• English
  • Business News
Wednesday, October 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masu Sana’ar Bola-jari Sun Buƙaci Gwamnatin Nijeriya Ta Tallafa Musu Da Rancen Kuɗaɗe

by Muhammad
2 years ago
Bola-jari

Kungiyar dillalan masu sana’ar Bola-jari ta Nijeriya ta kasa, ta bukaci gwamnatin tarayya da ta ba su lamuni mai sauki domin fadada harkokin kasuwancinsu.

Dillalan na jari-bola sun kuma bukaci gwamnati da ta yi duba kan hukumomin tsaro da su daina muzgunawa mambobinsu.

  • Rayuwar ‘Yan Jari-bola Bayan Fatattakar Su A Abuja
  • Abin Haushi, Mata Sun Mayar Da Maza Tamkar Bola

Shugaban shugabannin kungiyar, Alhaji Aminu Hassan, ne ya yi wannan roko a taron masu ruwa da tsaki na kungiyar a ranar Lahadi a Abuja.

Kungiyar ta masu sana’ar Bola-jari, kungiya ce da take da rijista a hukumance a karkashin dokar kungiyar kwadago, Cap. T14, na dokokin Tarayyar Nijeriya 2004.

Ita ce jigo ta duk mutanen da ke sana’ar Bola-jari, kuma take rarrabawa kamfanoni masu sarrafa lallatattun kaya su juya su zuwa sababbi kaya.

LABARAI MASU NASABA

DSS Ta Kama Wani Matashi Da Ya Yi Kira A Yi Juyin Mulki A Kafofin Sada Zumunta

An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe

Masana sun ce sana’ar tana samun sama da Naira tiriliyan daya a duk shekara.

A cewar Hassan, kungiyar na matukar bukatar kudade da kariya domin bunkasa gudummawar da take bayarwa ga tattalin arzikin kasa.

“Muna da mambobi har miliyan biyar, amma suna aiki a cikin yanayi mai wahala,” in ji shi.

Hassan ya yi zargin cewa jami’an tsaro na cin zarafinsu “musamman wajen isar da kayayyakinmu ga kamfanonin da ke hakar man fetur”.

“Saboda haka, muna kira ga gwamnatin tarayya da ta shiga tsakani ta kuma taimaka mana wajen bin diddigin wannan mugunyar dabi’ar domin ba mu damar gudanar da harkokinmu ba tare da wata matsala ba.

“A jihar Kano kadai muna da mambobi kusan miliyan guda da suke bazuwa a fadin jihar ba a maganar jihar Legas inda muke da mambobi kusan miliyan biyu a sana’ar Bola-jari.

Shugaban ya kara da cewa “Kasuwancin da ke da dimbin mambobi sun cancanci tallafin kudi da kariya daga gwamnatin tarayya don ba su damar yin aiki yadda ya kamata.”

Hassan ya kuma yi kira ga gwamnatin tarayya da ta sa baki kan farashin kayayyakin da suke sayar da su, kar a bar wa kamfanonin da suke kasuwanci da su.

“Wadannan kamfanoni, galibin kamfanonin kasashen waje, mallakar Sinawa da Indiyawa, suna sha’awar canza farashin kayayyakin da suke saya daga gare mu yadda suke so, wani lokacin ba tare da sanar da mu, masu kawo kayayyaki ba.

“Wannan ci gaban ya shafi kasuwancinmu sosai.

“Misali, za ku iya siyan kaya a kan Naira 500,000, amma idan kun isa kamfanin, za su ce muku ba za su iya siyan sa fiye da N400,000 ba.

“Wannan yakan haifar da babban rashi ko asara daga bangarenmu. Ka yi tunani bayan ka sayi samfur akan N500,000 kawai ka gama sai ka siyar da shi akan N400,000.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamnatin Rikon Kwarya: Shirin DSS Ne Na Damke Atiku Da Peter Obi Kafin Rantsar Da Tinubu
Labarai

DSS Ta Kama Wani Matashi Da Ya Yi Kira A Yi Juyin Mulki A Kafofin Sada Zumunta

October 29, 2025
An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe
Labarai

An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe

October 29, 2025
Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Tayar Da Hankali A Zaɓen Anambra
Labarai

Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Tayar Da Hankali A Zaɓen Anambra

October 29, 2025
Next Post
Wakiliyar Musamman Ta Shugaban Kasar Sin Ta Halarci Bikin Rantsar Da Shugaban Jamhuriyar Demokradiyyar Kongo

Wakiliyar Musamman Ta Shugaban Kasar Sin Ta Halarci Bikin Rantsar Da Shugaban Jamhuriyar Demokradiyyar Kongo

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Rikon Kwarya: Shirin DSS Ne Na Damke Atiku Da Peter Obi Kafin Rantsar Da Tinubu

DSS Ta Kama Wani Matashi Da Ya Yi Kira A Yi Juyin Mulki A Kafofin Sada Zumunta

October 29, 2025
An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe

An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe

October 29, 2025
Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Tayar Da Hankali A Zaɓen Anambra

Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Tayar Da Hankali A Zaɓen Anambra

October 29, 2025
ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa

Ba Matakan Tinubu Ne Suka Karyar Da Farashin Kayan Abinci Ba – ADC

October 29, 2025
‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa

‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa

October 29, 2025
Sanusi Ga ‘Yan Nijeriya: Ku Dora Wa Buhari Alhakin Matsatsin Tattalin Arziki Ba Tinubu Ba

Tsoron Boko Haram Ne Ya Sa Jonathan Ya Fasa Cire Tallafin Man Fetur – Sanusi II

October 29, 2025
Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

October 28, 2025
JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

October 28, 2025
An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

October 28, 2025
Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

October 28, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.