• English
  • Business News
Friday, June 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Ceto Dimokuradiyyar Nijeriya Bisa Kin Katsalandan A Shari’ar Gwamnoni – Kabiru Marafa

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Manyan Labarai
0
Irin Ministocin Da ‘Yan Nijeriya Ke Tsammani Daga Gwamnatin Tinubu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Majalisar Tarayya Na Ƙoƙarin Zama Ƴar Amshin Shata – Saraki

Cikin Shekaru 2, Tinubu Ya Karɓo Bashi Fiye da Shugabannin Nijeriya 3 – Obi

Ko-odinetan yakin neman zaben Tinubu a Zamfara a zaben da ya gabata, Sanata Kabiru Marafa ya bayyana cewa rashin katsalandan Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu a shari’o’in zaben gwamnoni a kotun koli ya yi matukar ceto dimokuradiyyar kasar nan da kuma farfado da bangaren shari’a.

A ranar Juma’a da ta gabata ce, kotun koli ta raba gardama a zaben gwamnoni guda 8, inda ta tabbatar da nasarar gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, gwamnan Jihar Filato, Caleb Mutfwang, gwamnan Jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu, gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed, gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, gwamnan Jihar Ebonyi, Francis Nwifuru, gwamnan Jihar Abiya, Aled Otti da kuma gwamnan Jihar Kuros Riba, Bassey Otu.

  • ‘Yan Bindiga Sanye Da Hijabi Sun Farmaki Ofishin ‘Yansanda A Katsina
  • Nijeriya Na Fatan Samun Karin Masu Zuba Jari A Taron Kasuwanci Na Duniya

 Marafa ya bayyana haka ne a cikin wata sanarwa da ya fitar a Abuja, inda ya bayyana cewa Shugaba Tinubu da alkalan kotun koli sun cancanji yabo a wurin ‘yan Nijeriya, saboda sun tabbatar da abun da ‘yan Nijeriya suka zaba.

Ya yaba wa shugaban kasa na kin yin katsalandan, musamman ma a shari’ar gwamnan Jihar Kano wanda ya samu matsin lamba daga magoya bayan jam’iyyarsa.

Marafa ya ce, “Abin farin ciki ne yadda Shugaba Bola Ahmed Tinubu bai tsoma baki a hukuncin kotun koli ba, haka ya ceci dimokuradiyyar kasar tare da hana sake faruwan abin da ya auko a shekarar 1983.”

Da yake jinjina wa alkalan kotun kolin, Sanata Marafa ya ce sun cika abin da talakawan Nijeriya ke bukata, inda ya ce sun sanya kasar cikin alfahari.

Ya tuno da irin wannan lamari da ya faru zaben 2019, inda a lokacin yake fafatukan neman tikitin takarar gwamnan Zamfara a karkashin jam’iyyar.

Ya ce, “Na yi adawa na nuna rashin amincewa da yadda zaben fid da gwani wajen tsayar da ‘yan takara da Abdulaziz Yari ya samu nasara, inda bangaren shari’a ya tsaya tsayin daka wajen zartar da hukunci da ya bai wa jam’iyyar adawa ta PDP a jihar baki daya.

“Dole ne a bar bangaren shari’a su kasance masu gaskiya da adalci idan ‘yan siyasa suna son dimokuradiyya ta dore a kasar nan.”

Marafa ya bukaci gwamnonin takwas da su kasance masu kankan da kai da adalci wajen tafiyar da mulki a jihohinsu.

Ya taya gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal murna tare da jawo hankalinsa wajen yin aiki domin cika amincewar da al’ummar jihar suka yi masa.

Marafa ya ce, “A saboda haka, ina kira ga gwamnan jiharmu ta Zamfara da ya hada kai da mai girma Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu da mataimakinsa, Sanata Kashim Shettima da hukumomin tsaro domin dawo da zaman lafiya da tsaro da ake bukata a Jihar Zamfara. Zaman lafiya shi ne abin da jama’armu ke fata ba komai ba.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Da Kamaru Sun Yi Alkawarin Kara Samun Sabbin Nasarori A Hadin Gwiwar Dake Tsakaninsu

Next Post

Yadda Za Ku Inganta Rayuwarku A 2024 A Kimiyyance

Related

Majalisar Tarayya Na Ƙoƙarin Zama Ƴar Amshin Shata – Saraki
Manyan Labarai

Majalisar Tarayya Na Ƙoƙarin Zama Ƴar Amshin Shata – Saraki

8 hours ago
Cikin Shekaru 2, Tinubu Ya Karɓo Bashi Fiye da Shugabannin Nijeriya 3 – Obi
Manyan Labarai

Cikin Shekaru 2, Tinubu Ya Karɓo Bashi Fiye da Shugabannin Nijeriya 3 – Obi

10 hours ago
nijeriya
Manyan Labarai

Yadda Badakalar Tallafin Man Fetur Ta Zame Wa Nijeriya Alakakai

12 hours ago
Ba Zan Bar Nijeriya Ta Zama Kasa Mai Jam’iyya Daya Ba – Tinubu
Manyan Labarai

Ba Zan Bar Nijeriya Ta Zama Kasa Mai Jam’iyya Daya Ba – Tinubu

1 day ago
Sojoji Sun Kashe Auta, Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda Da Wasu 13 a Jihar Zamfara
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Auta, Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda Da Wasu 13 a Jihar Zamfara

1 day ago
Zamfara: APC Za Ta Maka PDP A Kotu Kan Zargin Matawalle Da Hannu A Satar Mutane
Manyan Labarai

Zamfara: APC Za Ta Maka PDP A Kotu Kan Zargin Matawalle Da Hannu A Satar Mutane

1 day ago
Next Post
Yadda Za Ku Inganta Rayuwarku A 2024 A Kimiyyance

Yadda Za Ku Inganta Rayuwarku A 2024 A Kimiyyance

LABARAI MASU NASABA

Bin Hanya Daya Da Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Muhimmin Mataki Ne Na Ba Da Tabbaci Ga Huldar Ciniki Da Tattalin Arzikin Sin Da Amurka

Bin Hanya Daya Da Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Muhimmin Mataki Ne Na Ba Da Tabbaci Ga Huldar Ciniki Da Tattalin Arzikin Sin Da Amurka

June 13, 2025
Sin Ta Bayyana Adawa Da Keta Hurumin ‘Yanci Tsaro Da Ikon Mulkin Yankunan Iran

Sin Ta Bayyana Adawa Da Keta Hurumin ‘Yanci Tsaro Da Ikon Mulkin Yankunan Iran

June 13, 2025
Gwamnati Ta Yi Karin Haske Kan Biyan Tallafin Rage Radadi Da Mafi Karancin Albashi

Gwamnati Ta Yi Karin Haske Kan Biyan Tallafin Rage Radadi Da Mafi Karancin Albashi

June 13, 2025
An Kaddamar Da Bikin Gabatar Da Jerin Shirye-shiryen Telebijin Da Fina-finai Na CMG A Birnin Astana

An Kaddamar Da Bikin Gabatar Da Jerin Shirye-shiryen Telebijin Da Fina-finai Na CMG A Birnin Astana

June 13, 2025
Kamfanonin Waje Sun Ce Dole Ne Su Shiga A Dama Da Su A Cikin Kasuwar Kasar Sin

Kamfanonin Waje Sun Ce Dole Ne Su Shiga A Dama Da Su A Cikin Kasuwar Kasar Sin

June 13, 2025
Dawanau

Gwamnatin Tarayya Ta Dukufa Wajen Karya Farashin Kayan Abinci – Minista

June 13, 2025
Ƴansanda Sun Kama Shahararren Ɗan Damfarar Yanar Gizo A Bauchi

Ƴansanda Sun Kama Shahararren Ɗan Damfarar Yanar Gizo A Bauchi

June 13, 2025
Matsin Rayuwa: ‘Yan Nijeriya Sun Rage Zuwa Kasashen Waje

Matsin Rayuwa: ‘Yan Nijeriya Sun Rage Zuwa Kasashen Waje

June 13, 2025
Gwamna Bala

Gwamnatin Bauchi Ta Fara Shirin Kirkirar Sabbin Masarautu Da Sarakuna Da Gundumomi

June 13, 2025
Ƴansanda Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 2, Sun Ceto Mutane 11 A Delta Da Katsina

Ƴansanda Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 2, Sun Ceto Mutane 11 A Delta Da Katsina

June 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.