• English
  • Business News
Monday, August 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Ceto Dimokuradiyyar Nijeriya Bisa Kin Katsalandan A Shari’ar Gwamnoni – Kabiru Marafa

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Irin Ministocin Da ‘Yan Nijeriya Ke Tsammani Daga Gwamnatin Tinubu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

Ƙungiyoyin Farar Hula Sun Nemi A Dakatar Da Jami’an Gwamnatin Kano

Ko-odinetan yakin neman zaben Tinubu a Zamfara a zaben da ya gabata, Sanata Kabiru Marafa ya bayyana cewa rashin katsalandan Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu a shari’o’in zaben gwamnoni a kotun koli ya yi matukar ceto dimokuradiyyar kasar nan da kuma farfado da bangaren shari’a.

A ranar Juma’a da ta gabata ce, kotun koli ta raba gardama a zaben gwamnoni guda 8, inda ta tabbatar da nasarar gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, gwamnan Jihar Filato, Caleb Mutfwang, gwamnan Jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu, gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed, gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, gwamnan Jihar Ebonyi, Francis Nwifuru, gwamnan Jihar Abiya, Aled Otti da kuma gwamnan Jihar Kuros Riba, Bassey Otu.

  • ‘Yan Bindiga Sanye Da Hijabi Sun Farmaki Ofishin ‘Yansanda A Katsina
  • Nijeriya Na Fatan Samun Karin Masu Zuba Jari A Taron Kasuwanci Na Duniya

 Marafa ya bayyana haka ne a cikin wata sanarwa da ya fitar a Abuja, inda ya bayyana cewa Shugaba Tinubu da alkalan kotun koli sun cancanji yabo a wurin ‘yan Nijeriya, saboda sun tabbatar da abun da ‘yan Nijeriya suka zaba.

Ya yaba wa shugaban kasa na kin yin katsalandan, musamman ma a shari’ar gwamnan Jihar Kano wanda ya samu matsin lamba daga magoya bayan jam’iyyarsa.

Marafa ya ce, “Abin farin ciki ne yadda Shugaba Bola Ahmed Tinubu bai tsoma baki a hukuncin kotun koli ba, haka ya ceci dimokuradiyyar kasar tare da hana sake faruwan abin da ya auko a shekarar 1983.”

Da yake jinjina wa alkalan kotun kolin, Sanata Marafa ya ce sun cika abin da talakawan Nijeriya ke bukata, inda ya ce sun sanya kasar cikin alfahari.

Ya tuno da irin wannan lamari da ya faru zaben 2019, inda a lokacin yake fafatukan neman tikitin takarar gwamnan Zamfara a karkashin jam’iyyar.

Ya ce, “Na yi adawa na nuna rashin amincewa da yadda zaben fid da gwani wajen tsayar da ‘yan takara da Abdulaziz Yari ya samu nasara, inda bangaren shari’a ya tsaya tsayin daka wajen zartar da hukunci da ya bai wa jam’iyyar adawa ta PDP a jihar baki daya.

“Dole ne a bar bangaren shari’a su kasance masu gaskiya da adalci idan ‘yan siyasa suna son dimokuradiyya ta dore a kasar nan.”

Marafa ya bukaci gwamnonin takwas da su kasance masu kankan da kai da adalci wajen tafiyar da mulki a jihohinsu.

Ya taya gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal murna tare da jawo hankalinsa wajen yin aiki domin cika amincewar da al’ummar jihar suka yi masa.

Marafa ya ce, “A saboda haka, ina kira ga gwamnan jiharmu ta Zamfara da ya hada kai da mai girma Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu da mataimakinsa, Sanata Kashim Shettima da hukumomin tsaro domin dawo da zaman lafiya da tsaro da ake bukata a Jihar Zamfara. Zaman lafiya shi ne abin da jama’armu ke fata ba komai ba.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Da Kamaru Sun Yi Alkawarin Kara Samun Sabbin Nasarori A Hadin Gwiwar Dake Tsakaninsu

Next Post

Yadda Za Ku Inganta Rayuwarku A 2024 A Kimiyyance

Related

Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike
Manyan Labarai

Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

2 hours ago
Ƙungiyoyin Farar Hula Sun Nemi A Dakatar Da Jami’an Gwamnatin Kano
Manyan Labarai

Ƙungiyoyin Farar Hula Sun Nemi A Dakatar Da Jami’an Gwamnatin Kano

8 hours ago
Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

18 hours ago
Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP
Manyan Labarai

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

1 day ago
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru
Manyan Labarai

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

2 days ago
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu
Ilimi

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

2 days ago
Next Post
Yadda Za Ku Inganta Rayuwarku A 2024 A Kimiyyance

Yadda Za Ku Inganta Rayuwarku A 2024 A Kimiyyance

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Shiga Jerin Kasashe 3 Dake Sahun Gaba Wajen Gudanar Da Cinikayya Da Kasashe Da Yankunan Duniya 157

Sin Ta Shiga Jerin Kasashe 3 Dake Sahun Gaba Wajen Gudanar Da Cinikayya Da Kasashe Da Yankunan Duniya 157

August 25, 2025
Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

August 25, 2025
Harin Asibitin Gaza Ya Halaka Mutane da Dama, Ciki Har da Ƴan Jarida

Harin Asibitin Gaza Ya Halaka Mutane da Dama, Ciki Har da Ƴan Jarida

August 25, 2025
Sojoji Sun Kama Mutane 69 Masu Fasa Bututun Mai A Yankin Neja-Delta

Sojoji Sun Kama Mutane 69 Masu Fasa Bututun Mai A Yankin Neja-Delta

August 25, 2025
Ƙungiyar KSCI Ta Nemi Sabon Tsari Don Magance Ƴan Bindiga A Katsina

Ƙungiyar KSCI Ta Nemi Sabon Tsari Don Magance Ƴan Bindiga A Katsina

August 25, 2025
Ƙungiyoyin Farar Hula Sun Nemi A Dakatar Da Jami’an Gwamnatin Kano

Ƙungiyoyin Farar Hula Sun Nemi A Dakatar Da Jami’an Gwamnatin Kano

August 25, 2025
Tinubu Ya Isa Brazil, Zai Nemi Masu Zuba Jarin Biliyoyi A Noma, Makamashi Da Fasaha

Tinubu Ya Isa Brazil, Zai Nemi Masu Zuba Jarin Biliyoyi A Noma, Makamashi Da Fasaha

August 25, 2025

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

August 24, 2025
Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

August 24, 2025
Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

August 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.