ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Ceto Dimokuradiyyar Nijeriya Bisa Kin Katsalandan A Shari’ar Gwamnoni – Kabiru Marafa

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Tinubu

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

Ko-odinetan yakin neman zaben Tinubu a Zamfara a zaben da ya gabata, Sanata Kabiru Marafa ya bayyana cewa rashin katsalandan Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu a shari’o’in zaben gwamnoni a kotun koli ya yi matukar ceto dimokuradiyyar kasar nan da kuma farfado da bangaren shari’a.

A ranar Juma’a da ta gabata ce, kotun koli ta raba gardama a zaben gwamnoni guda 8, inda ta tabbatar da nasarar gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, gwamnan Jihar Filato, Caleb Mutfwang, gwamnan Jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu, gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed, gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, gwamnan Jihar Ebonyi, Francis Nwifuru, gwamnan Jihar Abiya, Aled Otti da kuma gwamnan Jihar Kuros Riba, Bassey Otu.

  • ‘Yan Bindiga Sanye Da Hijabi Sun Farmaki Ofishin ‘Yansanda A Katsina
  • Nijeriya Na Fatan Samun Karin Masu Zuba Jari A Taron Kasuwanci Na Duniya

 Marafa ya bayyana haka ne a cikin wata sanarwa da ya fitar a Abuja, inda ya bayyana cewa Shugaba Tinubu da alkalan kotun koli sun cancanji yabo a wurin ‘yan Nijeriya, saboda sun tabbatar da abun da ‘yan Nijeriya suka zaba.

Ya yaba wa shugaban kasa na kin yin katsalandan, musamman ma a shari’ar gwamnan Jihar Kano wanda ya samu matsin lamba daga magoya bayan jam’iyyarsa.

Marafa ya ce, “Abin farin ciki ne yadda Shugaba Bola Ahmed Tinubu bai tsoma baki a hukuncin kotun koli ba, haka ya ceci dimokuradiyyar kasar tare da hana sake faruwan abin da ya auko a shekarar 1983.”

Da yake jinjina wa alkalan kotun kolin, Sanata Marafa ya ce sun cika abin da talakawan Nijeriya ke bukata, inda ya ce sun sanya kasar cikin alfahari.

Ya tuno da irin wannan lamari da ya faru zaben 2019, inda a lokacin yake fafatukan neman tikitin takarar gwamnan Zamfara a karkashin jam’iyyar.

Ya ce, “Na yi adawa na nuna rashin amincewa da yadda zaben fid da gwani wajen tsayar da ‘yan takara da Abdulaziz Yari ya samu nasara, inda bangaren shari’a ya tsaya tsayin daka wajen zartar da hukunci da ya bai wa jam’iyyar adawa ta PDP a jihar baki daya.

“Dole ne a bar bangaren shari’a su kasance masu gaskiya da adalci idan ‘yan siyasa suna son dimokuradiyya ta dore a kasar nan.”

Marafa ya bukaci gwamnonin takwas da su kasance masu kankan da kai da adalci wajen tafiyar da mulki a jihohinsu.

Ya taya gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal murna tare da jawo hankalinsa wajen yin aiki domin cika amincewar da al’ummar jihar suka yi masa.

Marafa ya ce, “A saboda haka, ina kira ga gwamnan jiharmu ta Zamfara da ya hada kai da mai girma Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu da mataimakinsa, Sanata Kashim Shettima da hukumomin tsaro domin dawo da zaman lafiya da tsaro da ake bukata a Jihar Zamfara. Zaman lafiya shi ne abin da jama’armu ke fata ba komai ba.”

Tinubu
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Next Post
Yadda Za Ku Inganta Rayuwarku A 2024 A Kimiyyance

Yadda Za Ku Inganta Rayuwarku A 2024 A Kimiyyance

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.