Hukumar kwallon kafa ta kasar Ghana ta dauki matakin korar kocin tawagar ‘yan kwallon kasar ta Black Stars, Chris Hughton bayan fitar da kasar daga gasar cin kofin Nahiyar Afirka (AFCON) a Cote d’Ivoire.
Kamfanin dillancin labaran Nijeriya (NAN), ya ruwaito cewa hukumar kwallon kafar Ghana (GFA) ta sanar da hakan a ranar Talata jim kadan bayan da aka tabbatar da fitar da kasar.
- AFCON 2023: Nijeriya Za Ta Kara Da Kamaru A Zagayen Gaba
- Sin Ta Ba Da Rahoton Fadada Shigo Da Kayayyakin Gona Da Na Abinci A Shekarar 2023
An kori Chris Hughton daga aikinsa na babban kocin tawagar kasar tare da sauran masu taimaka masa nan take.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp