ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masu Sana’ar Bola-jari Sun Buƙaci Gwamnatin Nijeriya Ta Tallafa Musu Da Rancen Kuɗaɗe

by Muhammad
2 years ago
Bola-jari

Kungiyar dillalan masu sana’ar Bola-jari ta Nijeriya ta kasa, ta bukaci gwamnatin tarayya da ta ba su lamuni mai sauki domin fadada harkokin kasuwancinsu.

Dillalan na jari-bola sun kuma bukaci gwamnati da ta yi duba kan hukumomin tsaro da su daina muzgunawa mambobinsu.

  • Rayuwar ‘Yan Jari-bola Bayan Fatattakar Su A Abuja
  • Abin Haushi, Mata Sun Mayar Da Maza Tamkar Bola

Shugaban shugabannin kungiyar, Alhaji Aminu Hassan, ne ya yi wannan roko a taron masu ruwa da tsaki na kungiyar a ranar Lahadi a Abuja.

ADVERTISEMENT

Kungiyar ta masu sana’ar Bola-jari, kungiya ce da take da rijista a hukumance a karkashin dokar kungiyar kwadago, Cap. T14, na dokokin Tarayyar Nijeriya 2004.

Ita ce jigo ta duk mutanen da ke sana’ar Bola-jari, kuma take rarrabawa kamfanoni masu sarrafa lallatattun kaya su juya su zuwa sababbi kaya.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Masana sun ce sana’ar tana samun sama da Naira tiriliyan daya a duk shekara.

A cewar Hassan, kungiyar na matukar bukatar kudade da kariya domin bunkasa gudummawar da take bayarwa ga tattalin arzikin kasa.

“Muna da mambobi har miliyan biyar, amma suna aiki a cikin yanayi mai wahala,” in ji shi.

Hassan ya yi zargin cewa jami’an tsaro na cin zarafinsu “musamman wajen isar da kayayyakinmu ga kamfanonin da ke hakar man fetur”.

“Saboda haka, muna kira ga gwamnatin tarayya da ta shiga tsakani ta kuma taimaka mana wajen bin diddigin wannan mugunyar dabi’ar domin ba mu damar gudanar da harkokinmu ba tare da wata matsala ba.

“A jihar Kano kadai muna da mambobi kusan miliyan guda da suke bazuwa a fadin jihar ba a maganar jihar Legas inda muke da mambobi kusan miliyan biyu a sana’ar Bola-jari.

Shugaban ya kara da cewa “Kasuwancin da ke da dimbin mambobi sun cancanci tallafin kudi da kariya daga gwamnatin tarayya don ba su damar yin aiki yadda ya kamata.”

Hassan ya kuma yi kira ga gwamnatin tarayya da ta sa baki kan farashin kayayyakin da suke sayar da su, kar a bar wa kamfanonin da suke kasuwanci da su.

“Wadannan kamfanoni, galibin kamfanonin kasashen waje, mallakar Sinawa da Indiyawa, suna sha’awar canza farashin kayayyakin da suke saya daga gare mu yadda suke so, wani lokacin ba tare da sanar da mu, masu kawo kayayyaki ba.

“Wannan ci gaban ya shafi kasuwancinmu sosai.

“Misali, za ku iya siyan kaya a kan Naira 500,000, amma idan kun isa kamfanin, za su ce muku ba za su iya siyan sa fiye da N400,000 ba.

“Wannan yakan haifar da babban rashi ko asara daga bangarenmu. Ka yi tunani bayan ka sayi samfur akan N500,000 kawai ka gama sai ka siyar da shi akan N400,000.

Bola-jari
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Wakiliyar Musamman Ta Shugaban Kasar Sin Ta Halarci Bikin Rantsar Da Shugaban Jamhuriyar Demokradiyyar Kongo

Wakiliyar Musamman Ta Shugaban Kasar Sin Ta Halarci Bikin Rantsar Da Shugaban Jamhuriyar Demokradiyyar Kongo

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.