadda zai taimakawa bunkasar harkokin kasuwanci a Nijeriya. Muna bayar da shawara ga Babban Bankin Nijeriya ya bar matsayin harkokin kasuwanci ta nema wa naira daraja, a kuma dawo da ba masu masana’antu muhimmanci a wajen bayar da kudaden kasashen waje. Ya kuma kamata a rage ruwan da ake dorawa basukan da ake ba masu kanana da manyan masana’antu, hakan zai kara jawo masu zuba jari na ciki daga kasashen waje.

Samar da ingantaccen wutar lantarki, ta hanyar sake yi wa sashin garambawul zai matukar taimakawa zai kuma karfafa bunkasar masana’antunmu a cikin wannan shekarar.

Haka kuma ya kamata gwamnatin shugaba Tinubu ta ta tabbatar da an aiwatar da tanade tanaden da ke cikin kasafin kudin 2024 musamman bagarorin da suka nemi ba masu masana’antu tallafin kudade don samar da daidaito ga tattalin arzkin Nijeriya.

Muna kuma karfafa bukatar ‘yan Nijeriya su rika amfani da kayyakin da aka sarrafa a cikin gida, ya kuma kamata gwamnati ta jagoranci wannan yunkurin ta hanyar umartar hukumomi da ma’aikatun gwamnati su rika sayen kayayyakin da aka sarrafa a cikin gida, ta haka za a iya kauce wa durkushewar kamfanoni a wannan shekarar ta 2024.

2024
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Shugaban Miyetti Allah, Bodejo Ya Karyata Zargin Halatta Kudin Haram A Zaman Kotu
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kafa Cibiyar NIPHID: NCDC Ta Yi Kuskuren Fahimtar Ƙudirin Dokar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Muhimman Ayyukan Ci Gaba A Jihar Jigawa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ƙungiyar Kansilolin APC Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Idan Ba A Daina Zargin Sanata Yari Ba

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Tattalin Arziki

Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar

July 11, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN
Tattalin Arziki

Rage Farashin Mai Na Ɗangote: Dillalan Man Fetur Sun Yi Burus Da Sauya Nasu Farashin

June 27, 2026
Gwamnatin Tarayya, Bankin Duniya Da Cibiyar IITA Za Su Bunkasa Noma Ta Fasahar Zamani
Tattalin Arziki

Bankin Duniya Ya Ɗora Tashoshin Apapa Da Tincan Kan Sikelin Maki Na 20 A Duniya

June 26, 2026
Next Post
Rikici Ya Ɓarke Bayan Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Sule A Gwamnan Nasarawa

Rikici Ya Ɓarke Bayan Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Sule A Gwamnan Nasarawa

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.